Aminiya:
2025-07-31@06:26:04 GMT

’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili

Published: 4th, April 2025 GMT

Tsohon Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Kano kuma tsohon Mashawarci na Musamman ga Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, CP Muhammad Wakili (ritaya), ya jaddada cewa dole ne ’yan sanda su yi amfani da ikon da suke da shi cikin gaskiya da adalci, don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Da yake jawabi a wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Gombe, a matsayin wani ɓangare na bikin makon ’yan sanda, CP Wakili ya ce ba zai yiwu jami’an tsaro su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata ba tare da goyon bayan al’umma ba.

An ceto yara ’yan Taraba da aka yi safararsu zuwa Kudu Adadin waɗanda suka mutu a harin Filato ya kai 52

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su kasance ƙofar su a buɗe ga jama’a, su saurari ƙorafe-ƙorafensu, tare da gina kyakkyawar alaƙa da su.

” ’Yan sanda ba abokan gaba ba ne ga jama’a, su ne ginshiƙin tsaro da ci gaba. Amma dole ne su kula da yadda suke amfani da ikon da aka ba su, domin kada ya rikiɗe ya zama cin zarafi,” in ji Wakili.

Ya yabawa Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, bisa ƙwazon da yake nunawa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Wakili ya kuma buƙaci al’umma da su bada haɗin kai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Gombe da ƙasa baki ɗaya.

A nasa jawabin, Kwamishinan ‘Yan sanda na Gombe, CP Bello Yahaya, ya jaddada cewa Ranar ‘Yan Sanda ta Duniya, da ake gudanarwa duk shekara na da nufin tunawa da irin rawar da ’yan sanda ke takawa wajen tabbatar da tsaro.

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su ƙara ƙaimi wajen kusantar da kansu ga jama’a, su nuna gaskiya da ƙwarewa a ayyukansu, domin gina amana da fahimtar juna.

A nasa ɓangaren, Kwamishinan Harkokin Tsaro da Cikin Gida na Gombe, Laftanar Kanar Abdullahi Bello (ritaya), ya jinjinawa CP Yahaya bisa shirya wannan muhimmin taro.

“Wannan irin shiri yana taimakawa wajen gina kyakkyawar fahimta tsakanin jami’an tsaro da jama’a. Ina kira ga rundunar ’yan sanda da su ci gaba da irin waɗannan shirye-shirye,” in ji shi.

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa manufar wannan bikin ita ce kusantar da jama’a ga ’yan sanda tare da inganta ayyukansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda CP Muhammad Wakili Gwamna Inuwa Yahaya

এছাড়াও পড়ুন:

 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus

Da safiyar yau Laraba Yahudawa ‘yan share wuri zauna sun kutsa cikin masallacin kudus a karkashin kariyar jami’an tsaron ‘yan sahayoniya, tare da yin ayyukan bautar yahudanci a ciki.

Wannan kutsen dai yana zuwa ne a daidai lokacin da sojojin HKI suke ci gaba da kai wa Falasdinawa hare hare  a cikin yankuna mabanbanta na Gaza da yammacin kogin Jordan.

Rahotanni da suke fitowa daga Falasdinu sun ce ya zuwa yanzu adadin wadanda su ka yi shahada sun haura 18. Daga cikin wadanda su ka yi shahadar da akawi Fursunonin da aka ‘yanto su a musayar fursunoni tsakanin Hamas da HKI.

A yankin Khalil sojojin HKI sun kutsa cikin kauyen Ummul-Khair tare da kame mutane 8 bayan yin kutse a cikin gidajensu.

Haka nan kluma sojojin mamayar sun kama wasu matasa biyu  a garin “Tuba” wanda yake a Khalil.

Wasu Falasdinawan 3 sun yi shahada a yau Laraba a wurin karbar abinci, bayan da sojojin HKI su ka bude musu wuta.

A cikin asibitocin yankin na Gaza an  kai gawawwakin shahidai 16 daga cikinsu da akwai 16 da su ma masu neman abinci ne.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  •  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati