Sojojin HKI sun kara yawan hare-haren da suke kaiwa kan Falasdinawa a Gaza, a dai-dai lokacinda ake kiranta zuwa tsagaita wuta a gazar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar kungiyar kare fararen hula ta falasdinawa a Gaza, tana fadar haka a safiyar yau Talata. Ta kuma kara da cewa, Ta kuma kara da cewa a daren jiya kadai jiragen yakin yahudawan sun kashe akalla falasdinawa 19 mafi yawansu yara kanana.

Labarin ya nakalto kakakin kungiyar kare fararen hula na Gaza Mhmood Bassal yana fadar haka, ya kuma kara da crawa , a garin Deir Balah jiragen yakin yahudawan sun kai hari a kan wani gida inda suka kashe yara 5 da manyan mutane 4.

Sannan sun sake kai hare-hare kafin safiyar yau Talata a garin Beit Lahiya da kuma birnin Gaza, inda a nan ma suka kashe mutabe 10.

A jiya litinin ma sojojin HKI sun kashe fiye da mutane 24 a cikin zirin gaza gaba daya. Daya daga cikin hare-haren na jiya Litinin ya kai ga shahadar wani dan jaridar na tashar talabijin ta ‘Palastine Today’ wanda yake cikin tentin da yan jaridu suka kada a cikin asbitin Naser a garin Khan Yunus na kudancin Gaza.

Hilmi Alfaqwi ya kone kurmus a wannan harin tare da wani mutum mai suna  Yusuf Al-Khazandar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

An miƙa batun zuwa Rundunar ‘yansandan Jihar don ci gaba da bincike kafin gurfanar da wanda ake zargin a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
  • Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco