HausaTv:
2025-07-31@17:42:30 GMT

Isra’ila ta sake kai hare-hare ta sama kan kasar Siriya

Published: 4th, April 2025 GMT

Jiragen yakin Isra’ila sun kai karin hare-hare ta sama kan kasar Siriya, inda suka bijirewa gargadin Majalisar Dinkin Duniya game da hadassa asarar fararen hula yayin da suke ci gaba da kai wa kasar ta Larabawa hare-hare.

Rahotanni sun ce a ranar alhamis, jiragen saman Isra’ila sun kai hare-hare a kalla sau biyu a kan wuraren da sojoji a kusa da birnin Damascus, inda bayanai suka ce sun kai hari a yankunan Al-Kiswah da Al-Muqaylibah.

Kawo yanzu dai babu rahoton asarar rayuka.

Hare-haren sun zo ne kasa da kwana guda bayan hare-haren da Isra’ila ta kai makamancin haka inda ta kashe mutane 13.

Fararen hula 9 ne suka mutu wasu da dama kuma suka jikkata a wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai a lardin Dara’a da ke kudu maso yammacin kasar Siriya a yammacin ranar Laraba.

Isra’ila dai ta tsananta kai hare-hare kan Siriya tun bayan da ‘yan tawayen HTS suka karbe iko daga hannun gwamnatin Bashar Al’Assad a watan Disambar bara.

Wakilin Majalisar Dinkin Duniya a kasar Syria Geir Pedersen a ranar Alhamis ya yi Allah wadai da karuwar hare-haren soji da gwamnatin Isra’ila ke yi, yana mai gargadin cewa suna yin zagon kasa ga yunkurin sake gina kasar Syria da kuma kara jefa kasar cikin mawuyacin hali.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce “Irin wadannan ayyuka na kawo cikas ga kokarin samar da sabuwar kasar Siriya mai zaman lafiya da yankin, da kuma jefa Siriya a cikin wani mawuyacin hali.”

Tun bayan rugujewar gwamnatin Bashar al-Assad, sojojin Isra’ila ke kai hare-hare ta sama a kan cibiyoyin da suke bayyanawa da na soji, da kuma rumbun adana kayan yaki na sojojin Siriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kai hare hare kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

 Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI

Shugaban kasar Lebanon wanda ya gabatar da jawabi da safiyar yau ya ce; A cikin sakwannin da mu ka aike wa Amurka, mun bukaci ganin an kawo karshen hare-haren da Isra’ila take ci gaba da kawo wa Lebanon, ta sama, kasa da ruwa, haka nan kuma kisan gillar da take yi wa mutane a cikin kasar.”

Shugaba Aun ya kuma yi jinjina ga dukkanin shahidan kasar da su ka kwanta dama saboda kare Lebanon,kuma yana a matsayin wani abu ne mai kima da daraja a wurinmu.”

Shugaba Aun na Lebanon ya kuma ce, Isra’ila abokiyar gaba ce wacce take hana mutanen da yaki ya tarwatsa komawa zuwa garuruwansu da kuma sake gina kudancin Lebanon da yaki ya rusa.”

Haka nan kuma ya ce , sojojin Lebanon sun sadaukar da kawukansu ta hanyar kasancewa a tare da mutanen kudancin Lebanon.

Danagen da makaman Hizbullah, Shugaban kasar ya ce nauyi ne da ya rataya a wuyansa da kuma dukkanin ‘yan siyasa da su ga cewa makamai suna hannun gwamnati ne kadai, a hannun soja da jami’an tsaro.”

Har ila yau ya kara da cewa, yanayin da ake ciki baya da bukatuwa da duk wani abu da zai zama tsokana da tayar da hankali, ba kuma za su bari ‘yan ta’adda su cutar da al’umar Lebanon ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Sojojin Mamaya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza July 31, 2025 Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu
  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa