Rasha ta caccaki gwamnatin Syria dangane da kisan kiyashin da jami’anta suke yi a kan tsiraru
Published: 14th, March 2025 GMT
Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa, a wani taron sirri da kwamitin sulhu na MDD ya yi a wannan mako kasar Rasha ta yi Allah-wadai da sabuwar gwamnatin kasar ta Syria dangane da kisan kiyashin da jami’anta suke yi a kan tsiraru a kasar.
Wannan dai na zuwa ne bayan da kungiyar kare hakkin dan Adam ta kasar Syria (SOHR) ta sanar da kashe fararen hula 1,383, galibi ‘yan Alawite a cikin makon da suka gabata.
Kasar Rasha ta yi gargadi kan karuwar ta’addanci a kasar Syria tare da kwatanta kashe-kashen da kisan kiyashin da aka yi a kasar Rwanda da abin da yake faruwa a yanzu a kasar Syria. Ta yadda masu rike da madafun iko da ‘yan bindigar da ke karkashinsu suke tara daruruwan fararen hula daga bangaren marasa rinjaye su kashe su baki daya, kamar yadda ‘yan kabilar Hutu suka rika yi wa ‘yan kabilar Tutsi a Rwanda a shekara ta 1994.
Jakadan kasar Rasha a Majalisar Dinkin Duniya Vassily Nebenzia, ya ce abin takaici shi ne babu wata kasa a duniya da ta dauki wani mataki domin ganin dakatar da wannan kisan kiyashi da ake yi a Syria.
Hotunan bidiyo da dama sun nuna Kungiyoyin da ke dauke da makamai karkashin inuwar kungiyar Tahrir Sham mai alaka da alkaida wadda kuma itace ta kfa gwamnatia halin yanzu a Syria tare da taimakon Turkiya da Qatar, su ne suke aiwatar da wannan kisan kiyashi a kan ‘yan alawiyya, bisa hujjar cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Bashar Assad.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
Jamus ta shiga sahun ƙasashen duniya da ke kiran a gaggauta tsagaita wuta a yaƙin da ke ci gaba da salwantar rayuka a ƙasar Sudan.
Sama da shekaru biyu ke nan Sudan na fama da yaƙin da ya ɗaiɗaita fararen hula baya ga asarar rayuka.
Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — TrumpMinistan Harkokin Wajen Jamus, Johann Wadephul, ya bayyana halin da Sudan ke ciki a matsayin “mummunan bala’i,” yana mai cewa babbar matsalar jinkai ta duniya a yanzu ta tattara ne a Sudan ɗin.
A taron da aka gudanar a Bahrain, ƙasashen Birtaniya da Jordan su ma sun yi magana kan rikicin, suna kiran da a kawo ƙarshen tashin hankalin.
A ƙarshen makon da ya gabata, RSF ta kori rundunar soji daga sansanin ta na ƙarshe a yammacin Darfur.
Rahotanni daga garin El-Fasher sun bayyana cewa ana samun kashe-kashe ba tare da shari’a ba, da fyaɗe da fashi har ma da hare-hare kan ma’aikatan agaji.
Wata Kungiyar Likitoci ta MSF a ranar Asabar ta ce ana fargabar dubban fararen hula sun maƙale sannan suna cikin mummunan haɗari a birnin Al Fasher wanda ya koma hannun dakarun RSF.
Rikicin Sudan ya fara ne a watan Afrilun 2023, bayan taƙaddama ta siyasa tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan, shugaban sojin ƙasar, da Mohamed Hamdan Dagalo (Hemedti), Kwamandan RSF.
Bayanai sun ce rikicin ya samo asali ne daga saɓani kan yadda za a haɗa rundunar RSF da sojojin ƙasar bayan juyin mulkin 2021 da ya hamɓarar da gwamnatin farar hula.
Tun daga lokacin, yaƙin ya zama wani mummunan bala’i na jin kai, inda Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) ta ce fiye da mutane miliyan bakwai sun tsere daga gidajensu, yayin da dubbai ke buƙatar taimakon gaggawa.