Sojojin HKI Sun Yi Kisan Kiyashi A Yankin Shuja’iyya
Published: 11th, April 2025 GMT
Sojojin HKI suna ci gaba da yin kiyashi a sassa mabanbata na Gaza, da a bayan nan su ka yi wa mutane 30 kisan kiyashi a unguwar Shuja’iyya dake birnin Gaza.
Majiyar asibitin Falasdinawa ta ambaci cewa; Harin da sojojin HKI su ka kai da manyan bindigogi sun yi sanadiyyar shahadar mutane 17 a unguwar ta Shuja’iyya.
Wasu majiyoyin Falasdinawa sun ambaci cewa: Sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren da manyan bindigogi a kusa da masallacin; UMMU HaBIBAH, da kuma kasuwar sayar da kekune a yankin Qaizan a kudancin Khan-Yunus.
A gefe daya,majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa; Da akwai Falasdinawa miliyan daya da aka kora daga gidajensu da karfi.
Kungiyoyin fararen hula sun ambaci cewa; A kalla da akwai mutane miliyan daya da aka tilastawa ficewa daga gidajensu zuwa wasu yankuna. Kungiyoyin suna kokarin kafa sansanonin tsugunar da wadanda aka tilastawa yin hijirar.
Wata matsalar da ake fuskanta a Gaza ita ce yadda ‘yan sahayoniyar su ka hana yi wa kananan yaran yankin allurar riga-kafin shan inna, lamarin da yake yin barazana sake dawowar cutar bayan kawar da ita.
Bayanin ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ya ambaci cewa tun daga 2023 zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 50,886, yayin da wadanda su ka jikkata adadinsu ya kai 115,875.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ambaci cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
Rundunar Ƴansandan Nijeriya, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, ta samu nasarar cafke mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ceto mutane 11 da aka sace a jihohin Delta da Katsina. Wannan na cikin ƙoƙarin ci gaba da yaƙi da miyagun laifuka a faɗin ƙasa.
A jihar Katsina, an daƙile wani yunƙurin garkuwa da mutane a ranar 8 ga Yuni, 2025, a hanyar Danmusa zuwa Mara Dangeza, inda jami’an haɗin gwuiwa suka yi artabu da ‘yan bindiga. Bayan musayar wuta mai tsanani, jami’an suka tilasta masu laifin guduwa da raunukan harbi tare da kuɓutar da mutum 11 da suka sace ba tare da raunuka ba.
Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye AikinsaA jihar Delta, jami’an CP-Special Assignment sun cafke wani Abubakar Hassan, wanda ake zargin jagoran gungun masu garkuwa da mutane ne da ke aiki a jihohi da dama. Bayan gudanar da bincike, ya jagoranci jami’ai zuwa maboyarsu a dajin Ozoro, inda aka ƙwato bindigogi AK-47 guda biyu da harsasai. Hakanan, wani direba, Obi Ezekiel, ya shiga hannu yayin da aka gano bindiga ƙirar gida da alburusai a motarsa.
Babban Sufeton Ƴansanda na ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya yaba da ƙwarewa da kwazon jami’an tsaro a waɗannan ayyuka, tare da jan hankali cewa rundunar zata ci gaba da gudanar da irin wadannan farmaki don tabbatar da cewa babu mafaka ga masu aikata laifi a duk faɗin Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp