HausaTv:
2025-12-01@00:01:35 GMT

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe

Cibiyar HANs Centre for Social Justice and Development tare da Kanady Academy, sun kammala horon kwana uku domin koya wa yara marasa galihu da matasa mata sana’o’in dogaro da kai a Jihar Gombe.

Shugabar HANs, Barista Hannatu Dauda Simon, ta ce an shirya horon ne domin ƙarfafa gwiwar mahalarta, tare da koya musu yadda za su iya rayuwa ba tare da dogaro da wasu ba.

Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali

Ta ce halin tattalin arziƙin ƙasar nan ya ƙara nuna muhimmancin sana’ar hannu ga matasa.

Ta bayyana cewa matasa mata 100, ciki har da ɗaliban Kanady Academy ne, suka halarci horon.

Masu horarwa daga fannoni daban-daban sun koya wa matasan sana’o’i kamar:

– Yin takalmi

– Yin burodi

– Kwalliya

– Turaren wuta

– Sarrafa kilishi

– Kula da shagunan kaya

– Da sauran sana’o’in dogaro da kai.

Ta yaba da yadda mahalarta suka dage a lokacin horon, tana mai cewa za su yi baje kolin abin da suka koya nan gaba domin nuna ƙwarewarsu.

Ta kuma ce ilimin da aka ba su zai taimaka musu wajen samun abin dogaro da kai.

Wasu daga cikin mahalartan sun bayyana farin cikinsu, inda suka bayyana cewa horon ya taimaka musu gano sana’ar da ta dace da su.

Haka kuma sun yi godiya kan kayan aikin da aka ba su domin su fara ƙananan sana’o’i.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5
  • Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya
  • Larijani: Da’awar lalata karfin nukiliyar Iran wauta ce
  • Iran Za ta Kauracewa taron fasalta kasashen da za su halarci  gasar cin kofin duniya na shekara ta 2026
  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
  • Yamen Ta Soki Kasashen Birtaniya Da Amurka Da Tsoma Baki Kan harkokin Kasarta
  • Ministocin Tarayyar Turai Sun yi Tir Da Karuwar Hare –Haren Da Yahudawa Ke Kai wa Falasdinawa
  • Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulki ya ritsa da shi a Guinea-Bissau