Aminiya:
2025-12-11@06:21:27 GMT

Wasu sarakunan gargajiya na ta’ammali da ƙwayoyi — Obasanjo

Published: 16th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya nuna damuwarsa kan yadda sarautar gargajiya ke rasa martabarta a ƙasar nan.

A cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’, ya bayyana cewa yanzu akwai masu laifi, ’yan daba, da masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka zama sarakuna a wasu yankuna na Najeriya.

Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

“A yau, akwai ’yan daba, masu safarar miyagun ƙwayoyi, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ake kira sarakuna,” in ji Obasanjo.

“Wannan abu ne mai matuƙar ban takaici, kuma yana daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya.”

Ya ce dole ne a dawo da mutunci da ƙimar sarautar gargajiya domin tana taka rawar gani a ci gaban ƙasa.

Har ila yau, ya gargaɗi shugabanni cewa idan ba su magance matsalolin da jama’a ke fuskanta ba, hakan na iya haifar da rikici a nan gaba.

“Idan gwamnati ba ta saurari kokensu ba—musamman matasa da suka fusata—to nan gaba abubuwa ba za su yi kyau ba,” in ji shi.

“Waɗanda suka hana a samu sauyi cikin lumana, za su gamu da sauyi ta hanyar tashin hankali.”

Obasanjo ya ƙara da cewa idan shugabannin Afirka suka yi watsi da wannan gargaɗi, hakan na iya haddasa rikici a nahiyar gaba ɗaya.

“Yin watsi da wannan gargaɗi kamar yin rawa ne lokacin da gidanka ke ci da wuta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi Miyagun ƙwayoyi Najeriya Sarakunan Gargajiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici

Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi da kuma shugaban kasar Azarbaijan Ilham Aleyev a birnin Baku sun tattauna kan dangantakar dake tsakaninsu da kuma hanyoyin da zaa bi wajen warware kalubalen da ake fuskanta.

Kasashen iran da Azarbaijan suna da alakar aladu da tarihi mai zurfi a tsakaninsu, kuma dukkan bangarorin biyu, sun jaddada game da mihimmancin ci gaba da tattaunawar diplomasiya domin kaucewa rashin fahimta tsakani.

Tattaunawar ta su ta kunshi hadin guiwar siyasa da lamarin da ya shafi makwabta da kuma hanyoyin kyautata dangantaka tsakani , kana kuma ya isar da sakon gaisuwar shugaban kasa mas’ud pezeshkiyan ga shugaban kasar ta Azarbaijan da kuma aniyarsa ta ganin an kara zurfafa danganata tsakaninsu.

Ana san bangaren shugaban kasar Azarbaijan Aliyuv ya bayyana shirinsa na yi amfani da kowwacce irin dama ta kara karfafa dagantaka tsakaninsu,  kuma ya bayyana ziyarar da shugaban iran pezeshkiyan ya kai a baya bayan nan a matsayin mai tarihi, kuma ta taka rawa sosai wajen samar da karin fahimtar juna .

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025  Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47