NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato
Published: 15th, April 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A yanzu haka, al’ummar Filato na cikin fargaba da tashin hankali sakamakon jerin hare-haren da suka afku a wasu sassan jihar, inda daruruwan mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka tsere daga muhallansu.
Ko mene ne dalilin sake dawowar rikice-rikicen da suka dabaibaye yankin da ake ganin an fara samun zaman lafiya?
NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan rikice rikicen Jihar Filato da dalilan aukuwarsu.
Domin sauke shirin, latsa nan: https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16978635-dalilan-rikice-rikice-a-jihar-filato.mp3?download=true
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Filato
এছাড়াও পড়ুন:
An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
Aƙalla ’yan Najeriya 32 ne aka koro su daga Indiya kan zargin su da hannu a kasuwancin miyagun ƙwayoyi.
A ƙarshen watan da ya gabata, ’yan sandan Delhi da na Telangana, sun kama ’yan Najeriya 50 biyo bayan samamen da suma kai wa wata ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi mai alaƙa da ƙasashen waje.
Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPCAna zargin mutanen da rarraba ƙwayoyi a birane da dama a Indiya, inda suke amfani da kamfanonin bayar da kaya don ɓoye ƙwayoyin da suke safara.
An gano mutanen suna da alaƙa da wani ɗan Najeriya mai suna “Nick,” wanda ake nema ruwa a jallo, kuma ana zargin yana jagorantar wannan ƙungiyar daga Najeriya.
Wasu majoyi sun bayyana cewa yana da abokan aiki aƙalla 100 a Delhi.
Masu bincike sun ce ƙungiyar tana da waɗanda ke aiki a ƙarƙashinta sama da 3,000 a Indiya kuma tana aika manyan kuɗaɗe zuwa Najeriya.
Daga cikin waɗanda aka kama, an koro ’yan Najeriya 32, yayin da wasu bakwai ke fuskantar tuhumar shari’a.
Hukumomi a ƙasar sun ana ci gaba da ce bincike.