Sojojin HKI Sun Yi Kisan Kiyashi A Yankin Shuja’iyya
Published: 11th, April 2025 GMT
Sojojin HKI suna ci gaba da yin kiyashi a sassa mabanbata na Gaza, da a bayan nan su ka yi wa mutane 30 kisan kiyashi a unguwar Shuja’iyya dake birnin Gaza.
Majiyar asibitin Falasdinawa ta ambaci cewa; Harin da sojojin HKI su ka kai da manyan bindigogi sun yi sanadiyyar shahadar mutane 17 a unguwar ta Shuja’iyya.
Wasu majiyoyin Falasdinawa sun ambaci cewa: Sojojin mamayar sun kai wasu hare-haren da manyan bindigogi a kusa da masallacin; UMMU HaBIBAH, da kuma kasuwar sayar da kekune a yankin Qaizan a kudancin Khan-Yunus.
A gefe daya,majiyar Falasdinawa ta ambaci cewa; Da akwai Falasdinawa miliyan daya da aka kora daga gidajensu da karfi.
Kungiyoyin fararen hula sun ambaci cewa; A kalla da akwai mutane miliyan daya da aka tilastawa ficewa daga gidajensu zuwa wasu yankuna. Kungiyoyin suna kokarin kafa sansanonin tsugunar da wadanda aka tilastawa yin hijirar.
Wata matsalar da ake fuskanta a Gaza ita ce yadda ‘yan sahayoniyar su ka hana yi wa kananan yaran yankin allurar riga-kafin shan inna, lamarin da yake yin barazana sake dawowar cutar bayan kawar da ita.
Bayanin ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ya ambaci cewa tun daga 2023 zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 50,886, yayin da wadanda su ka jikkata adadinsu ya kai 115,875.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ambaci cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
Daga Ali Muhammad Rabi’u
An samu mummunan rikici tsakanin mambobin ƙungiyoyin asiri wanda ya shafi tsofaffin daliban kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kwara da ke Ilorin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum ɗaya.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa dalibin mai suna Oyelade Olawale wanda ya karanci aikin Injiniya a fannin Gine-gine, ya rasu ne a yayin wannan rikici na kungiyoyin asiri.
An samu labarin cewa an kama wasu daga cikin wadanda ake zargi da hannu a tarzomar da ta faru a Kwalejin.
A cikin wata sanarwa, Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta Kwalejin, Halima Garba, ta tabbatar da mutuwar matashin da kuma kama wasu mutane da ake zargi da hannu a rikicin.
Sanarwar ta yi kira ga dalibai da al’umma su rika kai rahoton duk wani abin da suke zargin zai iya haddasa fitina ga hukumomin da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a makarantar.