Asusun ba da lamuni na ilimi na Najeriya ya yi barazanar daukar matakin shari’a a kan cibiyoyin da ke boye bayanai kan yadda ake biyan dalibai rancen kudi yayin da suke neman biyan kudaden makarantun daga hannun daliban.

 

Sanarwar da Manajin Darakta na NELFUND, Mista Akintunde Sawyerr ya fitar ta bayyana cewa, sakamakon binciken da aka gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa wasu cibiyoyi bayan karbar lamunin dalibai kai tsaye a cikin asusunsu, sun kasa sanar da daliban da abin ya shafa ko kuma nuna kudaden da aka biya a cikin takardun kudin makarantarsu, wanda hakan ya haifar da rudani da bai kamata ba.

 

Mista Sawyerr wanda ya bayyana lamarin a matsayin rashin da’a, ya kuma gargade su da su daina ko kuma su fuskanci fushin doka.

 

“Wannan matakin na hana mahimman bayanan kuɗi daga ɗalibai ba rashin da’a ba ne kawai amma cin zarafi ne kai tsaye ga ƙa’idodin da aka kafa NELFUND a kai. “Ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin shari’a kan duk wata cibiya da aka samu da aikata irin wadannan ayyukan yaudara.”

 

 

Ya shawarci dukkanin cibiyoyi da su tabbatar da gaskiya tare da yin aiki tare da Asusun don tabbatar da isar da ayyukan sa yadda ya kamata.

 

Mista Sawyerr ya jaddada cewa manufar NELFUND ita ce fadada hanyoyin samun ilimi mai zurfi ta hanyar sauke nauyin kudi a kan daliban Najeriya da iyalansu, daidai da hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Asusun yana tabbatar wa ɗalibai da jama’a jajircewar sa na yin riko da gaskiya, yin adalci, da samun nasarar aiwatar da shirin rancen ɗalibai a faɗin ƙasar.

 

HAKURI OLUMATI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

Bisa labarin da babban bankin jama’ar kasar Sin ya fitar, ya zuwa ranar 15 ga watan Afrilun shekarar 2025, jimillar cibiyoyin hada-hadar kudi na kasashen waje 1,160 ne suka shiga kasuwar hada-hadar lamuni ta kasar Sin, wadanda suka hada da cibiyoyin hada-hadar kudi masu zaman kansu da cibiyoyin hada-hadar kudi na kasuwanci a kasashe da yankuna fiye da 70, wadanda ke rike da takardun lamuni da yawansu ya kai yuan tiriliyan 4.5, adadin da ya karu da sama da yuan biliyan 270 daga karshen shekarar 2024. Kazalika, jimillar darajar kasuwar lamuni ta kasar Sin ta kai yuan tiriliyan 183, wanda ke matsayi na biyu a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin
  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Tsohon Minista Ya Zargi Isra’ila Da Kasashen Yammacin Turai Da Kitsa Kashe-kashen Rayuka A Nijeriya 
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato