HausaTv:
2025-06-15@16:38:34 GMT

Isra’ila ta sake kai hare-hare ta sama kan kasar Siriya

Published: 4th, April 2025 GMT

Jiragen yakin Isra’ila sun kai karin hare-hare ta sama kan kasar Siriya, inda suka bijirewa gargadin Majalisar Dinkin Duniya game da hadassa asarar fararen hula yayin da suke ci gaba da kai wa kasar ta Larabawa hare-hare.

Rahotanni sun ce a ranar alhamis, jiragen saman Isra’ila sun kai hare-hare a kalla sau biyu a kan wuraren da sojoji a kusa da birnin Damascus, inda bayanai suka ce sun kai hari a yankunan Al-Kiswah da Al-Muqaylibah.

Kawo yanzu dai babu rahoton asarar rayuka.

Hare-haren sun zo ne kasa da kwana guda bayan hare-haren da Isra’ila ta kai makamancin haka inda ta kashe mutane 13.

Fararen hula 9 ne suka mutu wasu da dama kuma suka jikkata a wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai a lardin Dara’a da ke kudu maso yammacin kasar Siriya a yammacin ranar Laraba.

Isra’ila dai ta tsananta kai hare-hare kan Siriya tun bayan da ‘yan tawayen HTS suka karbe iko daga hannun gwamnatin Bashar Al’Assad a watan Disambar bara.

Wakilin Majalisar Dinkin Duniya a kasar Syria Geir Pedersen a ranar Alhamis ya yi Allah wadai da karuwar hare-haren soji da gwamnatin Isra’ila ke yi, yana mai gargadin cewa suna yin zagon kasa ga yunkurin sake gina kasar Syria da kuma kara jefa kasar cikin mawuyacin hali.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce “Irin wadannan ayyuka na kawo cikas ga kokarin samar da sabuwar kasar Siriya mai zaman lafiya da yankin, da kuma jefa Siriya a cikin wani mawuyacin hali.”

Tun bayan rugujewar gwamnatin Bashar al-Assad, sojojin Isra’ila ke kai hare-hare ta sama a kan cibiyoyin da suke bayyanawa da na soji, da kuma rumbun adana kayan yaki na sojojin Siriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kai hare hare kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Bisa la’akari da haka, a fili kasar Sin tana adawa da matakin da Isra’ila ta dauka na keta dokokin kasa da kasa, inda ta kai wa kasar Iran hari, lamarin da ba za a amince da shi ba, musamman ma ta la’akari da yadda kasashe daban daban ke ci gaba da neman hanyar daidaita batun nukiliyar kasar ta Iran ta hanyar siyasa.

Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin ta bukaci Isra’ila da Iran da su warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, da lalubo bakin zaren kasancewa tare cikin kwanciyar hankali da lumana. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba