Rundunar ‘yansandan jihar Yobe ta kama wasu mutane biyu da ake zargin barayin wayar wutar lantarki ne a Damaturu babban birnin jihar. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa, rundunar ‘yansanda ta Karasuwa ce ta kama wadanda ake zargin – Yahaya Mustapha, 28, da Bello Yakubu, 38, da misalin karfe 1:00 na rana a ranar 12 ga watan Afrilun 2025.

‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Haɗa Makamai A Kano Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum Ɗaya A Bauchi, Wasu Sun Jikkata Abdulkarim ya ce, wadanda ake zargin sun fito ne daga unguwar Takari da ke karamar hukumar Gashua Bade a jihar, an kama su ne da manyan igiyoyin wutar lantarki a kauyen Waro da ke karamar hukumar Karasuwa. A cewar sanarwar, an kama wadanda ake zargin ne a lokacin da suke loda igiyoyin a kan keke-napep mai kafa uku. Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Emmanuel Ado ya jaddada kudirin rundunar na yaki da masu aikata miyagun laifuka da barnata dukiyoyin jama’a, inda ya bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton duk wasu zarge-zarge ko wasu mutane da ke shirin barnata kadarorin jama’a. Ya kuma yabawa ‘yan jihar bisa yadda suke bayar da sahihan bayanai, wanda hakan ya taimaka wajen bunkasa kokarin rundunar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe

Wasu mahara da ake zargin ‘yan Boko Haram ne sun kai hari gidan babban Jami’in kula da ofishin ‘yan sandan na Tattaɓa, ASP Mohammed Modu, da ke yankin Bara a ƙaramar hukumar Gulani, Jihar Yobe.

Kamar yadda rahoton Jami’an tsaro ke nunawa cewa, da misalin ƙarfe 1:30 na tsakar daren ranar 9 ga Disamba, maharan suka mamaye gidaje uku na jami’in, suka sace babur ɗinsa na Haojue da kekuna uku da mota ƙirar Golf 3, da sauran kayansa kafin su ƙona gidaje uku da motar Honda Civic.

Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos

An yi zargin cewa, wani mai kai rahoto ne ga ‘yan ƙungiyar da ke cikin al’ummar wannan yankin ya bada rahoton Jami’in ga waɗannan maharan.

Jami’an tsaro sun ziyarci wurin da lamarin ya faru kuma sun tattara bayanai game da ɓarnar, ba tare da an samu rahoton asarar rayuka ba.

An shawarci jami’in da ya yi taka-tsantsan yayin da ake ƙara tsaurara sa ido da sintiri a yankin don hana sake kai hari a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin da miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara