HausaTv:
2025-10-26@14:16:51 GMT

 Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14

Published: 15th, March 2025 GMT

Ministan ayyuka da sufuri na kasar Lebanon Yusuf Rasamani ya bayyana cewa; Asarar da HKI ta jazawa kasar Lebanon a lokacin yaki ta kai dalar Amurka biliyan 14, tare da bayyana cewa kasar Rasha ta bijiro da cewa za ta taimaka.

Rasamani ya fada wa Radiyon “Sputnik” na Rasha cewa; Suna ci gaba da aiki tare da babban bankin duniya, domin tantance barnar da yakin Isra’ila ya haddasa a Lebanon.

Bugu da kari ministan ayyukan na kasar Lebanon ya kuma ce; Ma’aikatar ta fara aikin debe baraguzai a cikin garuurwan da za su iya isa, wadanda babu sojojin HKI a cikinsu.”

Haka nan kuma ya ce; Kasar ta Lebanon da kuma Bankin Duniya da Asusun bayar da Lamuni suna aiki domin fito da tsarin aiki na sake gina wuraren da yakin ya rusa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin, ya bayyana cewa su na nazarin dokoki guda 69 da kuma buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙudirin ƙirƙirar ƙananan hukumomi 278 bisa ga tsarin kundin mulkin 1999.

Barau, wanda shi ne shugaban Kwamitin Bita na Tsarin Mulki a majalisar dattawa, ya bayyana hakan ne a taron haɗin gwuiwa da kwamitocin majalisar dattawa da kwamitocin majalisar wakilai kan gyare-gyaren dokokin tsarin mulki da suka gudanar a Lagos.

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

Ya jaddada cewa an dauki lokaci mai tsawo wajen tattaunawa da al’umma da masu ruwa-da-tsaki da ƙungiyoyi daban-daban, domin kawo waɗannan ƙuduri a gaban majalisar.

Ya kuma bayyana burin majalisar cewa za ta miƙa kashi na farko na gyare-gyaren tsarin mulki ga majalisun jihohi kafin ƙarshen shekarar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe October 25, 2025 Manyan Labarai Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025 October 25, 2025 Manyan Labarai Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3) October 25, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu
  • Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
  • Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki
  • Tsohon Shugaban Hukumar Leken Asirin Dakarun IRGC Ya Ce: Yakin Kwanaki 12 Kan Iran Ya Canza Tunanin Makiya
  • Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin
  • Kwamishinan Gombe ya rasu a hatsarin mota
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Za Su Dauki Matakin Soji Kan Kasar Venezuela Nan Gaba Kadan
  • Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa
  •  Shugaban Kasar Amurka Ya Soke Shirin Ganawa Da Takwaransa Na Kasar Rasha
  • Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka