Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
Published: 25th, March 2025 GMT
A ƙoƙarinta na tallafa wa marayu da mabuƙata, gidauniyar Zakkah da Wakafi a Gombe ta raba wa yara marayu da mabuƙata 100 kayan Sallah.
Da yake jawabi a lokacin rabon tufafin, Shugaban gidauniyar, Amir Abdullahi Abubakar Lamido, ya ce al’adar gidauniyar ce ta riƙa zaƙulo mabuƙata tare da tallafa musu musamman a lokutan bukukuwan Sallah.
Ya bayyana cewa, a da can gidauniyar na karɓo tsoffin tufafi daga hannun masu hannu da shuni, tana tsaftacewa tare da sake ƙunshe su kafin rabawa.
Amma wannan shekarar, gidauniyar ta ɗauki sabon tsari na sayan sababbin tufafi daga matan da ta koyar da sana’o’in hannu.
Waɗannan mata da suka samu horo a sana’o’i irinsu ɗinki, haɗa sarƙa da abun wuya na mata, da kuma ƙera takalma sun samu damar sayar wa gidauniyar kayayyakin da suka ƙera.
Lamido ya ce wannan hanya ba wai kawai ta amfani da tufafi don marayu da mabuƙata ba, har ma ta ba wa mata damar ƙarfafa musu gwiwa kan kasuwanci.
Lamido ya yi kira ga masu hannu da shuni su karkatar da zakkar su zuwa ga Zakkah da Wakafi tare da tabbatar musu cewa gudunmawarsu za ta isa ga waɗanda suka cancanta.
Ya ƙara da cewa, da dama daga cikin masu ba da gudummawa sun nuna gamsuwa da yadda gidauniyar ke gudanar da ayyukanta cikin gaskiya da tasiri.
Bayan rabon tufafin Sallah, gidauniyar ta kuma tallafa wa mata guda 75 da jari na ₦15,000 kowannensu.
Waɗannan mata sun samu horo kan yadda za su sarrafa kuɗin su da kyau, ciki har da tanadin kaso ɗaya bisa uku na ribar su a cikin asusu na musamman na tsawon shekara guda don ƙarfafa kasuwancin su ya dore.
Sakataren Jama’atu Nasril Islam (JNI), Saleh Danburan, ya yaba wa gidauniyar bisa ƙoƙarinta na taimakon al’umma tare da kira da ta ci gaba da tsayawa kan turbar addinin Musulunci.
Fitaccen malamin addini musulunci Malam Bello Doma, ya jinjina wa ayyukan gidauniyar tare da bayar da shawarar kafa wani bankin al’umma don bayar da rance marar riba cikin sharuɗa masu sauƙi.
A cewarsa, wannan zai samar da taimakon kuɗi ga al’umma ba tare da kunyata su ko ƙin karɓar buƙatunsu ba yayin da suka nemi taimako.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidauniyar Zakkah jihar Gombe kayan Sallah Marayu
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara
Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna
Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya
Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.
Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
ShareTweetSendShare MASU ALAKA