HausaTv:
2025-10-28@13:59:19 GMT

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Masu yabon Buhari sun yi masa ba’a bayan ya sauka daga mulki —Gwamna Sule

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce wasu daga cikin mutanen da saba yabon tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari lokacin yake kan mulki, su ne suka fara yi masa ba’a tare da suka bayan ya sauka daga mulki.

Da yake jawabi a wani taron “Lakcar Raymond Dokpesi” da Ƙungiyar Masana Hulɗa da Jama’a ta Najeriya (NIPR) ta shirya a birnin Abuja, Gwamna Sule ya ce ya shaida da idonsa yadda wasu ’yan siyasa ke yabo da fadanci a gaban Buhari, amma daga bisani su sauya baki sheƙa da zarar shugabannin sun bar mulki.

Ya ce, “Tun da na zama gwamna, na ga abin da son kai da kwaɗayi ke iya haifarwa. Na ga mutane suna zaune a gaban Shugaba Buhari suna cewa, ‘Kai ka fi kowa, babu wanda zai iya yin wannan kamar kai.’

“Amma bayan saukar Buhari daga mulki, sai suka fara cewa, ‘Ai, yana cikin shugabannin mafiya rauni.’ Waɗannan mutanen ɗaya ne, amma lokaci ne ya bambanta. Wannan shi ne kwaɗayin yabo da son kai,” in ji shi.

Mai mata ɗaya abin tausayi ne — Sanata Nwoko Saukar Farashin abinci: Manoma da gwamnati na nuna wa juna yatsa

A wajen taron, an karrama Gwamna Sule da kyauta da kuma lambar girmamawa ta NIPR, inda ya bayyana farin cikinsa da irin jarumtakar marigayi Cif Raymond Dokpesi, wanda ya kafa tashoshin rediyo da talabijin na farko masu zaman kansu a ƙasar tun lokacin mulkin soja.

“Ina nan ne don mu taya murna da tunawa da gwarzon kafafen yaɗa labarai. Dokpesi mutum ne mai gaskiya da jajircewa wajen faɗin gaskiya ga masu mulki, ko da a lokutan da suka fi wuya,” in ji Gwamna Sule.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkian: Hadin Kai A Tsakanin Kasashen Gabas Ta Tsakiya Ba Zabi Ba Ne, Amma Dole Ne
  • Wilayati: Kasashen Ian, China Da Rasha Suna Taka Rawa A Fagen Kafa Sabon Tsarin Duniya
  • Pezeshkian: Hadin kan Musulmi zai iya dakile zalincin kasashen waje
  • Iran ta bukaci MDD ta nisanci nuna bangaranci game da masu keta dokokin duniya  
  • Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
  • Paul Biya mai shekara 92 ya lashe zaɓen Kamaru
  • Masu yabon Buhari sun yi masa ba’a bayan ya sauka daga mulki —Gwamna Sule
  • An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Shugaban Amurka Zai Ci Gaba Da Kasancewa Cikin Rudu
  • Dan Majalisar Dokokin Tarayyar Turai Ya Ce: Dole Ne A Hakunta Isra’ila Kan Laifukan Da Ta Aikata