Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
Published: 14th, April 2025 GMT
Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.
Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.
A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”
Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.
A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kebbi, Muhammad Sama’ila Bagudo, ya kuɓuta bayan shafe fiye da mako guda a hannun ’yan bindigar da suka yi garkuwa da shi.
Aminiya ta ruwaito cewa an sace mataimakin shugaban majalisar ne a ranar Juma’a 31 ga Oktoba, 2025, jim kaɗan bayan ya kammala sallar la’asar a masallacin garinsu na Bagudo.
’Yan bindiga sun kashe kansila yayin Zaɓen Gwamnan Anambra Gwamna Soludo ya lashe Zaɓen Anambra karo na biyuSakataren gwamnatin jihar, Yakubu Tafida, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin Asabar.
Bayanai sun tabbatar da cewa lamarin na zuwa ne daidai da lokacin da aka gudanar da addu’o’in haɗin kai tsakanin Musulmai da Kiristoci domin neman zaman lafiya a jihar.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kebbi, CSP Nafiu Abubakar, ya tabbatar da cewa an saki mataimakin shugaban majalisar.
CSP Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka yana tare da iyalansa bayan mahukunta sun tabbatar da ƙoshin lafiyarsa a wani asibiti.
“An sace shi a ranar 31 ga Oktoba, amma an sako shi jiya [Asabar] kuma yanzu yana cikin ƙoshin lafiya kamar yadda mahukunta suka tabbatar,” in ji kakakin rundunar.
Ya ƙara da cewa rundunar ta yaba da jajircewar jami’an tsaro da suka shiga aikin ceto tare da goyon bayan al’umma, inda ya ce bayanan da jama’a suka bayar sun taka muhimmiyar rawa wajen ceto wanda aka sace lafiya.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za ta ci gaba da kai hare-hare kan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a faɗin jihar, tare da kira ga jama’a su kasance masu lura da duk wani motsi da ake zargi su kuma rika sanar da hukumomin tsaro cikin gaggawa.