Aminiya:
2025-11-27@21:54:55 GMT

Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar

Published: 14th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta kafa sansanin soji a Ƙaramar Hukumar Arewa domin inganta tsaro.

Ya yi wannan roƙo ne bayan ziyarar da ya kai sansanin ‘yan gudun hijira a Kangiwa, bayan harin da wasu da ake zargin Lakurawa ne suka kai musu.

Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3

Harin da aka kai a ranar 9 ga watan Maris ya yi sanadin mutuwar mutum 11 tare da ƙone ƙauyuka bakwai.

Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Birnin Debi, Garin Nagoro, da Garin Rugga.

“Sansanin soji a yankin zai taimaka wajen gaggauta kai ɗauki idan an kai wani hari,” in ji Gwamna Idris.

“Dole mu yi duk abin da za mu iya don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”

Yayin ziyarar tasa, gwamnan ya yi alƙawarin taimakawa wajen sake gina gidajen mutanen da suka rasa matsugunansu.

Haka kuma, ya umarci hukumomin ƙaramar hukumar da su riƙa samar wa ’yan gudun hijirar abinci, tare da yanka saniya bayan kwana huɗu.

Bugu da ƙari, ya umarci a yanka raguna biyu don jarirai huɗu da aka haifa a sansanin yayin rikicin.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Alhaji Sani Aliyu, ya gode wa gwamnan bisa ƙoƙarin da yake yi.

“Gwamnatin jiha tana bakin ƙoƙarinta wajen magance matsalar tsaro, amma muna buƙatar ƙarin tallafi daga Gwamnatin Tarayya,” in ji shi.

Gwamnan ya buƙaci mutanen da abin ya shafa da su ci gaba da haƙuri da addu’a, inda ya tabbatar musu da cewa gwamnati na ƙoƙarin kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamna Lakurawa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A cikin shekarun nan, matsalolin tsaro a Najeriya—kamar ta’addanci, da garkuwa da mutane, da rikicin manoma da makiyaya, da kuma ayyukan ’yan bindiga—suna kara ta’azzara, lamarin da ya sanya al’umma da masana tsaro ke tambayar wace hanya ta fi dacewa gwamatani ta yi amfani da shi wajen kawo karshen wadannan matsaloli da suka ki ci suka ki cinyewa tsawon shekaru.

 

Yayin da wasu ke ganin amfani da karfin soji ne kadai hanyar da zai kawo karshen wannan matsala, wasu na ganin tattaunawa ne kadai mafita, wasu har ila yau na ganin idan aka yi amfani da gaurayen biyun zai fi dacewa.

NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?

Ko wanne daga cikin wadannan hanyoyi ne idan gwamnati ta yi amfai dashi ko da su don magance wannan matsala?

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi