HausaTv:
2025-09-17@23:07:22 GMT

 Sojojin HKI Sun Yi Kisan Kiyashi A Yankin Shuja’iyya

Published: 11th, April 2025 GMT

Sojojin HKI suna ci gaba da yin kiyashi a sassa mabanbata na Gaza, da a bayan nan su ka yi wa mutane 30 kisan kiyashi a unguwar Shuja’iyya dake birnin Gaza.

 Majiyar asibitin Falasdinawa ta ambaci cewa; Harin da sojojin HKI su ka kai da manyan bindigogi sun yi sanadiyyar shahadar mutane 17 a unguwar ta Shuja’iyya.

Dama tun da safiyar Laraba wasu Falasdinawan 50 sun yi shahada a wannan unguwa ta Shuja’iyya dake cikin birnin Gaza.

Wasu majiyoyin Falasdinawa sun ambaci cewa: Sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren da manyan bindigogi a kusa da masallacin; UMMU HaBIBAH, da kuma kasuwar sayar da kekune a yankin Qaizan a kudancin Khan-Yunus.

A gefe daya,majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa; Da akwai Falasdinawa miliyan daya da aka kora daga gidajensu da karfi.

Kungiyoyin fararen hula sun ambaci cewa; A kalla da akwai mutane miliyan daya da aka tilastawa ficewa daga gidajensu zuwa wasu yankuna. Kungiyoyin suna kokarin kafa sansanonin tsugunar da wadanda aka tilastawa yin hijirar.

Wata matsalar da ake fuskanta a Gaza ita ce yadda ‘yan sahayoniyar su ka hana yi wa kananan yaran yankin allurar riga-kafin shan inna, lamarin da yake yin barazana sake dawowar cutar bayan kawar da ita.

Bayanin ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ya ambaci cewa tun daga 2023 zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 50,886, yayin da wadanda su ka jikkata adadinsu ya kai 115,875.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ambaci cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa