Leadership News Hausa:
2025-06-25@00:38:03 GMT

Li Qiang Ya Tattauna Da Shugabar Kwamitin EU

Published: 9th, April 2025 GMT

Li Qiang Ya Tattauna Da Shugabar Kwamitin EU

Li Qiang ya yi nuni da cewa, a kwanakin baya, kasar Amurka ta sanar da kara buga harajin kwastam ga dukkan kasashe abokanta na cinikayya ciki har da Sin da Turai, wanda mataki ne da bangare daya ya dauka, da ba da kariya ga cinikayya, da cin zarafin tattalin arziki. Ya ce, kasar Sin ta dauki matakai don tabbatar da ikon mulkinta da moriyar samun ci gaba cikin aminci, kana da tabbatar da ka’idojin cinikayya da adalci a duniya.

Ya kara da cewa, ya kamata Sin da Turai su kara mu’amala da juna, da bude kofa ga juna don tabbatar da yin ciniki da zuba jari cikin ‘yanci, da kiyaye tsarin samar da kayayyaki a duniya yadda ya kamata, ta yadda za su kara tabbatar da bunkasuwar tattalin arzikinsu da na duniya baki daya.

 

A nata bangare, Ursula von der Leyen ta bayyana cewa, matakan kara buga harajin kwastam na kasar Amurka sun kawo illa ga cinikayya tsakanin kasa da kasa, tare da yin mummunan tasiri ga kasashen Turai da Sin da sauran kasashe marasa karfi. Ta ce, bangarorin Turai da Sin sun yi kokarin tabbatar da tsarin yin ciniki tsakanin bangarori daban daban bisa tushen WTO da adalci da ‘yanci, da kiyaye bunkasa huldar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasa da kasa yadda ya kamata, lamarin da ya dace da moriyar bangarorin biyu har ma da ta duk duniya baki daya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz

Gwamnatin Amurka ta buƙaci ƙasar Sin da ta hana Iran rufe mashigar tekun Hormuz, ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin jigilar kayayyaki a duniya.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya yi kiran ne bayan da kafar yada labarai ta Iran, Press TV ta ruwaito cewa majalisar dokokin ƙasar ta amince da shirin rufe mashigar.

Duk wani cikas ga samar da man fetur zai yi tasiri mai tsanani ga tattalin arzikin duniya.

Ƙasar Sin ce babbar mai sayen mai daga Iran kuma tana da kyakkyawar alaka da Tehran.

Harin Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —Masani NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya

Farashin man fetur ya tashi bayan harin da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran, inda farashin man Brent crude ya kai matsayinsa mafi girma cikin watanni biyar.

Matakin rufe mashigar tekun Hormuz wadda kusan kashi 20 cikin ɗari na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta cikinta, zai iya jefa duniya cikin bala’in rashin mai.

Masani kan harkokin kasuwanci Gerrit Heinemann ya shaida wa kafar yaɗa labarai ta Daily Mail ta ƙasar Birtaniya, cewa idan Iran ta zaɓi rufe mashigar, sakamakon zai zama “bala’i.”

Mashigar hanya ce ta kasuwanci mai mahimmanci ga duniya, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na man fetur na duniya ke bi ta mashigar teku. Kazalika adadi mai yawa na iskar Gas Mai Ruwa (LNG), na bi ta mashigar,  wanda hakan ya sa ta zama “mafi muhimmancin mashigar isar da man fetur a duniya.”

Kwamandan Rundunar Juyi Juya Halin Musulunci na Iran kuma ɗan majalisar dokokin ƙasar, Esmail Kosari ya bayyana cewa wannan matakin yana cikin ajandarsu kuma “za a yi shi duk lokacin da ya zama dole.”

A ƙarshen makon jiya Kowsari ya sanar cewa rufe mashigar tekun Hormuz “yana cikin matakan da gwamnatin ƙasar ke duba yiwuwar ɗauka, kuma Iran za ta yanke shawara da ya fi dacewa.”

Press TV ya ruwaito cewa matakin rufe mashigar tekun Hormuz bai kammala ba, har yanzu Majalisar Koli ta Tsaro ta Kasa ta Iran ce ke da hurumin yanke shawara ta ƙarshe kan lamarin.

Amma Kowsari ya bayyana cewa Iran ba ta iyakance iya matakin da za ta ɗauka a kan Isra’ila ba, kuma, “martanin soji wani yanki ne kawai na martaninmu gaba ɗaya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha
  • Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
  • CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026
  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
  • Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato