HausaTv:
2025-12-12@17:45:03 GMT

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699

Matatar man Dangote ta sake rage farashin man fetur ɗin da take sayar da man, inda ta rage farashin man fetur ɗin daga Naira 828 zuwa Naira 699 kan kowace lita.

Bayanan farashin da aka wallafa a shafin  kasuwancin farashin man fetur a Petroleumprice.ng a ranar Juma’a sun nuna cewa matatar ta aiwatar da wani bita na baya-bayan nan, inda ta rage farashin man da N129 a kowace lita – ragin kashi 15.58 cikin 100.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina

Wani jami’in matatar man da ya zanta da manema labarai bisa sharaɗin sakaya sunansa saboda ba shi da izinin yin tsokaci a bainar jama’a, shi ma ya tabbatar da yin ragin.

Ya ce, matatar man ta rage farashin man fetur zuwa N699 kowace lita.

Sabon farashin ya fara aiki ne daga ranar 11 ga watan Disamba, 2025, wanda ya yi daidai da farashin man fetur karo na 20 da matatar man ta sanar a bana.

Ragi na baya-bayan nan ya zo ne kwanaki biyar bayan shugaban matatar, Aliko Dangote ya jaddada ƙudirinsa na ganin an tabbatar da farashin man fetur a cikin gida cikin “madaidaicin farashi a kasuwanni” duk kuwa da taɓarɓarewar da ake samu a duniya da fasaƙwaurin da ake yi a kan iyakokin Najeriya.

Da yake bayani bayan ganawar sirri da shugaban Najeriya, Bola Tinubu a ranar 6 ga watan Disamba, Dangote ya ce farashin zai ci gaba da faɗuwa yayin da matatar man ke ƙara yawan kayan da ake fitarwa da kuma yin gogayya kai tsaye da kayayyakin da ake shigowa da su daga ƙasashen waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Birtaniya Ta yi  Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim