Aminiya:
2025-09-17@21:52:12 GMT

Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe

Published: 25th, March 2025 GMT

A ƙoƙarinta na tallafa wa marayu da mabuƙata, gidauniyar Zakkah da Wakafi a Gombe ta raba wa yara marayu da mabuƙata 100 kayan Sallah.

Da yake jawabi a lokacin rabon tufafin, Shugaban gidauniyar, Amir Abdullahi Abubakar Lamido, ya ce al’adar gidauniyar ce ta riƙa zaƙulo mabuƙata tare da tallafa musu musamman a lokutan bukukuwan Sallah.

An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe

Ya bayyana cewa, a da can gidauniyar na karɓo tsoffin tufafi daga hannun masu hannu da shuni, tana tsaftacewa tare da sake ƙunshe su kafin rabawa.

Amma wannan shekarar, gidauniyar ta ɗauki sabon tsari na sayan sababbin tufafi daga matan da ta koyar da sana’o’in hannu.

Waɗannan mata da suka samu horo a sana’o’i irinsu ɗinki, haɗa sarƙa da abun wuya na mata, da kuma ƙera takalma sun samu damar sayar wa gidauniyar kayayyakin da suka ƙera.

Lamido ya ce wannan hanya ba wai kawai ta amfani da tufafi don marayu da mabuƙata ba, har ma ta ba wa mata damar ƙarfafa musu gwiwa  kan kasuwanci.

Lamido ya yi kira ga masu hannu da shuni su karkatar da zakkar su zuwa ga Zakkah da Wakafi tare da tabbatar musu cewa gudunmawarsu za ta isa ga waɗanda suka cancanta.

Ya ƙara da cewa, da dama daga cikin masu ba da gudummawa sun nuna gamsuwa da yadda gidauniyar ke gudanar da ayyukanta cikin gaskiya da tasiri.

Bayan rabon tufafin Sallah, gidauniyar ta kuma tallafa wa mata guda 75 da jari na ₦15,000 kowannensu.

Waɗannan mata sun samu horo kan yadda za su sarrafa kuɗin su da kyau, ciki har da tanadin kaso ɗaya bisa uku na ribar su a cikin asusu na musamman na tsawon shekara guda don ƙarfafa kasuwancin su ya dore.

Sakataren Jama’atu Nasril Islam (JNI), Saleh Danburan, ya yaba wa gidauniyar bisa ƙoƙarinta na taimakon al’umma tare da kira da ta ci gaba da tsayawa kan turbar addinin Musulunci.

Fitaccen malamin addini musulunci Malam Bello Doma, ya jinjina wa ayyukan gidauniyar tare da bayar da shawarar kafa wani bankin al’umma don bayar da rance marar riba cikin sharuɗa masu sauƙi.

A cewarsa, wannan zai samar da taimakon kuɗi ga al’umma ba tare da kunyata su ko ƙin karɓar buƙatunsu ba yayin da suka nemi taimako.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidauniyar Zakkah jihar Gombe kayan Sallah Marayu

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin