Wani jami’in ’yan sanda ya shaida wa Leadership cewa: “Duk da haramta bukukuwan sallah, an gudanar da hawa a motocin Sarkin a rana ta uku bayan Sallah, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce.”

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani bayani daga fadar Sarkin Kano game da gayyatar da aka yi masa.

Ga hoton takardar gayyatar da ‘yansandan suka fitar:

Daga kanmu, magana ta ƙare.

Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Gayyata Hawan Sallah Sarki

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta gano harsasai 210 da aka jefar a kan babbar hanyar Zariya zuwa Funtuwa, a unguwar Dogo Itace da ke Samaru, Zariya.

Lamarin ya faru ne lokacin da DPO na Samaru tare da tawagarsa suke sintiri a kan hanyar.

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau

Jama’ar yankin ne suka kira rundunar cewar fasinjojin wata mota ƙirar Volkswagen Golf mai launin baƙi sun jefar da wata jaka, sannan suka tsere.

Da jami’an rundunar suka isa, sun tarar da jakar da aka jefar.

Bayan gudanar da bincike, sun gano harsasai 210 na ɗangon 7.56mm.

DPO ɗin yankin ya sanar da sauran jami’an rundunar da ke kan hanyar Funtuwa domin dakatar da motar amma ba a ga motar ba.

Ana zargin direban da fasinjojin motar sun lura da jami’an tsaron da ke kan hanyar, wanda hakan ya sa suka zubar da jakar.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya yi kira ga jama’a da ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai.

Ya jaddada ƙudirin rundunar na ci gaba da sintiri da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Ya kuma gargaɗi masu aikata laifi da su guji duk wani yunƙurin tayar da zaune-tsaye, inda ya ce duk wanda aka kama zai fuskanci hukunci mai tsanani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Ramaphosa ya soki kalaman Trump na cewa ba zai gayyaci shi a taron G20
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano