Adadin wadanda suka yi shahada a zirin Gaza ya karu zuwa 58 a cikin ‘yan sa’o’i da suka gabata, yayin da wasu 213 suka jikkata sakamakon kazamin harin bam da Isra’ila ta kai a yankin.

Jiragen yakin Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun kai hari kan fararen hula da gidajensu, a ci gaba da luguden wutar da suke yia  kan fararen hula a yankuna da dama na Gaza.

Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta sanar da samun sabbin adadin wadanda suka yi shahada sakamakon hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ke kai wa zirin Gaza tun daga ranar 7 ga watan Oktoban 2023, inda adadin shahidai ya kai 50,810 yayin da adadin wadanda suka jikkata ya kai 115,688.

Adadin wadanda suka raa rayukansu tun daga ranar 18 ga Maris ya kai 1,449 sannan 3,647 suka jikkata.

A cikin wannan yanayi, wakilin Al-Mayadeen ya rawaito cewa, dakarun mamaya sun kai wani gagarumin farmakin a yankunan arewacin zirin Gaza. Har ila yau sun kafa wani sansanin soji a yankin Al-Muntar da ke unguwar Shuja’iyya da ke gabashin birnin Gaza, wanda ya zo daidai da lokacin hare-haren jiragen sama a yankunan gabashin unguwar.

Akasarin wadanda suka rasa rayukansu dai mata ne da kananan yara da kuma tsoffi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Rundunar sojin ba ta fitar da sanarwa ba game da wannan hari na baya-bayan nan, amma hukumar DSS ta tabbatar da faruwar lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata