Aminiya:
2025-10-22@13:52:47 GMT

NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Published: 14th, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yanzu haka al’ummar Borno na cikin zullumi sakamakon wasu hare-haren da ake zargin ƙungiyar Boko Haram ce ta kai a wasu sassan jihar.

Waɗannan hare-hare dai suna faruwa ne bayan shekaru da dama da iƙirarin hwamnati cewa an yi nasarar nakasa ƙungiyar.

Ko mene ne dalilin sake farfaɗowar ƙungiyar ta Boko Haram a wannan lokaci?

NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Wannan ne batun shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16971864-dalilan-farfa-owar-boko-haram-a-jihar-borno.mp3?download=true

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aikin Tsaro Boko Haram jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya karyata zargin kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya, yana mai cewa wannan ikirari ƙarya ne kuma bai kamata a ci gaba da yada shi ba.

Sarkin ya bayyana hakan ne a taron Babban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewa na shekarar 2025, wanda aka gudanar a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, a ranar Talata, da taken: “Ƙarfafa Haɗin Gwiwar Al’umma Domin Samun Zaman Lafiya da Tsaro Mai Dorewa a Arewa.”

Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya

Ya ce: “Sun dade suna cewa ana kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya daga ƙasashen Yamma kamar Amurka, Kanada da sauransu. A ina? Yaushe? Wannan labari ne na ƙarya.”

Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewacin Najeriya ya ce ba zai yiwu a ce ana irin wannan kisa a wani yanki na Najeriya ba, kuma sarakunan gargajiya ba su sani ba.

Ya roƙi shugabannin ƙasa da su sanya dokoki kan amfani da kafafen sada zumunta saboda illar da suke haifarwa da kuma abubuwan batanci da ake wallafawa game da ƙasa da mutane a cikinsu.

Sarkin ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya da su daina zagin sojoji, yana mai jaddada cewa da babu sadaukarwarsu, da ƙasa ba za ta ci gaba da kasancewa ƙasa ɗaya mai zaman lafiya ba.

Sai dai ya amince cewa sojoji na fama da ƙalubale da gazawa, amma ya soki maganganun da ake yi a kafafen sada zumunta da ke zargin jami’an tsaro da haɗin gwiwa da ‘yan ta’adda, yana mai cewa hakan rashin tausayi ne kuma bai dace ba.

Sarkin ya sake jaddada goyon bayan sarakunan gargajiya ga ci gaban dimokuraɗiyya da biyayya ga dukkan shugabannin da aka zaɓa, ciki har da Shugaban Ƙasa, Majalisun Tarayya da na Jihohi, da Gwamnoni.

Ya kuma buƙaci sarakunan da suka halarci taron da su haɗa kai domin fuskantar ƙalubalen da ƙasa ke ciki, yana mai cewa za a mika shawarwarin da suka bayar ga Gwamnonin Arewa domin ɗaukar matakin da ya dace.

Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a taron ya ce sarakunan gargajiya na da muhimmiyar rawa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya ce suna da ƙwarewa wajen rage tashin hankali, warware rikice-rikice, da kawo zaman lafiya a lokacin ƙalubale.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Borno rufe makarantun jihar saboda rigakafin ƙyanda da Polio
  • Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi
  • Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Biliyan Daya Wajen Gyaran Ajujuwa A Makarantu
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni
  • Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Muka Shiga Sakamakon Haihuwar ’Ya Mai Cutar Motsewar Kwakwalwa
  • Kano Pillars ta dakatar da Kocinta
  • Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?