Majalissar Dokokin Rasha ta amince da yerjejeniyar huldar ta shekara 20 da Iran
Published: 9th, April 2025 GMT
Majalissar Dokokin Rasha ta amince da yerjejeniyar huldar ta shakaru 20 tsakanin kasar da Iran.
Wannan na nuna muhimmin mataki na zurfafa dangantakar siyasa, soja da tattalin arziki tsakanin Moscow da Tehran.
Yarjejeniyar ta tsawon shekaru 20, wakilan majalisar sun amince da ita ne a kuri’ar da aka kada a ranar Talata ta yadda kasashen biyu za su iya yin hadin gwiwa cikin tsari da inganci.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin da takwaransa na kasar Iran Massoud Pezeshkian ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar a cikin watan Janairu, da nufin karfafa hadin gwiwa a fannoni daban daban da suka hada da tsaro, makamashi, kudi, sufuri, masana’antu, noma, al’adu, da kimiyya da fasaha.
Yarjejeniyar ta kuma bada damar zuba jari a fannin mai da iskar gas, da kuma raya ayyukan hadin gwiwa na dogon lokaci a fannin makamashin nukiliya cikin lumana.
A cikin ‘yan shekarun baya-bayan nan dai kasashen Iran da Rasha, sun kara karfafa hadin gwiwarsu a bangarori daban-daban, duk kuwa da tsauraran takunkumin da kasashen yamma suka kakaba musu.
Matakin ya zo ne a daidai lokacin da rikicin yankin ke kara ruruwa, sakamakon barazanar yaki da shugaban Amurka Donald Trump ya yi kan Iran idan har Tehran ta gaza cimma matsaya da Washington kan shirinta na nukiliya na zaman lafiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Sai dai babu wani tabbaci daga gwamnatin Iran ko Isra’ila kan cewa sun yarda su dakatar da yaƙin.
Trump ya kira rikicin da ake ciki da suna “yaƙin kwana 12,” yana mai cewa wannan rikici da za a iya yin shekaru ana fafatawa da shi bai bazu ba, kuma ba zai bazu ba.
Mene ne ke faruwa yanzu?
Bayan da Trump ya sanar da cewa an tsagaita wuta, Isra’ila ta ce an kashe mutane uku sakamakon hare-haren da Iran ta kai.
Amma ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce babu wata yarjejeniya ta tsagaita wuta.
Sai dai ya ce Iran za ta daina kai hari idan Isra’ila ma ta dakatar da nata.
Rikicin ya tsananta ne bayan Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke Qatar, wanda ya sa Trump ya nemi a dakatar da faɗan.
Me Iran da Isra’ila suka ce?
Gidan talabijin na Iran (IRINN) ya ce an tsagaita wuta ne bayan da Iran ta samu nasara a harin da ta kai.
Sun ce Trump ne ya roƙi a daina faɗam.
Ministan harkokin wajen Iran ya ce Iran ta daina kai hari tun ƙarfe 4 na dare, idan har Isra’ila za ta daina nata.
Har yanzu Isra’ila ba ta fitar da wata sanarwa ba kan tsagaita wutar, sai dai bayan sanarwar Trump, Isra’ila ta sake kai hari Iran.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp