Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe
Published: 11th, April 2025 GMT
Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.
A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.
Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.
Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Giya
এছাড়াও পড়ুন:
An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
Gwamnatin Jihar Gombe ta dakatar da wani Hakimi da Dagaci a ƙaramar hukumar Funakaye bayan barkewar rikici tsakanin manoma da makiyaya a yankin.
Rahotanni sun ce rikicin dai ya yi sanadin mutuwar ɗan sanda ɗaya tare da jikkatar wasu jami’an tsaro da dama.
Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin kashi 15 na shigo da fetur da dizal Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar KanoKwamishinan Shari’a na jihar, Barista Zubairu Muhammad, ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai bayan zaman kwamitin tsaro da aka gudanar ranar Laraba.
Ya ce an dauki matakin dakatarwar ne domin tabbatar da doka da oda, tare da aika sakon gargaɗi ga sauran masu rike da sarautun gargajiya cewa ba za a lamunci sakaci wajen dakile rikice-rikice ba.
“Majalisar ta yi nazari mai zurfi kan lamarin kuma ta nuna damuwa. Gwamnati ba za ta lamunci kai hari ga jami’an tsaro ko hana su gudanar da ayyukansu bisa doka ba. Duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci mai tsanani,” in ji shi.
Barista Muhammad ya tabbatar da cewa an kama wasu da ake zargi da hannu a harin da aka kai wa jami’an tsaron, kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya.
Kwamishinan ya ce kodayake ɗaya daga cikin shugabannin da aka dakatar ya rasa ɗansa a cikin lamarin, hakan bai hana gwamnati ɗaukar mataki ba saboda gazawarsa wajen hana rikicin ya ƙara kamari.
“Rahotanni game da halayen mamacin sun tayar da hankali. Da mahaifinsa, wanda shi ne shugaba a yankin, da ya ɗauki mataki tun da wuri, da ba a kai ga tashin hankali ba. Jagoranci na nufin jarumta da adalci,” in ji shi.
Kwamishinan ya sake jaddada goyon bayan gwamnati ga jami’an tsaro, inda ya yaba da jajircewarsu wajen tabbatar da zaman lafiya wanda ya sa jihar ta kasance ɗaya daga cikin jihohin da suka fi kwanciyar hankali a ƙasar.
“Gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro don su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa. Duk wani yunƙurin tsoratar da su ko hana su aiki ba za a lamunce shi ba,” in ji shi.
Barista Muhammad ya kuma ambaci rahoton kwamiti ƙarƙashin tsohon Mataimakin Sufeton ’yan sanda na kasa, AIG Zubairu Muazu (mai ritaya), wanda ya binciki tushen rikicin na manoma da makiyaya a jihar.
Kwamishinan ya ce kwamitin ya gano toshe burtalolin kiwo na asali ta hanyar gonaki da gine-gine a matsayin babban abin da ke haddasa rikice-rikicen da ake ta fama da su.
Gwamnatin jihar ta kuma jaddada aniyarta ta kare zaman lafiya tare da yin gargaɗin cewa babu wanda za a rufa wa asiri idan aka same shi da laifin kawo barazana ga tsaro ko hana shari’a gudanar da aikinta yadda ya kamata.