Aminiya:
2025-12-14@23:17:55 GMT

Wasu sarakunan gargajiya na ta’ammali da ƙwayoyi — Obasanjo

Published: 16th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya nuna damuwarsa kan yadda sarautar gargajiya ke rasa martabarta a ƙasar nan.

A cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’, ya bayyana cewa yanzu akwai masu laifi, ’yan daba, da masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka zama sarakuna a wasu yankuna na Najeriya.

Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

“A yau, akwai ’yan daba, masu safarar miyagun ƙwayoyi, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ake kira sarakuna,” in ji Obasanjo.

“Wannan abu ne mai matuƙar ban takaici, kuma yana daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya.”

Ya ce dole ne a dawo da mutunci da ƙimar sarautar gargajiya domin tana taka rawar gani a ci gaban ƙasa.

Har ila yau, ya gargaɗi shugabanni cewa idan ba su magance matsalolin da jama’a ke fuskanta ba, hakan na iya haifar da rikici a nan gaba.

“Idan gwamnati ba ta saurari kokensu ba—musamman matasa da suka fusata—to nan gaba abubuwa ba za su yi kyau ba,” in ji shi.

“Waɗanda suka hana a samu sauyi cikin lumana, za su gamu da sauyi ta hanyar tashin hankali.”

Obasanjo ya ƙara da cewa idan shugabannin Afirka suka yi watsi da wannan gargaɗi, hakan na iya haddasa rikici a nahiyar gaba ɗaya.

“Yin watsi da wannan gargaɗi kamar yin rawa ne lokacin da gidanka ke ci da wuta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi Miyagun ƙwayoyi Najeriya Sarakunan Gargajiya

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Tsatsauran Ra’yi Suna Kokarin Kaiwa Masu Hijira Da Musulmi A Ingila

Masu tsatsauran ra’ayi a Burtaniya sun gudanar da jerin gwano masu yawa a kasar don nuna kiyayya ga wadanda suka kaura zuwa kasar musamman musulmi.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran a nan Tehran ta bayyana cewa wannan ya nuna yadda mutane a kasar Burtaniya suka fada cikin rarraba mai zurfi a tsakaninsu dangane da yawan musulmi a kasar da kuma wadanda suka kaura daga kasashen duniya zuwa kasar.

Labarin ya kara da cewa wannan fahinta ta kin baki da kuma  musulmi ba zai rasa nasaba da abubuwan da shugaban kasar Amurka Donal Trump yake yi a kasar Amurka na korar baki da kuma nuna kiyayya ga musulmi ba. Wanda hakan yake narazana ga zaman lafiya tsakanin mabiya addinai daban –daban a kasar ba. Sannan wani abin lura shi ne ana iya ganin tutan HKI a hannun wadanda suke fitowa zanga-zangar kin jinin baki da kuma musulmi a kasar ta Burtania a cikin yan kwanakin nan. Wanda yake nuni da yadda Amurka da HKI suke da hannu a ayyukansu.  Labarin ya bayyana cewa wani dan siyasa Tommy Robinson ne yake jagorantar wadan nan zanga-zangar ta nuna kiyayya ga baki da kuma musulmi a birnin Londan. Sannan hare-hare a kan musulmi ya karu da kashi 90%   a kasar a kuma dukkan masallatai a birnin London.  Yawan zage-zage da kuma hare-hare a kan masallatai da kuma kan musulmi ya karu sosai a kasar musamman bayan yakin Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bukaci Mutanen Yemen Su Daina Kashe Juna December 14, 2025 Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia December 14, 2025 Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu December 14, 2025 Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani December 14, 2025 Araghchi ya bukaci Amurka ta girmama al’ummar Iran da gwamnatinta December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Tsatsauran Ra’yi Suna Kokarin Kaiwa Masu Hijira Da Musulmi A Ingila
  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki
  • Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169
  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci