HausaTv:
2025-06-25@01:04:23 GMT

 Uganda ta tura dakaru na musamman zuwa babban birnin Sudan ta Kudu

Published: 12th, March 2025 GMT

Rundunar sojan Uganda ta sanar da tura dakaru na musamman domin tabbatar da tsaro a babban birnin Sudan ta Kudu bisa bukatar Juba, a daidai lokacin da ake fargabar sake barkewar yakin basasa, musamman a halin da ake ciki tsakanin shugaban Sudan ta Kudu da mataimakinsa na farko.

A wannan Talata rundunar sojin Uganda ta sanar da tura dakaru na musamman zuwa Juba, babban birnin Sudan ta Kudu.

Kakakin rundunar sojin Uganda Felix Kulayigye ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, batun tura sojojin na zuwa ne bisa bukatar gwamnatin Sudan ta Kudu.

An kara samun tashin hankali a ‘yan kwanakin nan a kasar Sudan ta Kudu mai arzikin man fetur, bayan da gwamnatin shugaba Salva Kiir ta kame wasu ministoci biyu da wasu manyan jami’an soji da ke kawance da mataimakin shugaban kasar na farko Riek Machar. Tuni dai aka saki minista guda.

Kamen da aka yi a Juba da kuma kazamin fadan da ya barke a kusa da garin Nasir na arewacin kasar ana ganin zai kawo cikas ga yarjejeniyar zaman lafiya ta shekarar 2018 da ta kawo karshen yakin basasa na tsawon shekaru biyar tsakanin dakarun da ke biyayya ga Kiir da Machar inda aka kashe kusan mutane 400,000.

Bayan barkewar yakin basasa a Sudan ta Kudu a shekara ta 2013, Uganda ta aike da dakarunta zuwa Juba domin tallafawa dakarun Kiir da ke yaki da Machar. Daga karshe dai sojojin Uganda sun janye a shekarar 2015. An sake tura sojojin Uganda zuwa Juba a shekara ta 2016 bayan da aka sake gwabza fada tsakanin bangarorin biyu, amma kuma aka janye su daga bisani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Yanzu haka ana shirye-shiryen gudanar da taron kasa da kasa na tattauna batutuwan raya tattalin arziki na Davos na yanayin zafi karo na 16, taron da aka fi sani da dandalin Davos. A bana za a gudanar da taron ne tsakanin ranakun Talata 24 zuwa Alhamis 26 ga watan nan na Yuni, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin, bisa taken “sana’o’i a sabon zamani.”

A bana taron zai mayar da hankali ne ga muhimman fannoni biyar, wadanda suka hada da warware batu game da tattalin arzikin duniya, da hange game da kasar Sin, da halin da masana’antun duniya suka fuskanta na taka musu birki, da zuba jari kan al’umma da duniyar bil’adama da batun sabbin makamashi da hajoji.

Game da hakan, jami’i a hukumar tsara manufofin ci gaba da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin Chen Shuai, ya ce Sin za ta yi amfani da taron na Davos na bana, wajen jaddada aniyarta, ta ci gaba da kwazo don cimma nasarar bude kofa bisa matsayin koli, da rarraba damammakinta na ci gaba da ta samu tare da sauran sassan kasa da kasa.

A nata bangare kuwa, Gim Huay Neo, babbar daraktar dandalin tattalin arziki na duniya, ta shaidawa wani taron menema labarai da ya gudana a baya bayan nan cewa, daya daga cikin yankunan duniya mafiya samun sauye-sauye a duniya shi ne nahiyar Asiya, nahiyar da ke kunshe da kaso 60 bisa dari na ci gaban tattalin arzikin duniya, kuma cikin wannan adadi kasar Sin ita kadai na bayar da gudummawar rabin kason ci gaban nahiyar. Jami’ar ta kara da cewa, dandalin Davos na bana zai samar da zarafi ga mahalartansa, na zurfafa fahimtarsu ga salon ci gaban Sin da sauran sassan Asiya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
  • An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya
  • Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
  • Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
  • Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin
  • Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a Columbia
  • Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba