Wasu sarakunan gargajiya na ta’ammali da ƙwayoyi — Obasanjo
Published: 16th, March 2025 GMT
Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya nuna damuwarsa kan yadda sarautar gargajiya ke rasa martabarta a ƙasar nan.
A cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’, ya bayyana cewa yanzu akwai masu laifi, ’yan daba, da masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka zama sarakuna a wasu yankuna na Najeriya.
“A yau, akwai ’yan daba, masu safarar miyagun ƙwayoyi, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ake kira sarakuna,” in ji Obasanjo.
“Wannan abu ne mai matuƙar ban takaici, kuma yana daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya.”
Ya ce dole ne a dawo da mutunci da ƙimar sarautar gargajiya domin tana taka rawar gani a ci gaban ƙasa.
Har ila yau, ya gargaɗi shugabanni cewa idan ba su magance matsalolin da jama’a ke fuskanta ba, hakan na iya haifar da rikici a nan gaba.
“Idan gwamnati ba ta saurari kokensu ba—musamman matasa da suka fusata—to nan gaba abubuwa ba za su yi kyau ba,” in ji shi.
“Waɗanda suka hana a samu sauyi cikin lumana, za su gamu da sauyi ta hanyar tashin hankali.”
Obasanjo ya ƙara da cewa idan shugabannin Afirka suka yi watsi da wannan gargaɗi, hakan na iya haddasa rikici a nahiyar gaba ɗaya.
“Yin watsi da wannan gargaɗi kamar yin rawa ne lokacin da gidanka ke ci da wuta,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gargadi Miyagun ƙwayoyi Najeriya Sarakunan Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
Masu aikin ceto a Falasdinu, sun fada a ranar Litinin din da ta gabata cewa; An fito da gawawwakin shahidai 98 da aka binne su cikin gaggawa a lokacin yaki, a cikin harabar asibitin al-Shifa a cikin birnin Gaza.
An fito da gawawwakin ne dai domin kai su zuwa sanannun makabartun da ake da su a cikin yankin na Gaza,domin binnewa.
Sanarwar hukumar ceton ta ce; A tsakanin shahidan da akwai wasu 55 da ba iya tantance ko su wanene ba, sai dai an mika su ga kwararrun likitoci domin tantance da gano ko su wanene.
Ma’aikatan agaji suna ci gaba da fito da wasu gawawwakin na shahidai da aka binne a cikin asibitin, domin tantance su, kuma ana yin hakan ne dai a cikin kare hurumin matattun.
A farko-farkon kwanakin yakin Gaza, sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, sun kai hari akan wannan asibitin, wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane 500 a lokaci daya.
A wani labarin na daban, ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; A cikin sa’oi 24 da su ka gabata an kai gawawwakin shahidai 5, uku daga cikinsu sun kwanta dama ne sanadiyyar sabbin hare-haren da sojojin mamaya suke kai wa, duk da cewa an tsagaita wutar yaki. Sauran shahidan biyu kuwa wadanda aka fito da su ne daga karkashin baraguzai na gine-ginen da ‘yan sahayoniya su ka rusa gidaje da mutane a cikinsu a tsawon ranakun yaki.
Ma’aikatar kiwon lafiyar ta Gaza ta kuma ce, har yanzu da kawai adadi mai yawa na shahidai da suke a karkashin baraguzai, ana kuma samun jinkirin fito da su ne saboda rashin kayan aiki.
Daga tsagaita wutar yaki a ranar 11 ga watan Oktoba 2025 zuwa yanzu adadin wadanda su ka yi shahada sun kai 376, wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 981. Haka nan kuma an tono gawawwakin shahidai 626.
Idan aka koma zuwa Oktoba na 2023 kuwa, to adadin shahidan Falasdinawa ya kai 70,365, wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 171,058.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci