Aminiya:
2025-12-12@17:46:51 GMT

Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC

Published: 10th, April 2025 GMT

Ƙungiyar Ƙwadago a Jihar Sakkwato (NLC), ta musanta iƙirarin da shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta ƙasa (NULGE), Ali Kankara, ya yi cewa gwamnatin jihar ba ta fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 ba.

Shugaban NLC na jihar, Kwamared Aliyu Abdullahi, ya bayyana wa manema labarai a ranar Laraba cewa Gwamnatin Sakkwato ta fara biyan sabon albashin tun a watan Janairu ga dukkanin ma’aikatan jihar, ciki har da na ƙananan hukumomi.

Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi

Ya ce: “Sakkwato ce jiha ta farko da ta fara biyan sabon albashi na dubu 70, kuma ma’aikatan gwamnati da na ƙananan hukumomi na amfana da shi.

“Maganar shugaban NULGE na ƙasa ba gaskiya ba ce.”

Ya ƙara da cewa bai kamata shugaban NULGE ya faɗi irin wannan magana ba tare da ya bincika gaskiyar al’amari ba.

Kwamared Aliyu, ya yaba wa Gwamna Ahmad Aliyu bisa ƙoƙarinsa na biyan ma’aikata haƙƙoƙinsu da kuma dawo da kuɗin tafiyar da ofisoshi, biyan bashin fansho da sauran haƙƙoƙin ma’aikata.

Sai dai wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa ba dukkanin ma’aikatan ƙananan hukumomin jihar ne ke karɓar albashin dubu 70 ba.

Wani ma’aikaci ya ce: “Wasu daga cikinmu da muke karɓar dubu 18 a da, yanzu muna karɓar dubu 30, yayin da waɗanda ke karbar dubu takwas a baya, yanzu gwamnati na biyansu dubu 20.”

Wannan ya nuna cewa duk da gwamnati na ƙoƙarin biyan sabon albashi, har yanzu ba a kai ga kowa ya samu dubu 70 ba a matakin ƙananan hukumomi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mafi karancin albashi Sakkwato biyan sabon

এছাড়াও পড়ুন:

Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ƙaryata zargin cewa Gwamna Bala Mohammed na shirin ficewa daga PDP zuwa jami’yyar PRP.

Jita-jitar ta samo asali ne bayan Sakataren jam’iyyar PRP na Bauchi, Hon. Wada Abdullahi, ya ce ba za su karɓi gwamnan zuwa jami’yyarsu ba.

Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky

Ya ce gwamnan bai cika ƙa’idojin da PRP ke buƙata ba a shugabancinsa a Bauchi.

Amma mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Gidado, ya ce gwamnan bai taɓa tunanin barin PDP ba.

Ya ce babu wata tattaunawa ko mataki da aka ɗauka na komawa PRP.

Gidado, ya ce gwamnan na aiki ne wajen ƙarfafa PDP kuma ya taɓa doke PRP a zaɓuka da suka gabata.

Ya ƙara da cewa Jihar Bauchi ta samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnan, musamman a ɓangaren tallafa wa jama’a, ababen more rayuwa, ci gaban ƙauyuka, da yawon buɗe ido.

Gwamnatin ta soki PRP kan yaɗa jita-jita marasa tushe.

Ya ce gwamnan na da ’yancin zaɓar makomarsa a harkokin siyasa, amma duk wata shawara da zai ɗauka ba za ta kasance bisa ƙarya ko jita-jita ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Australia ta Fara Aiwhatar da Dokar Hana Yara Amfani da Shafukan Sada Zumunta