HausaTv:
2025-11-27@22:18:11 GMT

 Uganda ta tura dakaru na musamman zuwa babban birnin Sudan ta Kudu

Published: 12th, March 2025 GMT

Rundunar sojan Uganda ta sanar da tura dakaru na musamman domin tabbatar da tsaro a babban birnin Sudan ta Kudu bisa bukatar Juba, a daidai lokacin da ake fargabar sake barkewar yakin basasa, musamman a halin da ake ciki tsakanin shugaban Sudan ta Kudu da mataimakinsa na farko.

A wannan Talata rundunar sojin Uganda ta sanar da tura dakaru na musamman zuwa Juba, babban birnin Sudan ta Kudu.

Kakakin rundunar sojin Uganda Felix Kulayigye ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, batun tura sojojin na zuwa ne bisa bukatar gwamnatin Sudan ta Kudu.

An kara samun tashin hankali a ‘yan kwanakin nan a kasar Sudan ta Kudu mai arzikin man fetur, bayan da gwamnatin shugaba Salva Kiir ta kame wasu ministoci biyu da wasu manyan jami’an soji da ke kawance da mataimakin shugaban kasar na farko Riek Machar. Tuni dai aka saki minista guda.

Kamen da aka yi a Juba da kuma kazamin fadan da ya barke a kusa da garin Nasir na arewacin kasar ana ganin zai kawo cikas ga yarjejeniyar zaman lafiya ta shekarar 2018 da ta kawo karshen yakin basasa na tsawon shekaru biyar tsakanin dakarun da ke biyayya ga Kiir da Machar inda aka kashe kusan mutane 400,000.

Bayan barkewar yakin basasa a Sudan ta Kudu a shekara ta 2013, Uganda ta aike da dakarunta zuwa Juba domin tallafawa dakarun Kiir da ke yaki da Machar. Daga karshe dai sojojin Uganda sun janye a shekarar 2015. An sake tura sojojin Uganda zuwa Juba a shekara ta 2016 bayan da aka sake gwabza fada tsakanin bangarorin biyu, amma kuma aka janye su daga bisani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji

Sojojin Guinea-Bissau sun naɗa Janar Horta Nta Na Man a matsayin sabon shugaban ƙasar na rikon kwarya, kwana ɗaya bayan sun yi juyin mulki tare da kama shugaban ƙasar, Umaro Sissico Embalo.

Sojojin dai sun kwace mulkin ne yayin da ake shirin bayyana sakamakon zaɓen kasar mai cike da takaddama.

Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

“Na rantsar da kaina a matsayin shugaban Babban Kwamandan Soja,” in ji Janar Horta bayan ya karbi rantsuwar aiki a wani biki da aka gudanar a hedkwatar sojoji a ranar Alhamis, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito.

Daruruwan sojoji dauke da makamai sun kasance a wurin rantsuwar.

A ranar Laraba, kwana guda bayan manyan ’yan takara biyu a zaɓen shugaban ƙasa mai cike da takaddama kowannensu ya ayyana nasara, wata ƙungiyar hafsoshin soja ta bayyana cewa ta karɓi “cikakken iko” a ƙasar.

Sojojin sun karanta sanarwa a talabijin, suna bayyana cewa sun dakatar da tsarin zaɓe “har sai an ba da sanarwa ta gaba.”

Sun kifar da Shugaba Umaro Sissoco Embalo a sabon lamari na rikice-rikicen siyasa da ke yawan faruwa a ƙasar.

Wata ƙungiyar hafsoshin sojoji ta bayyana cewa ta karɓi cikakken iko da mulkin ƙasar, kwana guda bayan manyan ’yan takara biyu, Shugaba Umaro Sissoco Embalo da Fernando Dias, kowannensu ya yi ikirarin samun nasara.

Sojojin sun bayar da umarnin dakatar da tattara sakamakon zaɓen har sai an ba da sanarwa ta gaba.

Haka kuma sun bayar da umarnin rufe dukkan iyakokin ƙasa da na sama da ruwa, tare da sanya dokar hana fita da dare.

“An yin min juyinmulki,” in ji Embalo a zantarwarsa da gidan talabijin na Faransa France24 ta wayar tarho, yana mai cewa “yanzu haka ina hedkwatar babban hafsan sojoji.”

Shugaban babbar jam’iyyar adawa ta PAIGC, Domingos Simoes Pereira, ma an kama shi, in ji Haque. “Haka kuma mun ji cewa sojoji na ƙoƙarin katse intanet. An kuma sanya dokar hana fita.”

Shugaban rundunar tsaron fadar shugaban ƙasar, Denis N’Canha, shi ne dai sojan da ke jagorantar juyin mulkin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin
  • Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya