HausaTv:
2025-06-15@19:48:29 GMT

An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila

Published: 21st, March 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta sanar da korar shugaban hukumar liken asiri ta cikin gidan kasar Ronen Bar, wanda Firaministan kassar Benjamin Netanyahu ya ce bai gamsu da kwarewarsa ba hasali ma ba’a yarda da shi.

 “Gwamnati baki daya ta amince da shawarar Firaminista Benjamin Netanyahu na kawo karshen wa’adin” Ronen Bar, wanda zai bar ofis idan aka nada magajinsa ye zuwa ranar 10 ga watan Afrilu, in ji ofishin Firayim Minista a cikin wata sanarwa.

Rashin gamsuwa da aikin na kokaren shugaban hukumar ta Shin-bet, ta fito fili a baya bayan bayan bayannan da suke fitowa game da harin kungiyar Hamas na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Ronen Bar, wanda aka nada a watan Oktoba 2021 na wa’adin shekaru biyar, ya tabbatar tun kafin yanke hukuncin cewa zai kare kansa a gaban “hukumomin da suka dace”.

A cikin wata wasika da ya aikewa jama’a da yammacin Alhamis, ya bayyana cewa dalilan da suka sa aka kore shi daga aiki, wanda Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Lahadi, ya dogara ne da “sha’awar kansa” da nufin “hana bincike kan al’amuran da suka shafi harin ranar 7 ga Oktoba da wasu muhimman batutuwa da Shin Bet ke bincikar su.”

Dama shugaban hukumar ya amince kwanan baya da gazawar hukumar da ayek jagoranta wajen hana harin na Hamas.

A cikin wata sanarwa da aka fitar kwanan baya, shugaban hukumar ta Shin Bet, Ronen Bar, ya amince da cewa, hukumar ta ” gaza a cikin aikinta” na dakile ayyukan Operation Al-Aqsa, tare da kutsawa manyan sansanonin Isra’ila bayan da sojoji da ‘yan sandan gwamnatin suka yi kaca-kaca da su, kuma y ace ya dauki nauyin gazawar a wuyansa.

Hukumar ta amince da gagarumin gibi a cikin tattara bayanan sirri da kuma dogaro da matakan kariya da ake da su, wanda ya haifar da rashin fahimtar kungiyar Hamas, tare da sauran kungiyoyin gwagwarmaya.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wani “binciken cikin gida” ya nuna cewa, an gaza wajen dakile harin na Hamas.

Binciken da sojojin Isra’ila suka gudanar ya soki yadda gwamnatin kasar ke dogaro da bayanan sirri da kuma raina karfin Hamas, kura-kuran da suka haifar da mummunan sakamako ga gwamnatin Isra’ila.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shugaban hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Asalin Tudun Loess
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran