Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
Published: 14th, April 2025 GMT
Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.
Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.
Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.
Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”
Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya ce yawan yara marasa zuwa makaranta a Najeriya a barazana ce da ke buƙatar haɗin gwiwa daga dukkan matakan gwamnati da masu ruwa da tsaki.
Shettima ya yi wannan bayani a taron Zauren Ilimin Najeriya na 2025 da aka gudanar a Abuja, wanda Kungiyar Gwamnonin Najeriya tare da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da abokan hulɗa suka shirya.
Ya ce matsalar ilimi ba za ta iya warwarewa da ƙoƙarin gwamnati kaɗai ba, yana mai jaddada cewa: “Yawan yaran da ba sa zuwa makaranta bukatar gaggawa ce ta ƙasa da ke buƙatar haɗin kai tsakanin Gwamnatin Tarayya, jihohi, kananan hukumomi da al’umma.”
Shettima, wanda mai ba shi shawara na musamman Aliyu Modibbo Umar ya wakilta, ya ce dole malamai su samu horo mai kyau, kulawa da kuma kima a matsayinsu na ƙwararru domin a samu ingantaccen ilimi.
An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa GubaYa kuma yi kira da a faɗaɗa ilimin sana’o’i da fasaha domin matasa su samu ƙwarewar da za ta taimaka musu a kasuwa. Ya ce hakan na buƙatar kuɗi masu dorewa da aka tsara yadda ya kamata.
Mataimakin Shugaban Kasa ya bayyana cewa duk da ƙarin kuɗin da gwamnati ta ware wa ilimi daga Naira tiriliyan 1.54 a 2023 zuwa Naira tiriliyan 3.52 a 2025, gibin kuɗi ya yi yawa fiye da abin da gwamnati za ta iya ɗauka ita kaɗai.
Ya ambaci ƙarin kuɗin da aka ware wa hukumar TETFUND, UBEC da asusun tallafin ilimi na NELFUND, ciki har da Naira biliyan 86.3 da aka raba wa ɗaliban jami’a sama da 450,000 a ƙarƙashin tsarin lamunin ɗalibai.
Sai dai ya jaddada cewa gina tsarin ilimi mai ɗorewa na buƙatar haɗin gwiwa daga kamfanoni masu zaman kansu, shugabannin masana’antu, ƙungiyoyin tsoffin ɗalibai, masu bayar da tallafi da al’umma.
Shettima ya ce: “Dole mu wuce tsarin gwamnati kaɗai wajen bayar da kuɗi, mu rungumi haɗin gwiwa da zai tallafa wa dakunan gwaje-gwaje, cibiyoyin bincike, cibiyoyin sana’o’i, ƙungiyoyin kirkire-kirkire da asusun tallafi.”
Ya kuma bukaci kananan hukumomi da masarautu su ɗauki nauyin gine-ginen makarantu, gyara, tsaro da kuma kulawa da malamai.
Shettima ya yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a taron da su jajirce wajen samar da kuɗin ilimi mai dorewa, yana mai cewa haɗin kai ne kaɗai zai iya sauya tsarin ilimi a Najeriya tare da shirya matasa domin fuskantar duniyar zamani.