Leadership News Hausa:
2025-11-21@10:58:10 GMT

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Published: 11th, April 2025 GMT

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.

A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.

Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.

Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Giya

এছাড়াও পড়ুন:

Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP

Shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hashimu Sulaiman Dungurawa, ya ce jam’iyyar APC ba ta da ƙarfin da zai kai ta ga samun nasara a 2027, sai dai idan ta jingina da tasirin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a sakatariyar NNPP ta jihar, Dungurawa ya ce APC a Kano har ma da matakin ƙasa “ta rasa shugabanci da tsari”, wanda hakan, a cewarsa, ya sa suke yawan neman kusanci da Kwankwaso.

Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka

A cewarsa, “Wannan mutanen APC ba su da ƙarfi, kuma a halin yanzu sun shiga ruɗani. Sun san cewa idan babu Kwankwaso, ba za su iya cin zaɓe a 2027 ba.

“Shi ya sa kullum sai ka ji suna cewa wai suna tattaunawa da shi wanda hakan ya nuna su ne buƙatar sa, a yayin shi kuma nasa hankalin ya karkata kan jin daɗin ’yan Najeriya.”

‘Sulhu a siyasa ba sabon abu ba ne’

Sai dai Dungurawa ya bayyana ce tattaunawa da sulhu a siyasa ba sabon abu ba ne, yana mai jaddada cewa haɗuwar Kwankwaso da wasu manyan ‘yan siyasa da ake yi a bayan nan “ba wai wata yarjejeniya ce ta siyasa ba, sai dai haɗuwa ta ba-zata da ba ta haɗi da sha’anin siyasa”.

‘Jama’a ba su waye da NNPP ba a Zaɓen 2023’

Yayin da yake amsa tambayar dalilin da NNPP ta samu kusan ƙuri’u 500,000 kacal a Kano a zaɓen 2023 duk kuwa iƙirarin shaharar Kwankwaso, Dungurawa ya ce ai a lokacin jam’iyyar “dududu ba ta wuce watanni bakwai da kafuwa ba.”

Ya ce, “Ko a 2023 tambarin jam’iyyar [NNPP] bai fito ba sosai a takardar zaɓen ba, sannan kuma mutane da dama ba su waye da jam’iyyar ba kasancewarta sabuwa ce a lokacin.

“Amma duk da haka mun samu kujeru a Kano, Jigawa, Taraba da Bauchi. Don haka zaɓen 2027 zai bambanta kwarai da abin da kuka gani.”

Game da shirye-shiryen tarukan jam’iyya masu zuwa, Dungurawa ya ce tsarin jam’iyyar ya bayyana cewa yawancin shugabannin jam’iyyar na yanzu za su ci gaba da riƙe muƙamansu.

Ya ce, “Dokokin jam’iyyar sun yarda shugabanni su yi wa’adi biyu muddin ba su fice daga jam’iyya ba, ko suka mutu ko kuma aka same su da laifi.”

Ya kuma bayyana cewa za a gudanar da zaɓen cike gurbi a watan gobe domin maye gurbin kansiloli uku da suka rasu a kananan hukumomin Garin Malam, Dala da Doguwa.

Ya yabi Gwamna Abba kan kasafin kuɗin Kano na 2026

Shugaban na NNPP ya kuma yaba wa ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2026 da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gabatar, yana mai cewa fifikon da aka ba bangaren ilimi da noma “abin yabawa ne”, tare da jinjina wa gwamnati kan “gyare-gyaren da ake gani da ido” a faɗin Jihar Kano.

Ya kuma soki tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje, yana zarginsa da “barin ilimi a baya, rashin tallafin karatu, da ƙin biyan haƙƙoƙin fansho.”

‘Ba mu damu da masu ficewa daga jam’iyyar ba’

Dangane da batun sauyin sheƙa, Dungurawa ya ce ɗan majalisar tarayya ɗaya kacal ne ya fice daga cikin jami’yyar da kansa, sauran kuwa an dakatar da su ne tun kafin su fice.

Ya ce, “Ba damuwar mu ba ce. Jam’iyyar ba ta buƙatar mutane masu wuyar sha’ani. NNPP kamar ɗakin otel ne — akwai masu barin ɗaki na alfarma ‘royal suite’ su koma na gama-gari wato ‘standard room’, daga baya sai su gane banbancin.”

Dungurawa ya buƙaci jama’ar NNPP su ci gaba da zama tsintsiya maɗauri ɗaya, su kuma fara shiri domin NNPP ta ci gaba da cin gajiyar mulki a 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP
  • Kotu Ta Yanke Wa Nnamdi Kanu Hukuncin Zaman Kurkuku Na Har Abada  Akan Laifin Ta’addanci
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki
  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
  • Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a Najeriya
  • United za ta yi wasanni 6 a jere babu Benjamin Sesko
  • Mutane 7 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa