HausaTv:
2025-12-01@13:17:33 GMT

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka

Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana cewa yana shirin daina karɓar mutane daga “ƙasashe masu tasowa” gaba ɗaya, ciki har da Afirka, Asiya da sauransu.

Ya bayyana haka ne yayin wani taro da ya gudana a fadar shugaban Amurka.

Ƙasar Japan ta fara sayar da i njin da ke yi wa mutane wanka

A cewarsa, tsohon tsarin shige da fice na Amurka yana rage ƙarfin tsaron ƙasa kuma yana matsa wa makarantun gwamnati, asibitoci, da sauran hidimomin jama’a.

Trump ya ce yawan baƙin haure a Amurka ya kai mutane miliyan 53, sannan ya yi zargin cewa mutane daga ƙasashen da ke fama da rikice-rikice, laifuka, da miyagun ƙungiyoyi suna ta zuwa ƙasar.

Ya ce shigowar baƙi ya kawo rabuwar kawuna da matsaloli a Amurka.

Haka kuma ya yi zargin cewa masu katin zama ’yan ƙasar da ke da tsarin ƙaramin albashi na rikice-rikice.

Ya batar da misali da Jihar Minnesota, yana inda ’yan gudun hijira daga Somaliya suka cika ta

Ya ce “ci gaban ƙasa ya lalace,” amma ya bayyana matakan da zai ɗauka.

Ya kuma ce zai soke shiga ƙasar ba bisa ƙa’ida ba wanda gwamnatin Biden ta bari ke faruwa.

Trump, ya ce burinsa shi ne rage yawan waɗanda yake ganin ba su da tasiri mai kyau ko kuma suna kawo matsala a ƙasar.

Ya ce “mayar da mutane ƙasashensu” shi ne kawai mafita mai ɗorewa.

Wannan sanarwa na zuwa ne bayan harin da aka kai a Washington, D.C, inda aka yi wa sojoji biyu rauni.

Hukumomi a ƙasar sun ce mutumin da ake zargi da kai harin, ya shiga Amurka a 2021 bayan ya taimaka wa sojojin ƙasar a Afghanistan, kuma an ba shi mafaka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
  • Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5
  • Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya
  • Larijani: Da’awar lalata karfin nukiliyar Iran wauta ce
  • Iran Za ta Kauracewa taron fasalta kasashen da za su halarci  gasar cin kofin duniya na shekara ta 2026
  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
  • Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka