NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
Published: 25th, March 2025 GMT
Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kebbi ta raba kayan abinci da kudi ga iyalan mambobinta da suka rasu a lokacin da suke kan aikin jarida, a matsayin kyautar azumin Ramadan.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kungiyar na Jiha, Kwamared Bello Sarki Abubakar, ya ce suna gudanar da wannan shiri a duk shekara, tun bayan kaddamar da shi da tsohon shugaban kungiyar na jiha Alhaji Aliyu Jajirma ya yi, domin faranta ran iyalan abokan aikinsu da suka rasu.
Kwamared Sarki Abubakar ya bayyana cewa dukkan shugabannin kungiyar da suka gabata sun tabbatar da ci gaba da gudanar da wannan shiri a duk lokacin azumin Ramadan domin rage wa iyalan mamatan radadin wahalhalun rayu.
Ya sanar da cewa kowane iyali daga cikin iyalan mambobi 21 da suka rasu za su karɓi buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 25 da kuma naira dubu goma.
Yayin da yake gode wa Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin Kwamared Nasiru Idris saboda goyon bayan da take bai wa kungiyar, Kwamared Sarki ya yaba da ayyukan ci gaba da Gwamna Nasir Idris ya aiwatar a cikin shekaru biyu da suka gabata domin inganta rayuwar al’ummar jihar.
Kwamishinan Watsa Labarai da Al’adu na Jihar Kebbi, Alhaji Yakubu Ahmed BK, yayin da yake yaba wa shugabancin kungiyar saboda tallafin da ta bai wa iyalan mamatan, ya tabbatar wa kungiyar cewa Gwamnatin jihar za ta ci gaba da fifita jin daɗin ‘yan jarida a jihar.
Haka kuma, ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa badi an gudanar da wannan taro cikin gagarumin shiri domin faranta wa iyalan mamatan rai.
A madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daya daga cikin matan wadanda suka rasu, Hajiya Hadiza Abdullahi, ta gode wa kungiyar saboda tunawa da su bayan rasuwar mazajensu.
Daga Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: da suka rasu Jihar Kebbi
এছাড়াও পড়ুন:
An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
An yi kira ga manoma a jihar Kwara da su yi taka tsan-tsan domin hasashen za a samu ruwan sama da kuma tsawa da ake hasashen nan da kwanaki masu zuwa.
A wata sanarwa da kwamishinan noma da raya karkara na jihar, Dr, Afees Abolore ya fitar, ya ce a cewar hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet, ana sa ran wasu sassa na jihar za su fuskanci ruwan sama da kuma yiwuwar tsawa.
Ya ce za a fuskanci ruwan sama ne da rana da yamma, tsakanin Litinin 28 ga Yuli da Laraba 30 ga Yuli, 2025.
Ya yi bayanin cewa duk da cewa ba a sami ruwan sama ba tukuna, yanayin da ke gaba zai iya kawo cikas ga ayyukan noma da ake ci gaba da yi, musamman ga masu sharefilaye, da watsin taki, ko girbin amfanin gona.
Ya yi nuni da cewa wuraren da ke da ƙarancin magudanar ruwa ko kuma waɗanda ke kusa da hanyoyin ruwa na iya zama mafi haɗari ga ambaliya.
Sanarwar ta shawarci manoman da su daina amfani da takin zamani domin gujewa wankewa da almubazzaranci, da kuma girbi manyan amfanin gona da wuri domin hana lalacewa daga ruwan sama.
Yana ƙarfafa manoma da su ɗauki hasashen da gaske kuma su hanzarta yin aiki don rage cikas da kiyaye rayuwarsu.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU