Aminiya:
2025-11-03@08:04:00 GMT

’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili

Published: 4th, April 2025 GMT

Tsohon Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Kano kuma tsohon Mashawarci na Musamman ga Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, CP Muhammad Wakili (ritaya), ya jaddada cewa dole ne ’yan sanda su yi amfani da ikon da suke da shi cikin gaskiya da adalci, don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Da yake jawabi a wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Gombe, a matsayin wani ɓangare na bikin makon ’yan sanda, CP Wakili ya ce ba zai yiwu jami’an tsaro su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata ba tare da goyon bayan al’umma ba.

An ceto yara ’yan Taraba da aka yi safararsu zuwa Kudu Adadin waɗanda suka mutu a harin Filato ya kai 52

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su kasance ƙofar su a buɗe ga jama’a, su saurari ƙorafe-ƙorafensu, tare da gina kyakkyawar alaƙa da su.

” ’Yan sanda ba abokan gaba ba ne ga jama’a, su ne ginshiƙin tsaro da ci gaba. Amma dole ne su kula da yadda suke amfani da ikon da aka ba su, domin kada ya rikiɗe ya zama cin zarafi,” in ji Wakili.

Ya yabawa Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, bisa ƙwazon da yake nunawa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Wakili ya kuma buƙaci al’umma da su bada haɗin kai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Gombe da ƙasa baki ɗaya.

A nasa jawabin, Kwamishinan ‘Yan sanda na Gombe, CP Bello Yahaya, ya jaddada cewa Ranar ‘Yan Sanda ta Duniya, da ake gudanarwa duk shekara na da nufin tunawa da irin rawar da ’yan sanda ke takawa wajen tabbatar da tsaro.

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su ƙara ƙaimi wajen kusantar da kansu ga jama’a, su nuna gaskiya da ƙwarewa a ayyukansu, domin gina amana da fahimtar juna.

A nasa ɓangaren, Kwamishinan Harkokin Tsaro da Cikin Gida na Gombe, Laftanar Kanar Abdullahi Bello (ritaya), ya jinjinawa CP Yahaya bisa shirya wannan muhimmin taro.

“Wannan irin shiri yana taimakawa wajen gina kyakkyawar fahimta tsakanin jami’an tsaro da jama’a. Ina kira ga rundunar ’yan sanda da su ci gaba da irin waɗannan shirye-shirye,” in ji shi.

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa manufar wannan bikin ita ce kusantar da jama’a ga ’yan sanda tare da inganta ayyukansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda CP Muhammad Wakili Gwamna Inuwa Yahaya

এছাড়াও পড়ুন:

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta raba zunzurutun kuɗi naira miliyan 63.4 ga iyalan jami’anta 84 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

Rundunar ta raba kudin ne a ƙarƙashin tsarin inshorar rayuwa da kuma tsarin kula da lafiyar iyali na Sufeto Janar na ’yan sanda.

 

An gudanar da rabon kuɗin ne a ranar Alhamis a Maiduguri babban birnin jihar kamar yadda Kakakin rundunar a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana a cikin wata sanarwa.

A cewar sanarwar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, wanda ya wakilci Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun, shi ne ya gabatar da takardun cakin kudin ga iyalan waɗanda suka ci gajiyar tallafin.

“Harkokin da suka shafi jami’anmu da iyalansu ya kasance babban fifiko ga rundunar,” in ji CP Abdulmajid yayin taron.

Ya ce wannan shiri na nuna tausayi da rikon amana, da kuma jagoranci mai nagarta daga Sufeto Janar wajen girmama jaruman da suka sadaukar da rayukansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyalan da suka amfana da tallafin da su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace, musamman wajen tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, da jin daɗin rayuwar iyalansu gaba ɗaya.

Ya yaba wa Sufeto Janar bisa ci gaba da tsare-tsaren jin daɗin jami’an rundunar, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyin da ke samar da agaji da kwanciyar hankali ga iyalan waɗanda suka rasa masoyansu.

A nata jawabin a madadin iyalan da suka amfana, Misis Nana Goni ta nuna godiya ga Sufeto Janar bisa goyon bayan da ya bayar, tana mai tabbatar da cewa za su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya kamata don inganta rayuwar iyalansu.

Rundunar ta bayyana cewa wannan rabon tallafi ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kula da walwala da mutuncin jami’anta da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m