Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi
Published: 14th, April 2025 GMT
Kasashen Iran da kuma Iraki sun kudiri anniyar karfafa alaka ta fuskar makamashi.
A ganawar da suka yi a birnin Bagadaza, kasashen biyu sun jaddada fadada hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannin mai da iskar gas, inda kasar Irakin ta bayyana matukar sha’awar yin hadin gwiwa a fannin fasaha da zuba jari da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Taron ya yi nuni da karfafa huldar dabarun samar da makamashi tsakanin kasashe biyu masu makwabtaka da juna.
Mataimakin firaministan kasar Iraki mai kula da harkokin makamashi Hayan Abdul-Ghani Al-Sawad ya bayyana cewa, Iraki na ci gaba da gudanar da ayyukan da ke da nufin cimma dogaro da kai wajen samar da albarkatun man fetur.
Ya jaddada aniyar Bagadaza na fadada hadin gwiwar fasaha da kuma jawo hannun jarin Iran a bangaren makamashi na Iraki.
Iraki na da burin rage dogaro da man fetur da ake shigowa da su daga kasashen waje kuma tana kallon Iran a matsayin babbar abokiyar huldar cimma wannan buri saboda ci gaban da take da shi na tace man.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ya amsa tambayoyin ‘yan jaridu, dangane da soke takunkumin tattalin arziki da cinikayya da kasar Amurka ta kakabawa kasar Sin.
Kakakin ya ce, bayan tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da aka yi tsakanin kasar Sin da kasar Amurka a birnin London na kasar Burtaniya, cikin ’yan kwanakin nan, bangarorin biyu sun aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma a ranar 5 ga watan Yuni, tare da inganta ayyukan da abin ya shafa bisa sakamakon da suka cimma a taron tattaunawar tattalin arziki da cinikayya na Geneva. A halin yanzu, tawagogin Sin da Amurka suna gaggauta aiwatar da sakamakon da aka cimma bisa “tsarin London”. Kana, kasar Sin tana tantance kayayyakin da za ta ba da iznin fitarwa zuwa kasashen ketare bisa dokoki da manufofin da abin ya shafa. Kasar Amurka ma ta dauki matakan soke takunkumin da ta kakabawa kasar Sin, ta kuma sanar wa bangaren Sin bayanai game da hakan.
Da kyar bangarorin biyu suka cimma matsaya daya tare da kulla “tsarin London”, don haka ya kamata a bi hanyar yin shawarwari, maimakon kalubalanta ko tilastawa wani. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp