HausaTv:
2025-06-30@22:21:16 GMT

 ‘Yan Hamayyar Tanzaniya Sun Ki Amincewa Da Hana Su Shiga Zabe

Published: 16th, April 2025 GMT

Jam’iyyar Hamayyar siyasa ta “Chadema” a kasar Tanzania ta ki amincewa da matakin gwamnatin kasar na haramta mata shiga manyan zabukan da za a yi a watan Oktoba.

Hukumar zaben kasar ta Tanzania ta zargi jam’iyyar Chameda’ da cewa ta ki amincewa ta rattaba hannu akan dokokin zabe, tana mai yin kira gare ta da ta girmama hukumar zaben kasar.

A ranar Asabar din da ta gabata ne dai babbar jam’iyyar adawa ta kasar Tanzania ta kauracewa halartar taron da aka yi wanda ya kunshi dukkanin jam’iyyun siyasa da su ka rattaba hannu akan dokokin zabe. Rattaba hannu akan dokokin dai yana a matsayin daya daga cikin sharuddan shiga cikin zabe da jam’iyyu za su yi,kamar yadda Ramadhani Kalima, daraktan hukumar zaben kasar ya fada wa manema labaru.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar Chadema  Regemeleza Nshala  ya bayyana matakin na  hukumar zaben da cewa ya saba wa doka. Haka nan kuma ya kara da cewa,abinda doka ta ce, duk jam’iyyar da ba ta rattaba hannu akan dokoki za a ci tararshi, ba hana shi shiga zabe ba.

An kama shugaban jam’iyyar ta Chameda,Tundu Lissu a yayin da ya shiga cikin zanga-zangar da take yin kira da a sauya dokokin zabe kafin lokacin zaben ya zo.

Jami’an ‘yan sanda sun yi awon gaba da shugaban jam’iyyar ta adawa, an kuma zarge shi da cin amanar kasa.

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama sun zargi gwamnatin kasar ta Tanzania da amfani da dabaru mabanbanta  na cutar da jam’iyyar ta jam’iyyar adawa. Gwamnatin kasar ta Tanzania ta yi watsi da zargin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, yana daukar shugaban hukumar makamashin Nukliya ta duniya IAEA Rafael Grosi a matsayin wanda ya ingiza HKI kaiwa kasar Iran hare-hare a ranar 13 ga watan Yuni. Ya kuma kara da cewa, Grossi a halin yanzu ya matsa yana son zuwa kasar Iran don ya dubi irin barnan da Amurka ta yiwa cibiyoyin nukliyar kasar Amma Iran ta ce ba zata bashi daman haka ba.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X ya kuma kara da cewa tuni majalisar dokokin kasar suka jingije aiki da hukumar saboda halayen munafursi na shugaban hukumar ta IAEA zuwa lokacinda Iran ta fahinci cewa za’a mutunta hakkinta.

Ministan ya kammala da cewa wannan shi ne sakamakon ayyukan Gorossi na munafurci a huldarsa da kasar Iran a hukumarsa.

Jiragen yakin Amurka samfurin B2 sun kai hare-hare a kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran guda 3 Natanz Fordo da kuma Esfhan. Trump ya bayyana cewa sun lalatasu kwata-kwata amma amma Iran ta musanta hakan, ta dai yarda an lalata wasu gine-gine kusa da su, amma ba mai hana aikin nukliya ya ci gaba ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  •  Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya
  • Kasashen Dimokaradiyyar Congo Da Ruwanda Sun Rattaba Hannu Kan Yrajejeniyar Zaman Lafiya
  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
  • Majaliar Dokokin Kasar Corsica Ta Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu Sannan Ta Ki Amincewa Da HKI
  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar