Li Qiang Ya Tattauna Da Shugabar Kwamitin EU
Published: 9th, April 2025 GMT
Li Qiang ya yi nuni da cewa, a kwanakin baya, kasar Amurka ta sanar da kara buga harajin kwastam ga dukkan kasashe abokanta na cinikayya ciki har da Sin da Turai, wanda mataki ne da bangare daya ya dauka, da ba da kariya ga cinikayya, da cin zarafin tattalin arziki. Ya ce, kasar Sin ta dauki matakai don tabbatar da ikon mulkinta da moriyar samun ci gaba cikin aminci, kana da tabbatar da ka’idojin cinikayya da adalci a duniya.
A nata bangare, Ursula von der Leyen ta bayyana cewa, matakan kara buga harajin kwastam na kasar Amurka sun kawo illa ga cinikayya tsakanin kasa da kasa, tare da yin mummunan tasiri ga kasashen Turai da Sin da sauran kasashe marasa karfi. Ta ce, bangarorin Turai da Sin sun yi kokarin tabbatar da tsarin yin ciniki tsakanin bangarori daban daban bisa tushen WTO da adalci da ‘yanci, da kiyaye bunkasa huldar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasa da kasa yadda ya kamata, lamarin da ya dace da moriyar bangarorin biyu har ma da ta duk duniya baki daya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Soja ya soka wa ɗan sanda wuƙa har Lahira a Taraba
Wani kurtun soja ya soka wani ɗan sanda mai mukamin Constable, Aaron John da wuƙa har lahira a garin Jalingo, hedikwatar Jihar Taraba.
Kakakin ’yan sanda na jihar, James Lashen, ya ce wannan mummunan al’amari ya faru ne da misalin karfe 9 na dare a ranar Litinin, a unguwar Mayo-Goyi, da ke gefen birnin Jalingo.
Lashen ya bayyana cewa marigayi John ya samu kiran gaggawa daga wasu mazauna yankin dangane da sabani da suka samu da sojan.
A yayin da yake kokarin warware rikicin, sai sojan mai suna Dauda Dedan, ya soka masa wuƙa.
Ya ce, “Mun samu rahoton lamarin daga hedikwatar Brigade ta 6 ta Rundunar Sojin Najeriya, da tabbacin cewa za a kamo sojan da ya tsere domin fuskantar hukunci,” in ji Lashen.
Ya ƙara da cewa rundunar soji ta fara bincike kan lamarin, tare da tabbatar wa ’yan sanda cewa za su haɗa kai wajen kamo wanda ake zargi.
“Sojoji da ’yan sanda na aiki tare. Mun kai ziyara har gidan sojan, kuma za mu tabbatar an kama shi domin ya fuskanci hukunci daidai da abin da ya aikata,” in ji Lashen.
Ya jaddada cewa dangantaka tsakanin sojoji da ’yan sanda a jihar Taraba tana da kyau kuma babu wata matsala a tsakaninsu.