Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
Published: 14th, April 2025 GMT
Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.
Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.
Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.
Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”
Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa
Rahotanni daga Jamhuriyar Benin na cewa am kama wasu 12 bayan yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba da jijjibin safiyar Lahadin nan.
Tun da farko dama fadar shugaban kasar ta ce har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin.
Ministan harkokin cikin gida na Jamhuriyar Benin ya bayyana a gidan talabijin din kasar cewa yunkurin juyin mulkin da wasu tsirarun sojoji suka yi bai yi nasara ba.
Wani rukunin sojojin kasar ne karkashin Laftanar Kanar Pascal Tigri ya sanar da hambare Shugaba Patrice Talon tare da dakatar da tsarin mulki a kafar talabijin din.
Mr Talon, mai shekaru 67, ana sa ran zai mika mulki a watan Afrilu na shekara mai zuwa bayan shekaru 10 a kan mulki.
Tuni Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta bayyana cewa “ta yi Allah wadai da yunkurin juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Patrice Talon da karfi kuma ta yi kira ga sojoji da su koma sansaninsu.
Ita ma kungiyar ECOWAS ta bayyana matukar damuwa bayan samun rahotannin yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, kungiyar ta soki abin da ta kira “yunkurin da ya saba wa tsarin mulki” wanda ke nufin take wa jama’ar Benin muradunsu.
A cewar ECOWAS, duk wani yunƙurin karɓe mulki ta hanyar ƙarfi barazana ce kai tsaye ga mulkin dimokuraɗiyya da zaman lafiya a yankin.
Yunkurin juyin mulkin na Benin na zuwa ne bayan wanda ya wakana a kasashen Mali, Burkina Faso, Nijar, Guinea sai kwanan nan a Guinea-Bissau.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci