HausaTv:
2025-12-03@08:52:04 GMT

Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi

Published: 14th, April 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Iraki sun kudiri anniyar karfafa alaka ta fuskar makamashi.

A ganawar da suka yi a birnin Bagadaza, kasashen biyu sun jaddada fadada hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannin mai da iskar gas, inda kasar Irakin ta bayyana matukar sha’awar yin hadin gwiwa a fannin fasaha da zuba jari da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Taron ya yi nuni da karfafa huldar dabarun samar da makamashi tsakanin kasashe biyu masu makwabtaka da juna.

Mataimakin firaministan kasar Iraki mai kula da harkokin makamashi Hayan Abdul-Ghani Al-Sawad ya bayyana cewa, Iraki na ci gaba da gudanar da ayyukan da ke da nufin cimma dogaro da kai wajen samar da albarkatun man fetur.

Ya jaddada aniyar Bagadaza na fadada hadin gwiwar fasaha da kuma jawo hannun jarin Iran a bangaren makamashi na Iraki.

Iraki na da burin rage dogaro da man fetur da ake shigowa da su daga kasashen waje kuma tana kallon Iran a matsayin babbar abokiyar huldar cimma wannan buri saboda ci gaban da take da shi na tace man.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa

Ma’aikatar harkokin wajen Njgeria ta sanar da bai wa dan takarar shugabanncin  kasar Guinea Bissau, Fernando Dias da Costa, ya kuma tsaya takara ne a tare da shugaban kasar  Umar Sisoko  Embalo da sojoji su ka kifar da gwamnatinsa kwanaki kadan bayan zabe.

A ranar 27 ga watan Nuwamba ne dai Dias Da Costa ya sanar da cewa,shi ne wanda ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi, tare da zargin Embalo da cewa shi ne ya shirya juyin mulkin da ya kawo karshen zaben kasar, tun kafin a sanar da sakamakon zaben.

Haka nan kuma ya ce ya tsallake rijiya daga kokarin kama shi a ranar da aka yi jiyin Mulki, ya kuma boye, har sai da ya sami goyon bayan kasar Najeriya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, al-Kassim Abdulkadir ya ce; manufar bayar da mafaakr siyasar, shi ne kokarin hana dambaruwar siyasar a cikin kasar ta Guinea Bissau da rashin zaman lafiya a cikin yammacin Afirka.

Shi kuwa shugaban kasar da aka hambarar Embalo an tsare shi na wani lokaci, sai dai kuma an sake, shi sannan kuma ya nufi kasar Senegal domin samun mafakar siyasa. Sakin Embalo ya biyo yana tsoma bakin kungiyar tarayyar Afirka ne wacce ta yi Allawadai da juyin Mulki.

Kungiyar ta Ecowas ta aike da tawaga zuwa kasar ta Guine Bissau inda su ka gana da sojojin da su ka yi juyin Mulki. Ministan harkokin wajen Saliyo Thimothy Musa Kaba wanda ya jagoranci tawagar ya ce; Tattaunawar ta haifar da Da,mai ido. Sai dai kuma ta jadda kin amincea da juyin Mulki, tare da yin kira da a koma aiki da tsarin Mulki.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota December 2, 2025 Hamas Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji  A Yankin Gaza December 2, 2025 Ministan Tsaron Najeriya  Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu. December 2, 2025 Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango December 2, 2025 Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau December 2, 2025 An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran December 2, 2025 Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa December 2, 2025 Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Don Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi December 2, 2025 Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma December 2, 2025 Chuck Schumer: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufar
  • Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa
  • Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango
  • Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon
  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari
  • Iran ta bayyana halin da Falasdinawa ke ciki da rauni mufi da aka wa dan adam a doron kasa
  • Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5