Leadership News Hausa:
2025-12-13@22:59:06 GMT

Salah Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniyar Shekaru 2 Da Liverpool

Published: 11th, April 2025 GMT

Salah Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniyar Shekaru 2 Da Liverpool

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta fara ɗaukar likitoci da sauran ma’aikatan lafiya domin aikin Hajji da ke tafe a ƙasar Saudiyya.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa shafin neman aikin ya fara aiki daga ƙarfe 11 na dare ranar Juma’a 12 ga Nuwamba, 2025. Za a rufe shafin da ƙarfe 11.59 ranar Litinin, 15 ga watan Disamba, 2025

Latsa nan domin shiga shafin ɗaukar ma’aikatan lafiyan kai-tsaye.

NAHCON ta bayyana cewa jami’an lafiyan da za a ɗauka Su ƙunshi likitoci, masu haɗa magunguna, malaman jinya, da jami’an kula da lafiyar lafiya da ta muhalli (CHO/EHO). Su ne za su yi aikin kula da lafiyar alhazai a yayin aikin Hajjin na shekarar 2026.

NAHCON ta bayyana cewa jami’an da suka yi aiki da ita a matsayin kula da lafiyar alhazai a  shekaru uku da suka gabata (2023 zuwa 2025) ba ne kaɗai za a ɗauka domin wannan aiki na 2026.

Yadda za ku nemi aikin

Masu nema za su shiga shafinta kai-tsaye domin ganin ka’idodin da kuma cike bayanansu. Latsa nan domin lafiyan kai-tsaye.

Ko kuma su gaida babban shafinta daga nan su latsa wasu layuka huɗu da ke hannun dama daga sama.

Daga daga nan su latsa RESOURCES, sai su latsa su shiga NMT Application Portal.

A ciki za su ga ka’idodin neman aikin, su cike bayansu, da kuma sauke duk dakardun da su cike.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa daga bisani za a tuntuɓi duk waɗanda suka yi nasara.

Allah Ya ba da sa’a.

Ka’idodin neman aikin

NAHCON ta jaddada cewa:

– Ma’aikatan lafiya da suka cancanta ne kawai za su iya nema aikin ba Tawagar Lafiya ta Ƙasa (NMT) domin aikin Hajjin 2026

– Aikin NMT na 2026 zai gudana ne bisa tsarin sa-kai, bisa ƙa’idojin duniya da NAHCON ta amince da su.

– Bayanai da aka bayar za su taimaka wajen tantance cancanta da shirin shiga matakin gaba na tantancewa ko jarabawa.

– Duk bayanan da aka gabatar za a duba su. Duk wani kuskure. Ɓoye gaskiya, ko ƙirƙirar bayanan ƙarya zai iya jawo ƙin amincewa da aikace-aikacen ko cirewa daga jerin waɗanda cancanta.

– Wannan aikace-aikacen kyauta ne gaba ɗaya. NAHCON ba ta karɓar kuɗi kai tsaye ko a kaikaice, ko ta hannun wakilai ko hukumomi. Ku yi hattara!

– Cika fom ɗin ba ya nufin an amince da cancanta ko zaɓen ku.

 

Ƙa’idar shekaru:

– Likitoci: 27 zuwa 60 shekara

– Masu haɗa Magunguna: shekara 26 zuwa 60

– Nas da sauran rukuni: 22–60 shekara .

Sharuɗɗa

Dole masu neman shiga NMT su kasance:

1. Suna aiki a lokacin neman shiga.

2. Ba su halarci ayyukan NMT a shekara uku da suka gabata ba (2023, 2024, da 2025).

3. Su kasance a shirye su yi aiki na tsawon kwanaki 28 da kuma zama a Saudiyya har zuwa kwanaki 45 kafin dawowa Najeriya.

4. Ba za a sallame su a wurin aikinsu ba kafin su kammala aikin NMT.

5. Su nuna kyawawan halaye tare da bin ƙa’idojin aikin lafiya da na NAHCON.

6. Su gabatar da tabbacin mai tsaya musu (guarantor).

 

Sharuɗɗan Guarantor:

– Dole ya kasance mutum mai daraja: Ma’aikacin gwamnati (ba ƙasa da GL 15), basaraken gargajiya, Alƙali (Magistrate), ko Shugaban Ƙaramar Hukuma.

– Dole ya san mai neman aikin NMT tsawon aƙalla shekaru biyar kuma ya tabbatar da gaskiya, ƙwarewa, da iya aikinsa.

– Dole ya gabatar da kwafin katin shaida ko wata takardar shaida da ake amfani da ita a ofisoshin gwamnati na Najeriya.

 

Takardun da dole a haɗa da su:

– Fom ɗin Guarantor da aka cika

– Takardar shaidar ƙwarewar aiki (Basic Professional Certificate)

– Takardar NYSC (idan ta shafi mai nema)

– Lasisin aikin lafiya na wannan shekara

– Hoton fasfo (mai farin baya)

– Sanarwar mai nema (applicant’s declaration)

– Takardar izini daga wurin aiki (employer’s clearance letter) .

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Haramta Sabuwar Hisbah Da Ganduje Ke Shirin Ƙirƙirowa
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon  A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Osimhen Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Bana A Kasar Turkiyya
  • Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos