Aminiya:
2025-06-30@22:48:09 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan

Published: 12th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da daruruwan fasinjoji a ranar Talata a wani yunkurin ci gaba da ta da hankali da wata kungiyar ’yan aware ke yi a Kudu maso yammacin Pakistan.

’Yan bindigar sun raunata direban jirgin kasan a kokarinsu na kwace iko da jirgin a yankin Balochistan mai duwatsu da ke iyaka da Afghanistan da kuma Iran.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa

Wani babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin sufurin jiragen kasa Muhammad Kashif ya shaida wa AFP cewa adadin mutane da aka yi garkuwa da su ya kai 450.

Sai dai kuma shafin jaridar rnz na intanet ya ruwaito cewa, daga bisani an kubutar da akalla fasinjoji 100 yayin da ajali ya katse hanzarin wasu uku a yayin harin da ya auku a kudu maso gabashin Balochistan.

Kungiyar Baloch Liberation Army (BLA) mai yunkurin neman cin gashin kan yankin Balochistan, ta dauki alhakin garkuwar baya ga zargin hukumomi da mamaye arzikin yankin.

Kungiyar dai BLA ta dade ta na tayar da zaune tsaye a Pakistan kuma ta na ikirarin a bar mata yankunanta don rike madafun iko.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira ga mazauna wani kauyen dake yankin Nyingchi na jihar Xizang mai cin gashin kai, da su rungumi akidar ‘yan uwantakar kabilarsu, da samar da yanayin gudanar da rayuwa mai kyau.

Shugaba Xi ya yi kiran ne cikin wasikar da ya mayar ga mazauna kauyen, wadda a ciki ya bayyana fatansa gare su, bayan da ya ziyarci kauyen cikin watan Yulin shekarar 2021. Ya ce, bayan fahimtar cewa kauyen ya samu sabbin sauye-sauye a shekarun baya-bayan nan, kuma mazaunansa sun samu karin kudaden shiga, ya yi matukar farin ciki.

Shugaba Xi ya kara da cewa, yana fatan karkashin manufofin JKS, mazauna kauyen za su gina yankunan kan iyakoki, tare da kyautata rayuwar al’ummunsu yadda ya kamata, kana za su zage damtse wajen kare kyakkyawan yanayin tuddan yankin, da raya sunan kauyen ta fuskar yawon bude ido, da bayar da gudummawa ga gina yankin kan iyaka mai wadata da daidaito.

Kauyen dai ya shahara sosai a fannin noman itacen Peach. A shekarun baya-bayan nan, ya cimma sabbin nasarori a fannin bunkasa sha’anin yawon bude ido na kauyuka, da karfafa sassan tattalin arziki, da ingiza ‘yan uwantakar kabila. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  •  Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
  • Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
  • Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
  • Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba