HausaTv:
2025-08-15@07:46:51 GMT

 ‘Yan Hamayyar Tanzaniya Sun Ki Amincewa Da Hana Su Shiga Zabe

Published: 16th, April 2025 GMT

Jam’iyyar Hamayyar siyasa ta “Chadema” a kasar Tanzania ta ki amincewa da matakin gwamnatin kasar na haramta mata shiga manyan zabukan da za a yi a watan Oktoba.

Hukumar zaben kasar ta Tanzania ta zargi jam’iyyar Chameda’ da cewa ta ki amincewa ta rattaba hannu akan dokokin zabe, tana mai yin kira gare ta da ta girmama hukumar zaben kasar.

A ranar Asabar din da ta gabata ne dai babbar jam’iyyar adawa ta kasar Tanzania ta kauracewa halartar taron da aka yi wanda ya kunshi dukkanin jam’iyyun siyasa da su ka rattaba hannu akan dokokin zabe. Rattaba hannu akan dokokin dai yana a matsayin daya daga cikin sharuddan shiga cikin zabe da jam’iyyu za su yi,kamar yadda Ramadhani Kalima, daraktan hukumar zaben kasar ya fada wa manema labaru.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar Chadema  Regemeleza Nshala  ya bayyana matakin na  hukumar zaben da cewa ya saba wa doka. Haka nan kuma ya kara da cewa,abinda doka ta ce, duk jam’iyyar da ba ta rattaba hannu akan dokoki za a ci tararshi, ba hana shi shiga zabe ba.

An kama shugaban jam’iyyar ta Chameda,Tundu Lissu a yayin da ya shiga cikin zanga-zangar da take yin kira da a sauya dokokin zabe kafin lokacin zaben ya zo.

Jami’an ‘yan sanda sun yi awon gaba da shugaban jam’iyyar ta adawa, an kuma zarge shi da cin amanar kasa.

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama sun zargi gwamnatin kasar ta Tanzania da amfani da dabaru mabanbanta  na cutar da jam’iyyar ta jam’iyyar adawa. Gwamnatin kasar ta Tanzania ta yi watsi da zargin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Ejodame ya rahoto CAS, yana cewa “Tare da ingantattun jirage da ke da ingantattun tsare-tsaren kai hare-hare na dare, jirgin NAF ya kai hare-hare guda 798”.

 

 

A nasa jawabin, Gwamna Zulum ya yabawa NAF bisa ci gaba da bayar da tallafi ta sama wajen gurgunta karfin ‘yan ta’adda da kuma kare al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
  • ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
  • An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
  • Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello
  • Ministocin Harkokin Wajen Kasashe 27 Ne Sun Bukaci HKI Ta Kawo Karshen Hana Abinci Shiga Gaza
  • Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
  • Rundunar ‘Yan Sandan Kano Ta Yi Gargadi Game Da Sabawa Dokokin Fitillun Bada Hannu A Titinan Jihar