Rundunar ‘yansandan jihar Yobe ta kama wasu mutane biyu da ake zargin barayin wayar wutar lantarki ne a Damaturu babban birnin jihar. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa, rundunar ‘yansanda ta Karasuwa ce ta kama wadanda ake zargin – Yahaya Mustapha, 28, da Bello Yakubu, 38, da misalin karfe 1:00 na rana a ranar 12 ga watan Afrilun 2025.

‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Haɗa Makamai A Kano Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum Ɗaya A Bauchi, Wasu Sun Jikkata Abdulkarim ya ce, wadanda ake zargin sun fito ne daga unguwar Takari da ke karamar hukumar Gashua Bade a jihar, an kama su ne da manyan igiyoyin wutar lantarki a kauyen Waro da ke karamar hukumar Karasuwa. A cewar sanarwar, an kama wadanda ake zargin ne a lokacin da suke loda igiyoyin a kan keke-napep mai kafa uku. Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Emmanuel Ado ya jaddada kudirin rundunar na yaki da masu aikata miyagun laifuka da barnata dukiyoyin jama’a, inda ya bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton duk wasu zarge-zarge ko wasu mutane da ke shirin barnata kadarorin jama’a. Ya kuma yabawa ‘yan jihar bisa yadda suke bayar da sahihan bayanai, wanda hakan ya taimaka wajen bunkasa kokarin rundunar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana

Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun sakandaren kwana a matsayin wani mataki na kariya ga ɗaliban makarantun.

A cikin wata sanarwa da Mamman Mohammed, kakakin gwamnan, ya ce, wannan shawara ta biyo bayan taron tsaro tsakanin Gwamna Mai Mala Buni da shugabannin tsaro a jihar, inda suka yi nazari kan abubuwan da suka faru na tsaro a makarantu a wasu sassan ƙasar nan.

Sanarwar da Babban Sakatare na ma’aikatar Ilimi na Jihar, Dakta Bukar, ya sanya wa hannu, ta umarci a rufe dukkan makarantun sakandare na kwana nan take har sai an samu ci gaba a lamarin.

Gwamna Buni ya yi kira ga al’ummar jihar da su yi wa shugabanni, jami’an tsaro, addu’ar ci-gaba da samun zaman lafiya da ingantaccen tsaro a Jihar da ma ƙasar baki ɗaya.

An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro NAJERIYA A YAU: Halin Da Shirin Samar Da Tsaro A Makarantun Najeriya Ke Ciki

Daga sai gwamnan ya yi fatan alheri ga ɗaurewar harkokin tsaron Jihar tare da bayar da tabbacin ci gaba da kula da harkokin tsaro da rayukan al’ummar jihar ta kowace fuska kuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar
  • Tuƙin ganganci: KASTELEA  Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
  • An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade
  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara