Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe
Published: 11th, April 2025 GMT
Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.
A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.
Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.
Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Giya
এছাড়াও পড়ুন:
An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
Gwamnatin Jihar Bauchi ta ba da umarnin rufe dukkan makarantun firamare, sakandare, da manyan makarantu—ciki har da Gwamnatin Tarayya da makarantu masu zaman kansu saboda matsalolin rashin tsaro da ke faruwa a faɗin ƙasar kan.
Sanarwa da Jalaludeen Usman Jami’in Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi, ya fitar ta ce, “Wannan shawara, duk da cewa tana da wahala, Gwamnatin Jihar Bauchi ta yanke ta ne bayan tattaunawa mai zurfi da kuma la’akari da matsalolin tsaro da suka shafi tsaron ɗalibai, malamai, da al’ummomin makarantu a faɗin jihar.”
“Gwamnati ta san abin da wannan matsala ka iya haifarwa. Duk da haka, kare ’ya’yanmu ya kasance babban nauyin da ke kanmu. Muna sane da cewa lowane ɗalibi a Jihar Bauchi ya cancanci ya yi karatu a cikin yanayi mai aminci, kwanciyar hankali, kuma ba tare da tsoro ba.
“Saboda haka muna kira ga iyaye, masu kula, masu mallakar makarantu, da duk masu ruwa da tsaki da abin ya shafa da kada su firgita, amma su kwantar da hankalinsu su kuma ba da haɗin kai.”
“Gwamnati tana aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro don magance matsalolin cikin sauri da kuma cikakkiyar fahimta, tare da tabbatar da cewa ayyukan ilimi na yau da kullum, za su ci gaba da gudana da zarar an tabbatar da hakan.
“Muna kuma kira ga jama’a da su ci gaba da taka tsantsan. Idan kun ga wani abu da ba ku gane ba ku bayar da bayani wa jami’an tsaro saboda bayar da bayanai da a kan lokaci suna da mahimmanci wajen kare al’ummominmu.
“Gwamnatin Jihar Bauchi za ta ci gaba da samar da sabbin bayanai yayin da lamarin ke ci gaba.”