HausaTv:
2025-12-14@20:14:27 GMT

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Taɓarɓarewar rashin tsaro ya nuna rashin shugabanci na gari — Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ce taɓarɓarewar rashin tsaro a Najeriya na nuna gazawar shugabanci.

Ya yi kira da a gudanar da bincike mai zurfi cikin gaggawa kan zargin wasu jami’an gwamnati da taimaka wa ’yan ta’adda.

Buɗe cibiyar horas da sabbin sojoji a Kudu zai taimaka — Janar Shaibu Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano

Obi, ya bayyana hakan ne bayan wani bidiyo da aka yaɗa a kafafen sada zumunta, inda wasu da ake zargin ’yan ta’adda ne suka ce jami’an gwamnati ne ke taimaka musu da makamai.

Ya ce wannan zargi abu ne mai matuƙar muhimmanci da bai kamata a yi watsi da shi ba.

“An ga wani bidiyo mai tayar da hankali a Jihar Kwara inda waɗanda aka kama suka ce jami’an gwamnati ne suka ba su harsasai da kayan aiki.

“Wannan zargi na buƙatar bincike cikin gaggawa kuma a bayyane.”

Obi ya ce duk da maƙudan kuɗaɗen da aka kashe a fannin tsaro tsawon shekaru, rashin tsaro na ƙara taɓarɓarewa a ƙasar.

“An kashe tiriliyoyin juɗi da biliyoyin daloli a fannin tsaro, amma duk da haka rashin tsaro na ƙara taɓarɓarewa a faɗin ƙasar nan.”

Ya kuma tambayi dalilin da ya sa ba a amfani da na’urorin zamani da fasahar tsaro wajen gano da kama ’yan ta’adda, duk da cewa ƙasar na da irin waɗannan damarmaki.

“Gwamnati na da iko da hanyoyin sadarwa, bayanan sirri da bin sahun kuɗaɗe, amma duk da haka satar mutane da ta’addanci na ci gaba da ƙaruwa.”

Obi ya kuma soki yadda ake murnar sakin waɗanda aka sace ba tare da kama waɗanda suka aikata laifin ba, inda ya ce hakan na nuna rashin ɗaukar al’amarin da muhimmanci.

A ƙarshe, ya yi gargaɗin cewa ƙaruwar rashin tsaro na nuni da gazawar gwamnati da kuma yin sakaci, inda ya jaddada cewa babban aikin kowace gwamnati ne kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taɓarɓarewar rashin tsaro ya nuna rashin shugabanci na gari — Obi
  • Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha
  • Araghchi ya bukaci Amurka da ta girmama al’ummar Iran da gwamnatin da ta zaba
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Birtaniya Ta yi  Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa