Sojojin HKI sun kara yawan hare-haren da suke kaiwa kan Falasdinawa a Gaza, a dai-dai lokacinda ake kiranta zuwa tsagaita wuta a gazar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar kungiyar kare fararen hula ta falasdinawa a Gaza, tana fadar haka a safiyar yau Talata. Ta kuma kara da cewa, Ta kuma kara da cewa a daren jiya kadai jiragen yakin yahudawan sun kashe akalla falasdinawa 19 mafi yawansu yara kanana.

Labarin ya nakalto kakakin kungiyar kare fararen hula na Gaza Mhmood Bassal yana fadar haka, ya kuma kara da crawa , a garin Deir Balah jiragen yakin yahudawan sun kai hari a kan wani gida inda suka kashe yara 5 da manyan mutane 4.

Sannan sun sake kai hare-hare kafin safiyar yau Talata a garin Beit Lahiya da kuma birnin Gaza, inda a nan ma suka kashe mutabe 10.

A jiya litinin ma sojojin HKI sun kashe fiye da mutane 24 a cikin zirin gaza gaba daya. Daya daga cikin hare-haren na jiya Litinin ya kai ga shahadar wani dan jaridar na tashar talabijin ta ‘Palastine Today’ wanda yake cikin tentin da yan jaridu suka kada a cikin asbitin Naser a garin Khan Yunus na kudancin Gaza.

Hilmi Alfaqwi ya kone kurmus a wannan harin tare da wani mutum mai suna  Yusuf Al-Khazandar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna

Bangarorin ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa sun kai hari kan sojojin mamaya a wani farmakin hadin gwiwa da suka kai a Khan Yunus

Dakarun Sarayal-Quds bangaren sojin kungiyar Jihadul-Islami da kuma dakarun Izzuddeen Al-Qassam bangaren sojin kungiyar gwagwagrmayar Musulunci ta Hamas sun tabbatar da cewa: Sun yi nasarar kashe sojojin mamayar Isra’ila tare da raunata wasu a farmakin hadin gwiwa da suka kai kan yankin “Unguwar Turawa” a kudu maso gabashin Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza.

Dakarun Sarayal-Quds a cikin wani takaitaccen bayani da suka fitar sun bayyana cewa: Sun gudanar da wani farmakin hadin gwiwa tare da dakarun Al-Qassam kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da suka kutsa cikin yankin Unguwar Turawa a kudu maso gabashin Khan Yunus, bayan da suka yi artabu da su gaba da gaba.

A nata bangaren, rundunar Al-Qassam ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Mayakan Al-Qassam tare da mayakan Sarayal- Quds, sun samu nasarar kai hari kan sojojin yahudawan sahayoniyya da ke cikin wani gida, da makamai masu linzami na TBG.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci  
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • ‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
  • ‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna
  • Cutar Kwalara Ta Yadu A Sudan Baya Ga Matsalar Tashe-Tashen Hankulan Da Suke Ci Gaba Da Yuduwa A Kasar
  • Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
  • Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza