Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar
Published: 14th, March 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta kafa sansanin soji a Ƙaramar Hukumar Arewa domin inganta tsaro.
Ya yi wannan roƙo ne bayan ziyarar da ya kai sansanin ‘yan gudun hijira a Kangiwa, bayan harin da wasu da ake zargin Lakurawa ne suka kai musu.
Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3Harin da aka kai a ranar 9 ga watan Maris ya yi sanadin mutuwar mutum 11 tare da ƙone ƙauyuka bakwai.
Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Birnin Debi, Garin Nagoro, da Garin Rugga.
“Sansanin soji a yankin zai taimaka wajen gaggauta kai ɗauki idan an kai wani hari,” in ji Gwamna Idris.
“Dole mu yi duk abin da za mu iya don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”
Yayin ziyarar tasa, gwamnan ya yi alƙawarin taimakawa wajen sake gina gidajen mutanen da suka rasa matsugunansu.
Haka kuma, ya umarci hukumomin ƙaramar hukumar da su riƙa samar wa ’yan gudun hijirar abinci, tare da yanka saniya bayan kwana huɗu.
Bugu da ƙari, ya umarci a yanka raguna biyu don jarirai huɗu da aka haifa a sansanin yayin rikicin.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Alhaji Sani Aliyu, ya gode wa gwamnan bisa ƙoƙarin da yake yi.
“Gwamnatin jiha tana bakin ƙoƙarinta wajen magance matsalar tsaro, amma muna buƙatar ƙarin tallafi daga Gwamnatin Tarayya,” in ji shi.
Gwamnan ya buƙaci mutanen da abin ya shafa da su ci gaba da haƙuri da addu’a, inda ya tabbatar musu da cewa gwamnati na ƙoƙarin kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamna Lakurawa Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
Wani soja mai muƙamin Las Kofur ya ɗirka wa matarsa harbi har lahira sannan ya kashe kansa a Jihar Neja.
Las Kofur Akenleye Femi da ke aiki a Bataliya ta 221, ya yi wannan aika-aika ne a Barikin Sojoji na Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja.
Muƙaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Soja ta 22 da ke Ilorin, Kyaftin Stephen Nwankwo, ne ya tabbatar da lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce abin ya faru ne a ranar 11 ga Oktoba, 2025.
Ya ce mutuwar sojan da matarsa ta haifar da tashin hankali a cikin sansanin soja, inda mazauna wurin suka shiga ɗimuwa da mamaki kan abin da zai iya jawo irin wannan lamari.
Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako“An gano gawar Last Kofur Femi da matarsa ne a cikin dakinsu da ke Block 15, Room 24 na Corporals and Below Quarters a Wawa Cantonment,” in ji Kyaftin Nwankwo.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa sojan yana kan aiki a cikin sansanin kafin ya nemi izinin zuwa gida domin wasu bukatun kansa, sai daga bisani aka gano gawarsu a gida.
Kyaftin Nwankwo ya ce an ajiye gawar mamatan domin ci gaba da bincike, kuma rundunar sojan na aiki tukuru don gano musabbabin lamarin.
Rundunar Soja ta Najeriya ta bayyana matuƙar baƙin cikinta kan wannan abin takaici, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalai, abokai da abokan aikin mamatan.
Kwamandan Rundunar, Birgediya Janar Ezra Barkins, ya sha alwashin gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru, tare da ɗaukar matakan da za su hana faruwar irin haka a nan gaba.