HausaTv:
2025-04-30@18:53:40 GMT

 ‘Yan Hamayyar Tanzaniya Sun Ki Amincewa Da Hana Su Shiga Zabe

Published: 16th, April 2025 GMT

Jam’iyyar Hamayyar siyasa ta “Chadema” a kasar Tanzania ta ki amincewa da matakin gwamnatin kasar na haramta mata shiga manyan zabukan da za a yi a watan Oktoba.

Hukumar zaben kasar ta Tanzania ta zargi jam’iyyar Chameda’ da cewa ta ki amincewa ta rattaba hannu akan dokokin zabe, tana mai yin kira gare ta da ta girmama hukumar zaben kasar.

A ranar Asabar din da ta gabata ne dai babbar jam’iyyar adawa ta kasar Tanzania ta kauracewa halartar taron da aka yi wanda ya kunshi dukkanin jam’iyyun siyasa da su ka rattaba hannu akan dokokin zabe. Rattaba hannu akan dokokin dai yana a matsayin daya daga cikin sharuddan shiga cikin zabe da jam’iyyu za su yi,kamar yadda Ramadhani Kalima, daraktan hukumar zaben kasar ya fada wa manema labaru.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar Chadema  Regemeleza Nshala  ya bayyana matakin na  hukumar zaben da cewa ya saba wa doka. Haka nan kuma ya kara da cewa,abinda doka ta ce, duk jam’iyyar da ba ta rattaba hannu akan dokoki za a ci tararshi, ba hana shi shiga zabe ba.

An kama shugaban jam’iyyar ta Chameda,Tundu Lissu a yayin da ya shiga cikin zanga-zangar da take yin kira da a sauya dokokin zabe kafin lokacin zaben ya zo.

Jami’an ‘yan sanda sun yi awon gaba da shugaban jam’iyyar ta adawa, an kuma zarge shi da cin amanar kasa.

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama sun zargi gwamnatin kasar ta Tanzania da amfani da dabaru mabanbanta  na cutar da jam’iyyar ta jam’iyyar adawa. Gwamnatin kasar ta Tanzania ta yi watsi da zargin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

A ko da yaushe Sin tana himmatuwa wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin kasar Sin, tare da kira da a warware rikici ta hanyar tattaunawa. A sa’i daya kuma, aniyarta ta kiyaye ikon mulkin kasa, da hakki da moriyarta a tekun kudancin Sin ba za ta sauya ba. Ita kasar Philippines kuma za ta dandana kudarta bisa ga yadda ta aiwatar da mummunan mataki kan batun zirin tekun Taiwan, da nufin biyan bukatun Amurka game da dabarunta a yankunan tekun Indiya da na fasifik. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • Sabbin Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci: Nan Ba Da Jimawa Ba, ‘Yan Ta’adda Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu – COAS
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare