Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno
Published: 17th, April 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.কীওয়ার্ড: Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
Hare-Haren Isra’ila Ya Hallaka Aƙalla Mutum 38 A Gaza Cikin Rabin Sa’a
Akalla Falasdinawa 38 ne suka rasa rayukansu a wani jerin hare-haren jiragen yaƙin Isra’ila da aka kai a sassa daban-daban na Gaza cikin rabin sa’a da dare, in ji likitocin Falasɗinawa.
Rahotanni daga hukumar agajin gaggawa da ke ƙarkashin Hamas sun ce jiragen yaƙin Isra’ila sun kai hari a wurare da dama, ciki har da wata makaranta a gabashin birnin Gaza, da kuma wani tsohon gidan mai a sansanin ’yan gudun hijira na Nuseirat da ke tsakiyar Gaza, inda iyalai da dama ke neman mafaka.
Hukumar ta ƙara da cewa tawagar ceto na fuskantar matsaloli wajen kai ɗauki ga waɗanda suka jikkata saboda ƙarancin kayan aiki da kuma tsananin harin.
Wannan hari ya biyo bayan umarnin kwashe jama’a gaba ɗaya da Isra’ila ta bayar a wani shiri na kai “mummunan hari da ba a taɓa gani ba,” a cewarta.
A cewar wasu masu rajin kare haƙƙin dan Adam a birnin Gaza, mutum 10 ne suka mutu a lokacin da wani hari da jirgi a makarantar Musa bin Nusayr inda ɗaruruwan ’yan gudun hijira ke fakewa.
A tsakiyar Gaza, rahotanni sun ce mutum 15 sun mutu a wani hari da aka kai kan tantuna a wani tsohon gidan mai da ke sansanin Nuseirat.