Leadership News Hausa:
2025-12-10@12:31:49 GMT

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Published: 11th, April 2025 GMT

Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe

Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.

A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.

Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.

Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Giya

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa

Muhsin Umar Chiroma wanda aka fi sani suna SKD Arewa, xaya ne daga cikin matasan mawaqan zamani da ludayinsu ke kan dawo wajen tashe, musamman a shafukan sada zaumunta. A hirarsa da Aminiya, saurayin mawaqin ya bayyana abin da ya xauki hankalinsa har ya yi wata waqa da ya yi wa laqabi da suna ‘Arewa’.

Muhsin wanda ya fi qwarewa a fagen waqoqin ‘Gambara’, da aka fi sani da Hip Hop, bayyana wa Aminiya cewa, halin da Arewacin Nijeriya ya shiga na rashin tsaro shi ne jigon waqarsa.

A cikin waqar haziqin mawaqin, ya yi tsokaci a kan yadda shugabanni a Arewa suka yi biris da halin da talakawa suka tsinci kansu a ciki na barazanar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro. Inda yake qoqarin ganin ya jawo hankalin masu muli da ma talakawa don su farka daga barci.

Matashi mawaqin ya ce, “waqata mai taken ‘Arewa’, waqa ce da zan ce na yi ta ne saboda in tayar da shugabanni da kuma talakawan Arewacin Nijeriya daga barci. Domin kuwa ga gobara nan ta tunkaro mu daga kogi amma kuma da alamu babu wanda ya damu da ita.”

Da yake amsa tambayar ko me ya sa ya zavi yin amfani da waqa don wayar da kan jama’a kan muhimmancin haxin kai don tunkarar wannan matsala? Mawaqin zamanin sai ya ce, “ka san kowa da dutsen da ke hannunsa zai yi jifa. Don haka tunda yake ina da fasahar waqa, shi ya sa na ga wannan ita ce, kawai hanya xaya tilo da tafi sauqi wajena in isar da wannan muhimmin saqo.”

Matashin ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu akwai fitattun mawaqan da suka yi waqoqi kan abin da ya shafi tavarvarewar tsaro a qasa. Amma duk da haka, ya dace manya fitattun mawaqa na zamani da duniya ta san su, su qara qaimi wajen wayar da kan matasa don su guji shiga ayyukan laifi da ke jefa qasa cikin rashin tabbas.

SKD Arewa, ya kuma shawarci matasan mawaqa da su rungumi karatu, domin a cewarsa, ilimi ne zai taimaka musu wajen inganta sana’o’insu kuma ya basu damar amfani da shafukan sada zumunta wajen tallata fasahohinsu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166