Sojojin HKI Sun Yi Kisan Kiyashi A Yankin Shuja’iyya
Published: 11th, April 2025 GMT
Sojojin HKI suna ci gaba da yin kiyashi a sassa mabanbata na Gaza, da a bayan nan su ka yi wa mutane 30 kisan kiyashi a unguwar Shuja’iyya dake birnin Gaza.
Majiyar asibitin Falasdinawa ta ambaci cewa; Harin da sojojin HKI su ka kai da manyan bindigogi sun yi sanadiyyar shahadar mutane 17 a unguwar ta Shuja’iyya.
Wasu majiyoyin Falasdinawa sun ambaci cewa: Sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren da manyan bindigogi a kusa da masallacin; UMMU HaBIBAH, da kuma kasuwar sayar da kekune a yankin Qaizan a kudancin Khan-Yunus.
A gefe daya,majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa; Da akwai Falasdinawa miliyan daya da aka kora daga gidajensu da karfi.
Kungiyoyin fararen hula sun ambaci cewa; A kalla da akwai mutane miliyan daya da aka tilastawa ficewa daga gidajensu zuwa wasu yankuna. Kungiyoyin suna kokarin kafa sansanonin tsugunar da wadanda aka tilastawa yin hijirar.
Wata matsalar da ake fuskanta a Gaza ita ce yadda ‘yan sahayoniyar su ka hana yi wa kananan yaran yankin allurar riga-kafin shan inna, lamarin da yake yin barazana sake dawowar cutar bayan kawar da ita.
Bayanin ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ya ambaci cewa tun daga 2023 zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 50,886, yayin da wadanda su ka jikkata adadinsu ya kai 115,875.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ambaci cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume
Sanata Ali Ndume ya ce jahiltar halin da Najeriya ke ciki ne ya sa Shugaban Amurka Donald Trump ya yi iƙirarin cewa ana kisan Kiristoci a ƙasar.
Ndume, wanda ke wakiltar mazabar Borno ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise ranar Talata.
Ousmane Dembele zai buga wasan PSG da Bayern Munich ’Yan kwangila sun hana zaman majalisa kan rashin biyan haƙƙoƙinsuSanatan ya ce maganganun Trump sun nuna rashin cikakken fahimtar yadda matsalar tsaro take da sarƙaƙiya a Najeriya.
Ya ce matsalar rashin tsaro a ƙasar ta shafi al’umma baki ɗaya ba tare da la’akari bambancin addini ba, yana mai cewa “mutane daban-daban ne ke fuskantar hare-hare daga ‘yan ta’adda, ba Kiristoci kaɗai ba.”
Sanatan ya ƙara da cewa kamata ya yi shugabannin ƙasashen waje su riƙa neman cikakken bayani kafin su yi maganganu da ka iya tada hankali, musamman kan lamurran da suka shafi addini da tsaro.
“Trump bai fahimci haƙiƙanin abin da ke faruwa a Najeriya ba. Matsalar nan ta wuce batun addini, domin dukkan al’ummomi na cikin halin tsoro da fargaba saboda ayyukan ‘yan ta’adda,” in ji Ndume.