Aminiya:
2025-07-31@18:30:57 GMT

Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe

Published: 25th, March 2025 GMT

A ƙoƙarinta na tallafa wa marayu da mabuƙata, gidauniyar Zakkah da Wakafi a Gombe ta raba wa yara marayu da mabuƙata 100 kayan Sallah.

Da yake jawabi a lokacin rabon tufafin, Shugaban gidauniyar, Amir Abdullahi Abubakar Lamido, ya ce al’adar gidauniyar ce ta riƙa zaƙulo mabuƙata tare da tallafa musu musamman a lokutan bukukuwan Sallah.

An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe

Ya bayyana cewa, a da can gidauniyar na karɓo tsoffin tufafi daga hannun masu hannu da shuni, tana tsaftacewa tare da sake ƙunshe su kafin rabawa.

Amma wannan shekarar, gidauniyar ta ɗauki sabon tsari na sayan sababbin tufafi daga matan da ta koyar da sana’o’in hannu.

Waɗannan mata da suka samu horo a sana’o’i irinsu ɗinki, haɗa sarƙa da abun wuya na mata, da kuma ƙera takalma sun samu damar sayar wa gidauniyar kayayyakin da suka ƙera.

Lamido ya ce wannan hanya ba wai kawai ta amfani da tufafi don marayu da mabuƙata ba, har ma ta ba wa mata damar ƙarfafa musu gwiwa  kan kasuwanci.

Lamido ya yi kira ga masu hannu da shuni su karkatar da zakkar su zuwa ga Zakkah da Wakafi tare da tabbatar musu cewa gudunmawarsu za ta isa ga waɗanda suka cancanta.

Ya ƙara da cewa, da dama daga cikin masu ba da gudummawa sun nuna gamsuwa da yadda gidauniyar ke gudanar da ayyukanta cikin gaskiya da tasiri.

Bayan rabon tufafin Sallah, gidauniyar ta kuma tallafa wa mata guda 75 da jari na ₦15,000 kowannensu.

Waɗannan mata sun samu horo kan yadda za su sarrafa kuɗin su da kyau, ciki har da tanadin kaso ɗaya bisa uku na ribar su a cikin asusu na musamman na tsawon shekara guda don ƙarfafa kasuwancin su ya dore.

Sakataren Jama’atu Nasril Islam (JNI), Saleh Danburan, ya yaba wa gidauniyar bisa ƙoƙarinta na taimakon al’umma tare da kira da ta ci gaba da tsayawa kan turbar addinin Musulunci.

Fitaccen malamin addini musulunci Malam Bello Doma, ya jinjina wa ayyukan gidauniyar tare da bayar da shawarar kafa wani bankin al’umma don bayar da rance marar riba cikin sharuɗa masu sauƙi.

A cewarsa, wannan zai samar da taimakon kuɗi ga al’umma ba tare da kunyata su ko ƙin karɓar buƙatunsu ba yayin da suka nemi taimako.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidauniyar Zakkah jihar Gombe kayan Sallah Marayu

এছাড়াও পড়ুন:

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Bayanin da ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya yi a baya-bayan nan game da hasashe kan tattalin arzikin kasar Sin cikin shekaru biyar masu zuwa ya jawo hankalin duniya sosai. Kuma sakamkon binciken jin ra’ayoyin jama’a da CGTN na babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG ya yi a tsakanin masu bayyana ra’ayoyi 47,000 a kasashe 46 daga shekarar 2023 zuwa 2025, ya nuna jama’ar sun nuna yakini game da karfi da juriyar tattalin arzikin kasar Sin.

Binciken ya nuna cewa, yawancin masu bayyana ra’ayoyin daga sassan duniya suna da kyakkyawan fata ga tattalin arzikin kasar Sin wajen samun bunkasa mai kyau a dogon lokaci, inda amincewarsu ta kai kashi 74.7 bisa dari, da 81.3 bisa dari, da kuma 81.9 bisa dari cikin shekaru uku a jere.

Binciken da aka yi a bana ya kuma nuna cewa, masu bayyana ra’ayoyin suna da kwarin gwiwa game da samun damammaki masu kyau a kasuwar Sin a cikin yanayin kasa da kasa mai sarkakiya da tashe-tashen hankula. A cikinsu akwai kashi 79.8 bisa dari da suka bayyana cewa, babbar kasuwar Sin ta ba da muhimman damammaki ga kasashen da suke gudanar da kasuwanci a ciki.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci