’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan
Published: 12th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da daruruwan fasinjoji a ranar Talata a wani yunkurin ci gaba da ta da hankali da wata kungiyar ’yan aware ke yi a Kudu maso yammacin Pakistan.
’Yan bindigar sun raunata direban jirgin kasan a kokarinsu na kwace iko da jirgin a yankin Balochistan mai duwatsu da ke iyaka da Afghanistan da kuma Iran.
Wani babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin sufurin jiragen kasa Muhammad Kashif ya shaida wa AFP cewa adadin mutane da aka yi garkuwa da su ya kai 450.
Sai dai kuma shafin jaridar rnz na intanet ya ruwaito cewa, daga bisani an kubutar da akalla fasinjoji 100 yayin da ajali ya katse hanzarin wasu uku a yayin harin da ya auku a kudu maso gabashin Balochistan.
Kungiyar Baloch Liberation Army (BLA) mai yunkurin neman cin gashin kan yankin Balochistan, ta dauki alhakin garkuwar baya ga zargin hukumomi da mamaye arzikin yankin.
Kungiyar dai BLA ta dade ta na tayar da zaune tsaye a Pakistan kuma ta na ikirarin a bar mata yankunanta don rike madafun iko.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Hamsa: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjeniyar Tsagaita Bude Wuta A Yankin
Kungiyar Hamas wace take iko da zirin Gaza ta yi allawadai da HKI kan rashin cika alkawulan da ta dauka a yarjeniyar da ta kulla a kungiyar da kuma masu shiga tsakani a gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Abduljabbar Saeed mamba a bagaren siyasa na kungiyar yana fadar haka a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta ‘Quds New a jiya Laraba . Ya kumakara da cewa HKI kasashe masu shiga tsakani sun tabbatar da cewa HKI bata cika alkawulan da ta dauka a kashi na farko na yarjeniyar tsagaita wuta ba.
Yace gwamnatin Amurka ta yi mamakin yadda kungiyar ta cika dukkan alkawulan da ta dauka a kasha farko na yarjeniyar tsagaita wutan . Musamman mika dukkan gawakin yahudawan da suka halaka gaza.
Amma ya ce a dayan bangaren HKI ta ci gaba da kashe Falasdinawa fararen hula hatta bayana tsagaita wuta, sun hana shigar kayakin agaji cikin yankin, sun bar falasdinawa cikin ruwa sama, saboda sun hana shigo da kayakin agaji wadanda suka hada da tantuna da gidajen tafi da gidanka da sauransu.
Sun hana shigo da manya-manya motoci don kwace burbushin ginene, sun hana sake gina gza sun hatta abinci asasshe ga mutanen gaza. A cikin wannan halin ta yaya zasu yi maganar sashe na biyu. Sannan dangane da kwance damarar dakarun Hamas Abduljabbar ya bayyana cewa makaman Hamas suna tare da kafuwar daular Falasdinu ne matukar ba’a kafa kasar Falasadinu mai cikekken yenci babu randa hamasa zata mika makamanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci