Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
Published: 15th, March 2025 GMT
Ministan ayyuka da sufuri na kasar Lebanon Yusuf Rasamani ya bayyana cewa; Asarar da HKI ta jazawa kasar Lebanon a lokacin yaki ta kai dalar Amurka biliyan 14, tare da bayyana cewa kasar Rasha ta bijiro da cewa za ta taimaka.
Rasamani ya fada wa Radiyon “Sputnik” na Rasha cewa; Suna ci gaba da aiki tare da babban bankin duniya, domin tantance barnar da yakin Isra’ila ya haddasa a Lebanon.
Bugu da kari ministan ayyukan na kasar Lebanon ya kuma ce; Ma’aikatar ta fara aikin debe baraguzai a cikin garuurwan da za su iya isa, wadanda babu sojojin HKI a cikinsu.”
Haka nan kuma ya ce; Kasar ta Lebanon da kuma Bankin Duniya da Asusun bayar da Lamuni suna aiki domin fito da tsarin aiki na sake gina wuraren da yakin ya rusa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kebbi, Muhammad Sama’ila Bagudo, ya kuɓuta bayan shafe fiye da mako guda a hannun ’yan bindigar da suka yi garkuwa da shi.
Aminiya ta ruwaito cewa an sace mataimakin shugaban majalisar ne a ranar Juma’a 31 ga Oktoba, 2025, jim kaɗan bayan ya kammala sallar la’asar a masallacin garinsu na Bagudo.
’Yan bindiga sun kashe kansila yayin Zaɓen Gwamnan Anambra Gwamna Soludo ya lashe Zaɓen Anambra karo na biyuSakataren gwamnatin jihar, Yakubu Tafida, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin Asabar.
Bayanai sun tabbatar da cewa lamarin na zuwa ne daidai da lokacin da aka gudanar da addu’o’in haɗin kai tsakanin Musulmai da Kiristoci domin neman zaman lafiya a jihar.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kebbi, CSP Nafiu Abubakar, ya tabbatar da cewa an saki mataimakin shugaban majalisar.
CSP Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka yana tare da iyalansa bayan mahukunta sun tabbatar da ƙoshin lafiyarsa a wani asibiti.
“An sace shi a ranar 31 ga Oktoba, amma an sako shi jiya [Asabar] kuma yanzu yana cikin ƙoshin lafiya kamar yadda mahukunta suka tabbatar,” in ji kakakin rundunar.
Ya ƙara da cewa rundunar ta yaba da jajircewar jami’an tsaro da suka shiga aikin ceto tare da goyon bayan al’umma, inda ya ce bayanan da jama’a suka bayar sun taka muhimmiyar rawa wajen ceto wanda aka sace lafiya.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za ta ci gaba da kai hare-hare kan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a faɗin jihar, tare da kira ga jama’a su kasance masu lura da duk wani motsi da ake zargi su kuma rika sanar da hukumomin tsaro cikin gaggawa.