Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi
Published: 14th, April 2025 GMT
Kasashen Iran da kuma Iraki sun kudiri anniyar karfafa alaka ta fuskar makamashi.
A ganawar da suka yi a birnin Bagadaza, kasashen biyu sun jaddada fadada hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannin mai da iskar gas, inda kasar Irakin ta bayyana matukar sha’awar yin hadin gwiwa a fannin fasaha da zuba jari da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Taron ya yi nuni da karfafa huldar dabarun samar da makamashi tsakanin kasashe biyu masu makwabtaka da juna.
Mataimakin firaministan kasar Iraki mai kula da harkokin makamashi Hayan Abdul-Ghani Al-Sawad ya bayyana cewa, Iraki na ci gaba da gudanar da ayyukan da ke da nufin cimma dogaro da kai wajen samar da albarkatun man fetur.
Ya jaddada aniyar Bagadaza na fadada hadin gwiwar fasaha da kuma jawo hannun jarin Iran a bangaren makamashi na Iraki.
Iraki na da burin rage dogaro da man fetur da ake shigowa da su daga kasashen waje kuma tana kallon Iran a matsayin babbar abokiyar huldar cimma wannan buri saboda ci gaban da take da shi na tace man.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Raya Ranar Haramta Takunkuman Bangare Guda A Duniya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baghaei ya yi tir da takunkuman tattalin arzikin da kasar Amurka take ci gaba da dorawa JMI na shekaru masu yawa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bada nakalto Baghaei yana fadar haka a dai dai ranar tunawa da ranar haramcin takunkuman tattalin arziki na bangare guda ta kasa da kasa wacce ba’a dade da samar da ita a farkon wannan shekarar.
Isma’el Baghaei ya bayyana haka ne a shafinsa na X a jiya Alhamis, inda yayi tir da Amurka wace ta fara fara dorawa JMI takunkuman tattalin arziki tun fiye da shekaru fiye da 40 da suka gabata. Kuma hakan take hakkin bil’adama.
Yace a farkon wannan shekarar ne dai babban zauren MDD ta samar da kuduri mai lamba 79/293 inda ta bayyana takunkuman tattalin arziki na bangaren guda ko kasar guda, baya bias ka’ida kuma duk kasar da ta yi haka tana take hakkin bil’adama a kan kasar da ta dorawa.
Majalis ta sanya ranar 4 gawatan Decemba na kowace shekara a matsayin ranar haramta takunkuman tattalin arziki na bangare guda. Wato MDD ce kadai take da alhakin dorawa wata kasa takunkuman tattalin arziki.
Yace takunkuman da gwamnatin kasar Amurka ta dorawa JMI tun farkon juyin juya halin musulunci har zuwa yanzu sun yisanadiyyar kashe mutane da dama a klasar Iran. Musamman takunkuman sayan maganin cututtukan masu tsanani.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Trump Ya Yabawa Rwanda Da Kongo DMK Kan Sulhuntawa A Yakin Gabancin Kongo December 5, 2025 Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu December 5, 2025 Shin Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump? December 5, 2025 Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale December 4, 2025 Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon December 4, 2025 An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci