HausaTv:
2025-09-18@22:56:47 GMT

Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba

Published: 14th, April 2025 GMT

Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya  zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.

Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.

 

Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.

Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”

Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Benfica ta naɗa Jose Mourinho sabon kociyanta

Benfica ta sanar da naɗa José Mourinho a matsayin sabon kociyanta, domin maye gurbin Bruno Lage, wanda ƙungiyar ta karo bayan da Qarabag ta doke ta a gasar Zakarun Turai ranar Talata.

Benfica ta kori Lage duk da cewa wasa ɗaya kawai ya yi rashin nasara a dukkanin gasa a bana.

Wata sanarwa da Benfica ta fitar a ranar Alhamis ta bayyana cewa, Mourinho mai shekaru 62 zai jagoranci ƙungiyar har zuwa kakar wasanni ta 2026/2027, tare da zaɓin raba gari a ƙarshen kakar nan.

An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar

Tsohon kociyan Chelsea, Real Madrid da Manchester United, ya dawo Benfica ne bayan ya rasa aiki a watan Agusta, wata ɗaya bayan da Fenerbahce ta kore shi sakamakon rashin samun gurbin Gasar Zakarun Turai.

Mourinho ya fara aiki a matsayin koci a Benfica a shekarar 2000, amma ya bar aiki bayan wasanni 11 kacal saboda saɓani da shugabanninta, lamarin da ya ba shi damar koma wa Porto, ƙungiyar da ya daukarwa kofin Zakarun Turai a 2004.

Tun da ya bar Benfica shekaru 25 da suka gabata, Mourinho ya yi aiki da manyan ƙungiyoyi kamar Chelsea, Inter Milan, Real Madrid, Tottenham, Roma da kuma Fenerbahce.

Ya lashe kofin Firimiyar Ingila guda uku, da La Liga, da Serie A, da Champions League guda biyu.

Sai dai daga 2017 zuwa yanzu, babban kambin da ya samu shi ne wanda ya lashe na Gasar Conference League da Roma a shekarar 2022.

A halin yanzu, Benfica tana matsayi na shida a teburin babbar gasar Portugal —Primeira Liga— da tazarar maki biyar tsakaninta da Porto, amma da kwantan wasa ɗaya.

Wasa na farko da Mourinho zai ja ragamar ƙungiyar da ke birnin Lisbon shi ne na ranar Asabar mai zuwa da AVS.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Benfica ta naɗa Jose Mourinho sabon kociyanta
  • Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kaduna Ranar Juma’a
  • Hukumar Alhazai Ta Jigawa Za Ta Shirya Taron Bita Na Musamman Ga Jami’anta
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna