Iran, Iraki Sun Karfafa Dangantakar Makamashi
Published: 14th, April 2025 GMT
Kasashen Iran da kuma Iraki sun kudiri anniyar karfafa alaka ta fuskar makamashi.
A ganawar da suka yi a birnin Bagadaza, kasashen biyu sun jaddada fadada hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannin mai da iskar gas, inda kasar Irakin ta bayyana matukar sha’awar yin hadin gwiwa a fannin fasaha da zuba jari da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Taron ya yi nuni da karfafa huldar dabarun samar da makamashi tsakanin kasashe biyu masu makwabtaka da juna.
Mataimakin firaministan kasar Iraki mai kula da harkokin makamashi Hayan Abdul-Ghani Al-Sawad ya bayyana cewa, Iraki na ci gaba da gudanar da ayyukan da ke da nufin cimma dogaro da kai wajen samar da albarkatun man fetur.
Ya jaddada aniyar Bagadaza na fadada hadin gwiwar fasaha da kuma jawo hannun jarin Iran a bangaren makamashi na Iraki.
Iraki na da burin rage dogaro da man fetur da ake shigowa da su daga kasashen waje kuma tana kallon Iran a matsayin babbar abokiyar huldar cimma wannan buri saboda ci gaban da take da shi na tace man.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
Ana taro kan yadda manzon Allah mohammad dan Abdullahi (a) ya zauna da wadanda ba musulmi ba a rayuwarsa a Madina.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto hukuma mai kula da al-adu da kuma al-amuran addinin Musulunci a nan Iran tana cewa ana gudanar da wannan taron ne a dai dai lokacinda aka fara bukukuwan cika shekaru 1500 na hijirar manzon Allah (s).
Labarin ya kara da cewa an sabi baki wadanda suka gabatar da jawabi masu muhimmanci daga kasashen Iran, Lebanon da kuma Masar.
Ahmad Mobaleghi na mamba a kwamitin al-amuran addini na hukumar ya kawo ayoyin al-kur’ani wadanda suka yi mgana kan yadda manzon Allah yayi mu’amala da yahudawan da ya samu a Madina, kuma ya ce wadannan ayoyi kekyawar misali ne nazamantakewar Musulmi da wadanda ba musulmi ba.
Louis Saliba wani marubu ce kirista daga kasar Lebanon, wanda kuma ya gabatar da Jawabinsa ta kafar Bidiyo daga kasar Lebanon yay aba da yadda manzon Allah (s) yayi mu’amala da nasaran Najran wadanda suka zo masa daga kasar yemen.
Sai kuma Abdolsalam Emami, mai bawa ma’aikatar al-adu shawara kan mabiya mazhabar sunna a nan Iran yayi magana a kan yadda manzon Allah (s) ya zauna da yahudawa a Madina ya kuma kawo misalai da dama wadanda suka shafi hakan.
Sai kuma Amani Mahmoud Ibrahim, sheikhin malami a Jami’ar Al-Azhar ta kasar Masar wanda ya kawo yadda yahudawan Madina suka saba al-kawalin da suka cimma da manzon Allah (s) a farkon hijira da kuma yadda yayi mu’amala da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci