HausaTv:
2025-12-06@02:23:13 GMT

Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba

Published: 14th, April 2025 GMT

Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya  zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.

Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.

 

Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.

Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”

Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Jirgin Fadar Shugaban Kasa da Gwamnatin Najeriya ta saka a kasuwa da nufin sayarwa ya kasa samun mai saye kusan watanni biyar bayan ɗora shi a dandalin sayar da jiragen sama na duniya.

A sakamakon haka, tuni ma kamfanin dillancin da ke kula da sayar da jirgin samfurin Boeing 737-700 Business Jet ya janye jerin sayar da shi daga shafinsa.

’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe

Jaridar Punch ta rawaito cewa jirgin da a baya aka saka a shafin kamfanin, yanzu an cire shi daga kai.

A cikin wata amsa ga sakon imel, Laurie Barringer wanda shi ne Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, ya tabbatar da cewa kamfanin ya cire jirgin daga jerin sayarwa, inda ya ce a nemi karin bayani daga Gwamnatin Najeriya.

“Mun gode da sakonku. Ba mu da jerin Boeing yanzu a shafinmu. Sai dai ku tuntubi Gwamnatin Najeriya don samun bayani kan abin da ya faru da jirgin. Na gode da lokacinku — Laurie Barringer, Manajan Binciken Kasuwanci, JetHQ,” in ji sakon.

Hadimin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa, Ismail Garba, ya yi alƙawarin bayar da amsa amma bai yi hakan ba har bayan kwanaki da dama.

Mataimakin Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, Marinell Nuevo, ya tabbatar da cewa jirgin “yana nan a kasuwa” amma ya tura karin tambayoyi zuwa Barringer.

Daga baya Barringer ya bayyana cewa kamfanin ba zai bayyana wasu bayanai fiye da kasancewar jirgin a kasuwa ba, yana mai cewa irin wannan bayani na sirri ne.

“Ba ma bayar da irin wadannan bayanan ga kowa sai ga mamallakin jirgin kai tsaye. Ana ɗaukar wannan bayani a matsayin sirri. Ina fatan za ku fahimta. Abin kawai da za mu iya bayarwa shi ne cewa jirgin yana nan a kasuwa,” in ji Barringer.

Kafin a cire shi daga jerin sayarwa, bayanai sun nuna cewa an yi wa jirgin gyare-gyare a watan Yuli 2024, ciki har da gyaran kujerun ajin farko, sauya kafet na cikin jirgi da sauran kananan gyare-gyare.

A cewar aircraftcostcalculator.com, jirgin Boeing 737 BBJ da aka taɓa amfani da shi darajarsa a kasuwa ta kai kusan $56m, kwatankwacin Naira sama da Naira biliyan 82.

An sayi jirgin a shekarar 2005 a kan $43m a zamanin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, kuma ya kasance wani jerin jiragen Fadar Shugaban Ƙasa.

A watan Yuli 2025, gwamnatin Tinubu ta sanar da shirin sayar da jirgin a matsayin wani ɓangare na dabarar rage kashe kuɗi da daidaita yawan jiragen, a yayin da jama’a ke ƙara sa ido kan yadda gwamnati ke kashe kuɗade.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Iran Da Pakisatan Sun Amince ِDa Dawoda Layin Dogo Tsakanin Istambul, Tehran Zuwa Islamabad
  • Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro
  • DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro