Rundunar Sojan Nijeriya Ta Fara Gasar Wasanni A Sakkwato
Published: 10th, April 2025 GMT
Runduna ta 8 ta sojojin Najeriya ta fara gasar wasanni ta kasa da ake gudanarwa duk shekara a jihar Sokoto da nufin karfafa sojojin Najeriya don shiryawa tsaron kasa.
Babban Jami’in Kwamandan runduna ta takwas Manjo Janar Ibikunle Ajose ya ce gasar tana nuni ne kai tsaye ga hafsan hafsoshin sojin kasar na ganin an gyara da sauya dabarun jagoranci da fagen fama a matakin farko.
GOC wanda ya samu wakilcin kwamandan runduna ta 78 da ke samar da kayayyaki da sufuri, Birgediya Janar Moses Udom Ikobah, ya bayyana cewa fafatawar ta yi daidai da kokarin da rundunar sojojin Najeriya ke yi na inganta yaki da ta’addanci ta fuskar tsaro.
Ya bukaci dukkan mahalarta taron da su kiyaye mafi girman matsayin wasanni, aiki tare, da rikon amana.
A jawabin maraba da Kwamandan, Birgediya Janar AbdulMalik Jibia Mohammed, shiyya ta 8, ya bayyana farin cikinsa da gudanar da taron tare da bayyana muhimmancinsa fiye da yadda ake gudanar da gasar.
Ya ce an shirya gasar ne domin karfafa kananan shugabanni, da karfafa kimar aikin soja, da kuma samar da kwakkwaran runduna a tsakanin sojoji da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin sassan, tare da kara kaimi, da juriya, da dabara na jami’an da ba manyan jami’ai ba.
Birgediya Janar Abdulmslik Jibia wanda ya ba da misali da dabarun da atisayen ke da su, ya ce gasar za ta kunshi abubuwa da dama da suka hada da karatun taswira, ninkaya, atisayen iri iri, da juriya, da sarrafa makamai, da nufin gwada shirye-shiryen yakar duk wani abin da zai taso.
Gidan Rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa, taron wanda ya dauki tsawon mako guda ana gudanar da shi, ya tattaro tsare-tsare daga sassan sassan, da suka hada da bataliya ta 1 da 17 da 48 da 58, da kuma rundunar da aka kafa, duk sun fafata ba don daukaka ba, sai dai don nuna shirye-shiryensu na gudanar da aiki da kuma kwazonsu na kwarewa.
NASIR MALALI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
An gudanar da taron tattaunawa na duniya kan kirkire-kirkire da bude kofa da ci gaba na bai daya, jiya Juma’a a birnin Lagos na Nijeriya. Yayin taron wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos suka shirya, ministan kula da harkokin matasa na Nijeriya Ayodele Olawande da shugaban CMG Shen Haixiong, sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
A cewar ministan na Nijeriya, cikin shekaru 5 da suka gabata, dubban matasan kasar sun ci gajiyar tallafin karatu da shirye-shiryen horo da na musaya da Sin ta samar, kuma wannan hadin gwiwa da ake yi a aikace ya kara fahimta da aminci tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, a shirye ma’aikatarsa take ta karfafa hadin gwiwa da sassa masu ruwa da tsaki na kasar Sin wajen ci gaba da fadada shirye-shiryen musaya da na hadin gwiwa da suka shafi matasa.
A nasa bangare, Shen Haixiong ya ce a matsayinta na babbar kafar yada labarai dake watsa shirye shiryenta ga sassa daban daban na duniya, tashar talabijin ta CCTV dake karkashin CMG da abokan huldarta, za su yayata shawarar Sin ta jagorantar harkokin duniya da gabatar da tafarkin Sin na zamanantar da kanta da karfinta na kirkire kirkire a sabon zamani ga al’ummar duniya. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA