Leadership News Hausa:
2025-12-14@19:27:29 GMT

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Published: 11th, April 2025 GMT

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.

A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.

Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.

Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Giya

এছাড়াও পড়ুন:

An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe

Wasu mahara da ake zargin ‘yan Boko Haram ne sun kai hari gidan babban Jami’in kula da ofishin ‘yan sandan na Tattaɓa, ASP Mohammed Modu, da ke yankin Bara a ƙaramar hukumar Gulani, Jihar Yobe.

Kamar yadda rahoton Jami’an tsaro ke nunawa cewa, da misalin ƙarfe 1:30 na tsakar daren ranar 9 ga Disamba, maharan suka mamaye gidaje uku na jami’in, suka sace babur ɗinsa na Haojue da kekuna uku da mota ƙirar Golf 3, da sauran kayansa kafin su ƙona gidaje uku da motar Honda Civic.

Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos

An yi zargin cewa, wani mai kai rahoto ne ga ‘yan ƙungiyar da ke cikin al’ummar wannan yankin ya bada rahoton Jami’in ga waɗannan maharan.

Jami’an tsaro sun ziyarci wurin da lamarin ya faru kuma sun tattara bayanai game da ɓarnar, ba tare da an samu rahoton asarar rayuka ba.

An shawarci jami’in da ya yi taka-tsantsan yayin da ake ƙara tsaurara sa ido da sintiri a yankin don hana sake kai hari a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
  • Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau
  • Gwamnatin Kano Ta Haramta Sabuwar Hisbah Da Ganduje Ke Shirin Ƙirƙirowa
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai
  • An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe