Aminiya:
2025-10-15@19:39:54 GMT

NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato

Published: 15th, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yanzu haka, al’ummar Filato na cikin fargaba da tashin hankali sakamakon jerin hare-haren da suka afku a wasu sassan jihar, inda daruruwan mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka tsere daga muhallansu.

Ko mene ne dalilin sake dawowar rikice-rikicen da suka dabaibaye yankin da ake ganin an fara samun zaman lafiya?

NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan rikice rikicen Jihar Filato da dalilan aukuwarsu.

Domin sauke shirin, latsa nan: https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16978635-dalilan-rikice-rikice-a-jihar-filato.mp3?download=true

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Filato

এছাড়াও পড়ুন:

Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEF

Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta zuba jari a fannin kayan aikin wanke hannu da kuma ilimin tsafta.

Asusun ya kuma ce kaso 35 cikin 100 na makarantu ne kawai ke da kayan wanke hannu na asali, yayin da kashi 8 cikin 100 na ’yan Najeriya ne kawai ke iya nuna yadda ake wanke hannu daidai.

Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike

Yayin wata ziyara da aka kai makarantu a Jihar Borno a ranar Laraba, a wani ɓangare na bikin Ranar Wanke Hannu ta Duniya ta shekarar 2025, Shugabar Ofishin UNICEF a Maiduguri, Dr. Marie Marcos, ta ce zuba jari a kayan wanke hannu zai ƙara adadin masu zuwa makaranta, inganta lafiyar al’umma, da kuma ƙara ƙwarewa a wuraren aiki.

A cewarta, yankin Arewa maso Gabas ne ke matsayi na biyu a Najeriya dangane da gidaje da ke da wuraren wanke hannu da ruwa da sabulu.

Marie ta ce, “Duk da cewa kaso 99 cikin 100 na ’yan Najeriya sun san lokacin da ya dace a wanke hannu, kashi 8 cikin 100 ne kawai ke iya nuna yadda ake wanke hannu daidai.

“Kaso 17 cikin 100 na gidaje ne ke da damar samun tsafta na asali. Kaso 35 cikin 100 na makarantu ne ke da kayan wanke hannu da ruwa da sabulu.”

“Arewa maso Gabas na matsayi na biyu a Najeriya dangane da gidaje da ke da wuraren wanke hannu da ruwa da sabulu, duk da cewa adadin ya yi kadan a matakin ƙasa baki ɗaya, wato kaso 22.1 cikin 100,” in ji ta.

Sai dai ta ce UNICEF, ta hannun Gwamnatin Jihar Borno, ta tallafa wajen kafa tsarin wanke hannu a makarantu 50 a faɗin jihar, wanda ke kare kusan ’yan makaranta 20,000 a halin yanzu.

“A Jihar Borno, kaso 14 cikin 100 na gidaje ne ke da kayan wanke hannu da sabulu da ruwa. Kashi 20 cikin 100 na makarantu ne ke da kayan tsafta na asali,” in ji ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Kaso 92 cikin 100 na ’yan Najeriya ba su iya wanke hannu ba — UNICEF
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa