Rasha ta caccaki gwamnatin Syria dangane da kisan kiyashin da jami’anta suke yi a kan tsiraru
Published: 14th, March 2025 GMT
Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa, a wani taron sirri da kwamitin sulhu na MDD ya yi a wannan mako kasar Rasha ta yi Allah-wadai da sabuwar gwamnatin kasar ta Syria dangane da kisan kiyashin da jami’anta suke yi a kan tsiraru a kasar.
Wannan dai na zuwa ne bayan da kungiyar kare hakkin dan Adam ta kasar Syria (SOHR) ta sanar da kashe fararen hula 1,383, galibi ‘yan Alawite a cikin makon da suka gabata.
Kasar Rasha ta yi gargadi kan karuwar ta’addanci a kasar Syria tare da kwatanta kashe-kashen da kisan kiyashin da aka yi a kasar Rwanda da abin da yake faruwa a yanzu a kasar Syria. Ta yadda masu rike da madafun iko da ‘yan bindigar da ke karkashinsu suke tara daruruwan fararen hula daga bangaren marasa rinjaye su kashe su baki daya, kamar yadda ‘yan kabilar Hutu suka rika yi wa ‘yan kabilar Tutsi a Rwanda a shekara ta 1994.
Jakadan kasar Rasha a Majalisar Dinkin Duniya Vassily Nebenzia, ya ce abin takaici shi ne babu wata kasa a duniya da ta dauki wani mataki domin ganin dakatar da wannan kisan kiyashi da ake yi a Syria.
Hotunan bidiyo da dama sun nuna Kungiyoyin da ke dauke da makamai karkashin inuwar kungiyar Tahrir Sham mai alaka da alkaida wadda kuma itace ta kfa gwamnatia halin yanzu a Syria tare da taimakon Turkiya da Qatar, su ne suke aiwatar da wannan kisan kiyashi a kan ‘yan alawiyya, bisa hujjar cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Bashar Assad.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar
“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.
Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp