Aminiya:
2025-12-12@15:11:33 GMT

Wasu sarakunan gargajiya na ta’ammali da ƙwayoyi — Obasanjo

Published: 16th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya nuna damuwarsa kan yadda sarautar gargajiya ke rasa martabarta a ƙasar nan.

A cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’, ya bayyana cewa yanzu akwai masu laifi, ’yan daba, da masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka zama sarakuna a wasu yankuna na Najeriya.

Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

“A yau, akwai ’yan daba, masu safarar miyagun ƙwayoyi, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ake kira sarakuna,” in ji Obasanjo.

“Wannan abu ne mai matuƙar ban takaici, kuma yana daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya.”

Ya ce dole ne a dawo da mutunci da ƙimar sarautar gargajiya domin tana taka rawar gani a ci gaban ƙasa.

Har ila yau, ya gargaɗi shugabanni cewa idan ba su magance matsalolin da jama’a ke fuskanta ba, hakan na iya haifar da rikici a nan gaba.

“Idan gwamnati ba ta saurari kokensu ba—musamman matasa da suka fusata—to nan gaba abubuwa ba za su yi kyau ba,” in ji shi.

“Waɗanda suka hana a samu sauyi cikin lumana, za su gamu da sauyi ta hanyar tashin hankali.”

Obasanjo ya ƙara da cewa idan shugabannin Afirka suka yi watsi da wannan gargaɗi, hakan na iya haddasa rikici a nahiyar gaba ɗaya.

“Yin watsi da wannan gargaɗi kamar yin rawa ne lokacin da gidanka ke ci da wuta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi Miyagun ƙwayoyi Najeriya Sarakunan Gargajiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe

Wani mutum ya mutu, wasu da dama kuma sun jikkata lokacin da wata tirela ta yi karo da wata mota ƙirar akori kura Mitsubishi Canter a Damagum da misalin ƙarfe 12:50 na tsakar dare a ranar Laraba.

Kamar yadda kakakin rundunar ‘Yan sanda Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya ce tirelar, mai lambar rajista MUS 791 XH, wacce Aliyu Muhammad, mai shekara 30, daga Azare, ƙaramar hukumar Katagum, Jihar Bauchi ke tuƙawa tana tafiya daga Damaturu zuwa Legas lokacin da motar ta kufcewa direban ta afka wa motar da ke gabanta.

Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

Motar, mai mutane 18 da ke ciki da lamba AA 641 PKM, wadda Usman Muhammad, mai shekara 40 daga ƙauyen Yaskawel ne ke tuƙa ta.

Mai magana da yawun rundunar ya ce, an tabbatar da mutuwar fasinja ɗaya, Ɗahiru Maikuɗi mai shekara 40, daga ƙauyen Yaskawel, a babban asibitin Damagum yayin da wasu da dama suka jikkata.

A cewar rundunar, an tura waɗanda abin ya shafa shida zuwa asibitin Koyarwa da ke Damaturu don ƙarin kula da lafiyar su.

Hatsarin ya haifar da zanga-zanga daga matasan Damagum waɗanda suka koka game da yawan haɗurra a kan babbar hanyar Damaturu zuuwa Potiskum, musamman kusa da Damagum inda ake harkokin kasuwanci da zirga-zirgar masu sufuri a ƙasa ke ƙaruwa musamman a ranakun Lahadi da Laraba.

Jami’an ‘yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zangar don hana cin zarafin da ake yi wa mutane.

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, Emmanuel Ado ya yi wa iyalan wanda ya rasu ta’azɗiyar rashin mamacin ya jajantawa waɗanda suka jikkata yayin wannan hatsari  yana mai umurtar Jami’in ‘yan sandan yankin da ya yi aiki tare da ƙaramar hukumar kan matakan kariya na dogon lokaci.

Ya gargaɗi masu ababen hawa game da yin gudun wuce ƙima kuma ya yi kira da a bi ƙa’idodin zirga-zirga sosai, yana mai gargaɗin cewa, waɗanda suka karya doka za su fuskanci hukunci.

Kwamishinan ya kuma shawarci mazauna yankin da su guji yin harkokin kasuwanci kusa da babbar hanyar don rage ƙarin faruwar haɗurra.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta