Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa
Published: 16th, April 2025 GMT
An yanke wa tsohon shugabar ƙasar Peru, Ollanta Humala hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari.
Wata kotu a ƙasar ce ta yanke masa hukuncin bisa samunsa da laifin halatta kuɗin haram a badaƙalar cin hanci da katafaren kamfanin gine-gine na Brazil Odebrecht ke yi don samun kwangila.
Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da LitininHaka kuma, ita ma mai ɗakinsa, Nadine Heredia, an yanke mata makamancin wannan hukuncin, duk da cewa ba ta halarci zaman kotun ba, saboda haka alƙalin ya bayar da umarnin kamo ta.
Ollanta Humala, mai shekaru 62, ya kasance tsohon shugaban ƙasar Peru na biyu da aka samu da laifi, lamarin da ya sa nan take aka kai shi wani gidan yari da ke gabashin Lima, inda ake tsare da tsoffin shugabannin kasar Peru Alejandro Toledo da Pedro Castillo.
Wannan hukuncin na zuwa ne sama da shekaru uku da fara shari’ar Humala wanda ya mulki ƙasar Peru daga 2011 zuwa 2016 —amma dai lauyoyinsa sun bayanna cewa za su ɗaukaka ƙara.
Ma’aikatar Shari’a ta Amurka ta ce Kamfanin Odebrecht ya ba da cin hanci dala miliyan 788 a cikin shekaru goma ga gwamnatocin yankin Latin Amurka domin samun kwangilar gine-gine.
Kamfanin ya bayyana cewar ya bayar da dala miliyan 29 na cin hanci ga Peru a tsakanin 2005 da 2014.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa
Rahotanni daga Jamhuriyar Benin na cewa am kama wasu 12 bayan yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba da jijjibin safiyar Lahadin nan.
Tun da farko dama fadar shugaban kasar ta ce har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin.
Ministan harkokin cikin gida na Jamhuriyar Benin ya bayyana a gidan talabijin din kasar cewa yunkurin juyin mulkin da wasu tsirarun sojoji suka yi bai yi nasara ba.
Wani rukunin sojojin kasar ne karkashin Laftanar Kanar Pascal Tigri ya sanar da hambare Shugaba Patrice Talon tare da dakatar da tsarin mulki a kafar talabijin din.
Mr Talon, mai shekaru 67, ana sa ran zai mika mulki a watan Afrilu na shekara mai zuwa bayan shekaru 10 a kan mulki.
Tuni Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta bayyana cewa “ta yi Allah wadai da yunkurin juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Patrice Talon da karfi kuma ta yi kira ga sojoji da su koma sansaninsu.
Ita ma kungiyar ECOWAS ta bayyana matukar damuwa bayan samun rahotannin yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, kungiyar ta soki abin da ta kira “yunkurin da ya saba wa tsarin mulki” wanda ke nufin take wa jama’ar Benin muradunsu.
A cewar ECOWAS, duk wani yunƙurin karɓe mulki ta hanyar ƙarfi barazana ce kai tsaye ga mulkin dimokuraɗiyya da zaman lafiya a yankin.
Yunkurin juyin mulkin na Benin na zuwa ne bayan wanda ya wakana a kasashen Mali, Burkina Faso, Nijar, Guinea sai kwanan nan a Guinea-Bissau.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci