Aminiya:
2025-12-08@12:41:42 GMT

Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC

Published: 10th, April 2025 GMT

Ƙungiyar Ƙwadago a Jihar Sakkwato (NLC), ta musanta iƙirarin da shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta ƙasa (NULGE), Ali Kankara, ya yi cewa gwamnatin jihar ba ta fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 ba.

Shugaban NLC na jihar, Kwamared Aliyu Abdullahi, ya bayyana wa manema labarai a ranar Laraba cewa Gwamnatin Sakkwato ta fara biyan sabon albashin tun a watan Janairu ga dukkanin ma’aikatan jihar, ciki har da na ƙananan hukumomi.

Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi

Ya ce: “Sakkwato ce jiha ta farko da ta fara biyan sabon albashi na dubu 70, kuma ma’aikatan gwamnati da na ƙananan hukumomi na amfana da shi.

“Maganar shugaban NULGE na ƙasa ba gaskiya ba ce.”

Ya ƙara da cewa bai kamata shugaban NULGE ya faɗi irin wannan magana ba tare da ya bincika gaskiyar al’amari ba.

Kwamared Aliyu, ya yaba wa Gwamna Ahmad Aliyu bisa ƙoƙarinsa na biyan ma’aikata haƙƙoƙinsu da kuma dawo da kuɗin tafiyar da ofisoshi, biyan bashin fansho da sauran haƙƙoƙin ma’aikata.

Sai dai wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa ba dukkanin ma’aikatan ƙananan hukumomin jihar ne ke karɓar albashin dubu 70 ba.

Wani ma’aikaci ya ce: “Wasu daga cikinmu da muke karɓar dubu 18 a da, yanzu muna karɓar dubu 30, yayin da waɗanda ke karbar dubu takwas a baya, yanzu gwamnati na biyansu dubu 20.”

Wannan ya nuna cewa duk da gwamnati na ƙoƙarin biyan sabon albashi, har yanzu ba a kai ga kowa ya samu dubu 70 ba a matakin ƙananan hukumomi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mafi karancin albashi Sakkwato biyan sabon

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161

Daga Usman Muhammad Zaria

Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jihar Jigawa ta yi kiyasin kashe kudade miliyan dubu 161 da milyan 336 domin gudanar da ayyukan hanyoyin mota da harkokin yau da kullum a sabuwar shekara ta 2026.

Babban sakataren ma’aikatar, Malam Ahmad Isah, ya bayyana haka lokacin da ya ke kare kiyasin kasafin kudin ma’aikatar a gaban kwamatin ayyuka da sufuri na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Babban Sakataren ya yi bayanin cewar, za a yi amfani da mafi yawan kudaden ne wajen gudanar da ayyukan hanyoyin mota tsakanin gariruwa da hanyoyin burji da kuma titunan cikin gari.

Yana mai cewar, haka kuma za a gudanar da ayyukan hanyoyi a manyan makarantun jihar ciki har Jami’ar Sule Lamido da ke Kafin Hausa da kwalejin fasaha da ke Dutse da cibiyar binciken aikin gona ta Kazaure, da kwalejin koyon aikin lafiya matakin farko da ke Jahun da sauransu.

Sai dai kuma babban sakataren ya koka dangane da bukatar daukar injiniyoyi domin aiki a ma’aikatar da hukumar gyaran hanyoyin mota JIRMA da kuma daukar sabbin jami’an duba lafiyar ababen hawa wato V.I.O, idan aka yi la’akari da karancin ma’aikata saboda masu yin ritaya.

Alhaji Ahmad Isah ya kara da cewar ma’aikatar tana kokarin cimma yarjajjeniya da makarantar koyon tukin jirgin sama ta kasa da ke Zaria domin amfani da filin jirgin sama na Dutse a matsayin sansanin koyon tukin jirgin sama.

Kazalika, ya ce makarantar koyon tukun mota da ke karamar hukumar Birnin Kudu za ta amfana da wasu ayyuka a sabuwar shekara.

A nasa jawabin, shugaban kwamatin ayyuka da sufuri na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Bulangu Alhaji Yusuf Ahmad Soja, ya yi addu’ar Allah Ya sa kasafin kudin ya karfafa cigaban jihar nan a sabuwar shekara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  •  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki