Kasar Sin Ta Sanar Da Daukar Matakan Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje Kan Wasu Ma’adinan Da Ba Kasafai Ake Samun Su Ba
Published: 4th, April 2025 GMT
Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin tare da hadin gwiwar babbar hukumar kwastam ta kasar Sin, ta sanar a yau Juma’a cewa, za ta fara aiwatar da matakan kiyaye fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje kan nau’o’in ma’adinai bakwai matsakaita da masu nauyi da ba kasafai ake samun su, wadanda suka hada da samarium, gadolinium, terbium, dysprosium, lutetium, scandium da yttrium.
Har ila yau, ma’aikatar ta sanar cewa, ta yanke shawarar kara wasu kamfanonin Amurka 16 da ke barazana ga tsaron kasa da moriyarta a cikin jerin sunayen kamfanonin da ta dauki matakin hana fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje a kansu, tare da sanya kamfanonin Amurka 11 cikin jerin sunayen kamfanonin da ba su da tabbas, yayin da ta sanar da kaddamar da wani binciken yaki da shigo da kayayyaki fiye da kima kan shigo da wasu na’urorin daukar hoton CT na x-ray wadanda suka samo asali daga Amurka da Indiya.
Kazalika, babbar hukumar kwastam ta kasar Sin a yau Juma’a har ila yau, ta dakatar da takardun cancantar shigo da kayayyakin wasu kamfanoni shida na Amurka sakamakon batutuwan da suka shafi bincike da kuma kandagarkin kayayyakinsu. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta
Kasar Amurka ta sanar da dakatar da bai wa mutanen Nijar bisa ta shiga cikin kasarta har illa masha Allahu.
Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka ne ya tabbatar da cewa an dakatar da bayar da bisa din ga ‘yan kasar Nijar da suke son shiga cikin kasar, saboda abinda ya kira matsala da ake da ita da gwamnatin Nijar, ba tare da yin Karin bayani ba.
Sai dai kuma sanarwar ta yi togiya akan jami’an diflomasiyya da sauran jami’an gwamanti,kamar yadda wani sako na diplomasiyya ya nuna a ranar 25 ga watan Yuli.
Wannan matakin na Amurka ya biyo byan rashin jituwar da ake da shi a tsakanin gwamatin Amurka da gwamnatin Jamhuriyar Nijar. A watan Satumba da ya shude ne dai Amurka ta kammala dauke sojojinta daga kasar Nijar bayan da gwamnatin sojan kasar ta umarce su, su fice daga kasar.
Da akwai sojojin Amurka da sun kai 1000 a cikin jamhuriyar Nijar, da janye su yake a matsayin kwankwasar kan Amurka da rage tasirinta a yammacin Afirka.
Gabanin juyin mulkin da aka yi a kasar dai Amurka tana amfani da wannan cibiyar a abinda take kira fada da ta’addaci a yammacin Afirka. Sai dai kuma hakan bai hana ci gaba da yaduwar ayyukan ta’addanci a cikin kasashen na yammacin Afirka ba.