Asusun ba da lamuni na ilimi na Najeriya ya yi barazanar daukar matakin shari’a a kan cibiyoyin da ke boye bayanai kan yadda ake biyan dalibai rancen kudi yayin da suke neman biyan kudaden makarantun daga hannun daliban.

 

Sanarwar da Manajin Darakta na NELFUND, Mista Akintunde Sawyerr ya fitar ta bayyana cewa, sakamakon binciken da aka gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa wasu cibiyoyi bayan karbar lamunin dalibai kai tsaye a cikin asusunsu, sun kasa sanar da daliban da abin ya shafa ko kuma nuna kudaden da aka biya a cikin takardun kudin makarantarsu, wanda hakan ya haifar da rudani da bai kamata ba.

 

Mista Sawyerr wanda ya bayyana lamarin a matsayin rashin da’a, ya kuma gargade su da su daina ko kuma su fuskanci fushin doka.

 

“Wannan matakin na hana mahimman bayanan kuɗi daga ɗalibai ba rashin da’a ba ne kawai amma cin zarafi ne kai tsaye ga ƙa’idodin da aka kafa NELFUND a kai. “Ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin shari’a kan duk wata cibiya da aka samu da aikata irin wadannan ayyukan yaudara.”

 

 

Ya shawarci dukkanin cibiyoyi da su tabbatar da gaskiya tare da yin aiki tare da Asusun don tabbatar da isar da ayyukan sa yadda ya kamata.

 

Mista Sawyerr ya jaddada cewa manufar NELFUND ita ce fadada hanyoyin samun ilimi mai zurfi ta hanyar sauke nauyin kudi a kan daliban Najeriya da iyalansu, daidai da hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Asusun yana tabbatar wa ɗalibai da jama’a jajircewar sa na yin riko da gaskiya, yin adalci, da samun nasarar aiwatar da shirin rancen ɗalibai a faɗin ƙasar.

 

HAKURI OLUMATI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza

Masu bincike sun gano cewa sojojin HKI sun kashe Falasdinawa akalla 100,000 tun bayan fara yakin tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara 2023.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kan cewa farfesa Michael Spagat da kuma Khalil Shikaki  Bafalasdine masanin masanin fasahar siyasa a Jami’ar London na kasar Burtania suka jagoranci bincike wanda ya kai ga fitar da wannan sakamakon.

Labarin ya kara da cewa masu binciken sun kiyasta mutane a gidaje 2000 a birnin  Gaza kadai wanda falasdinawa kimani 10,000 suke rayuwa, sannan suka yi lissafi suka kaim ga wannan sakamakon.

Bincike ya kara da cewa daga watan jenerun shekara ta 2025 falasdinawa 75,200 sojojin yahudawan suka kashe da makamai, sannan wasu kimani 8,540 sun mutu sabada yunwa da karancin magunguna da kuma wasu hanyoyi ba da wuta ba.

Amma ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta bayyana cewa daga watan Jeneru zuwa yanzu sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 10,000.

Ma’aikatar ta kara da cewa a baya bayan nan sojojin yahudawa suna kashe Falasdinawa a wuraren karban abinci da suka shirya a matsayin tarko ga Falasdinawa wadanda suke fama daga tsananin yunwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 
  • Dalibai 29 Suka Rasu A Turmutsitsin Tserewa Ga Fashewar Taransifoma A Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  •  Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
  • Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
  • Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100