Koch Usman Abdullahi Zai Jagoranci Kano Pillars A Karon Farko Bayan Dakatarwa
Published: 5th, April 2025 GMT
Kocin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars Abdallah Usman zai jagoranci kungiyar a karon farko cikin makonni 5 a wasan da Pillars zasu kara da Haertland Owerri.
Wasan na mako 32 a gasar Firimiya ta Nijeriya da za a buga a filin wasa na Sani Abacha dake Kofar Mata a birnin Kano, zai zama wani mataki da Abdallah zai sake kwantar da hankalin magoya bayan ƙungiyar bayan hatsaniyar da su ka samu a ƙarshen watan Fabrairu.
Pillars na mataki na 8 da maki 44 a wasa 31 da su ka buga, yayinda Heartland Owerri ke matsayi na 18 da maki 35 a wasanni 31.
Nasara a gida zai sa Pillars ta sake samun damar buga gasar Confederation Cup, amma kuma rashin nasara zai sake nitsar da kungiyar da kuma fargabar yin biyu babu a wannan kakar wasannin sakamakon wasanni 7 kacal su ka rage.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kano Pillars
এছাড়াও পড়ুন:
Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
Majiyar tsaron kasar ta Kamaru sanar da cewa, da dama daga cikin sojojin kasar sun rasa rayukansu sanadiyyar wani hari da kungiyar Bokoharam ta kai musu ta hanyar amfani da manyan bindigogi da kuma jirgin sama maras matuki akan iyaka da Najeriya.
Majiyar ta ce an kai harin ne a yankin Sagami dake kusa da tafkin Chadi a gundumar Logun mai iyaka da kasar Najeriya.
Ita dai kungiyar Bokoharam ta addabi kasashen Najeriya, Kamaru da kuma jamhuriyar Nijar. Yankun arewacin kasar ta Kamaru ya fara fuskantar kai hare-hare daga wannan kungiyar ne tun a 2014 wanda kuma har yanzu yana ci gaba da faruwa daga lokaci zuwa lokaci.