Aminiya:
2025-07-05@17:49:12 GMT

Wasu sarakunan gargajiya na ta’ammali da ƙwayoyi — Obasanjo

Published: 16th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya nuna damuwarsa kan yadda sarautar gargajiya ke rasa martabarta a ƙasar nan.

A cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’, ya bayyana cewa yanzu akwai masu laifi, ’yan daba, da masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka zama sarakuna a wasu yankuna na Najeriya.

Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

“A yau, akwai ’yan daba, masu safarar miyagun ƙwayoyi, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ake kira sarakuna,” in ji Obasanjo.

“Wannan abu ne mai matuƙar ban takaici, kuma yana daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya.”

Ya ce dole ne a dawo da mutunci da ƙimar sarautar gargajiya domin tana taka rawar gani a ci gaban ƙasa.

Har ila yau, ya gargaɗi shugabanni cewa idan ba su magance matsalolin da jama’a ke fuskanta ba, hakan na iya haifar da rikici a nan gaba.

“Idan gwamnati ba ta saurari kokensu ba—musamman matasa da suka fusata—to nan gaba abubuwa ba za su yi kyau ba,” in ji shi.

“Waɗanda suka hana a samu sauyi cikin lumana, za su gamu da sauyi ta hanyar tashin hankali.”

Obasanjo ya ƙara da cewa idan shugabannin Afirka suka yi watsi da wannan gargaɗi, hakan na iya haddasa rikici a nahiyar gaba ɗaya.

“Yin watsi da wannan gargaɗi kamar yin rawa ne lokacin da gidanka ke ci da wuta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi Miyagun ƙwayoyi Najeriya Sarakunan Gargajiya

এছাড়াও পড়ুন:

An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima

Tauraron Kannywood kuma mai sayar da maganin gargajiya, Abdullahi Alhikima ya magantu bayan da wasu ‘yan Kannywood suka caccake shi kan kalaman da ya yi a kansu.

Aminiya ta rawaito cewa hatsaniyar ta samo asali ne bayan fitattun ‘yan Kannywood da suka hada da Abdul M Sharif, Nura M Inuwa, Abubakar Bashir Maishadda, Sadik Sani Sadik, da sauransu suka kai wa tsohon dan takarar shugaban kasa a PDP Atiku Abubakar ziyarar goyon baya.

Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Wannan ya tunzura Alhikma kasancewar wasu daga cikin wadanda suka je mubayi’ar ‘ya’yan kungiyar YBN ne a baya, da kuma 13/13 ta ubangidansa, mawaki Rarara.

A cikin wadanda Alhikima ya caccaka har da Shugaban Hukumar Fina-finai ta Ƙasa, Ali Nuhu.

Sai dai a kan hakan ne kuma wasu ke hasashen lallai ta tabbata alaƙa ta yi tsami tsakanin Alin da Rarara, wadanda a da suke abokai.

To sai dai Alhikman ya yi mi’ara koma baya, inda a ranar Laraba ya fito yana bayar da haƙuri, a cikin wani bidiyo da ya karade soshiyal midiya.

“Ina amfani da wannan dama domin janye kalamaina, na kuma bayar da hakuri ga ‘yan masana’antar Kannywood. Na yi wasu maganganu kuma zan janye bisa dalilai guda uku.

“Na farko maganar da na yi wasu na ganin ciyaman Alhaji Dauda Kahutu Rarara shi ne ya saka ni na yi wannan maganar. Ina ba da hakuri domin barranta shi da ita, domin ni na yi ta. Domin ya kira ni ya kuma nuna min kuskuren da ke cikin maganganuna. Kuma dama cikar dan adam shi ne idan shugabanka ya ce ka yi daidai ka karbi daidai ne. Idan shugabanka ya ce kayi kuskure ka karba.

“Haka kuma akwai abokiyar aikina Aishatul Humaira ta zaunar da ni ta gwada min kurakuran da ke cikin maganar da na yi, musamman a kan mai girma MD, Ali Nuhu. Wanda uba ne a wurinta a masana’antar. Hallau a cikin masana’antar tana da aminai maza da mata wanda suke da alaka ta mutunci da mutunta juna.”

Sai dai Alhikma ya yi togaciya a ban hakurin nasa, in da ya ce iya ‘yan Kannywood zai bai wa hakuri ban da wadanda ya kira da ‘yan shisshigi’.

Ita ma dai Aishatul Humairan ta bai wa ‘yan Kannywood din hakuri duk da ba da yawunta Alhikima ya tayar da hazon ba,  musamman Ali Nuhu, wanda ta ce uba ne a gare ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata