’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan
Published: 12th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da daruruwan fasinjoji a ranar Talata a wani yunkurin ci gaba da ta da hankali da wata kungiyar ’yan aware ke yi a Kudu maso yammacin Pakistan.
’Yan bindigar sun raunata direban jirgin kasan a kokarinsu na kwace iko da jirgin a yankin Balochistan mai duwatsu da ke iyaka da Afghanistan da kuma Iran.
Wani babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin sufurin jiragen kasa Muhammad Kashif ya shaida wa AFP cewa adadin mutane da aka yi garkuwa da su ya kai 450.
Sai dai kuma shafin jaridar rnz na intanet ya ruwaito cewa, daga bisani an kubutar da akalla fasinjoji 100 yayin da ajali ya katse hanzarin wasu uku a yayin harin da ya auku a kudu maso gabashin Balochistan.
Kungiyar Baloch Liberation Army (BLA) mai yunkurin neman cin gashin kan yankin Balochistan, ta dauki alhakin garkuwar baya ga zargin hukumomi da mamaye arzikin yankin.
Kungiyar dai BLA ta dade ta na tayar da zaune tsaye a Pakistan kuma ta na ikirarin a bar mata yankunanta don rike madafun iko.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da bikin makon shari’a na shekarar 2025 wanda ƙungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA) reshen jihar Jigawa ya shirya, inda ya yi kira da a ƙara ƙarfafa bin ƙa’idojin aikin shari’a da hanzarta gudanar da shari’a a duk fadin jihar.
A jawabinsa wajen bikin bude taron a Dutse, Gwamna Namadi ya yaba wa shugabannin NBA bisa hadin kai da kwarewarsu wajen gudanar da aiki.
“Na shafe watanni da dama ina bin diddigi da sha’awar yadda kuka kafa, tare da gudanar da ayyukan kungiyar reshen jihar, cikin haɗin kai da ƙarfafawa, inda ya zama wata gagarumar kafa wacce ke kare muradun aikin lauya da mambobin ƙungiyar a Jigawa ma da wajen ta.” In ji shi.
“Na yaba ƙoƙarinku na ganin yadda NBA reshen jihar ta samu nasara wajen inganta manufofi da ƙa’idojin da aka san ƙungiyar da su—wato kare doka, tabbatar da samun adalci ga kowa, ciki har da talakawa, da kuma tabbatar da gudanar da shari’a cikin sauƙi a jihar Jigawa.
“Baya ga hulɗar aiki da zamantakewa, abin farin ciki ne ganin yadda irin waɗannan taruka ke taimaka wa wajen inganta bin ƙa’idojin aikin lauya da kuma ƙarfafa tattaunawa, ba kawai tsakanin lauyoyi ba, har ma da sauran muhimman masu ruwa da tsaki a harkar shari’a.”
Yayin bayyana gyare-gyaren gwamnatinsa a bangaren shari’a, Gwamna Namadi ya ambaci shirye-shiryen da suka haɗa da kafa Cibiyoyin Doka na Al’umma, gabatar da Zauren Sulhu, shirye-shiryen faɗaɗa Sashen Kare Haƙƙin Ɗan Kasa a kowace kotu, da sauran muhimman tsare-tsare.
Ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su yi aikinsu bisa gaskiya da rikon amana.
Ya bayyana fatan cewa tattaunawar za ta bayar da gagarumar gudummawa wajen kare ƙa’idojin aikin lauya da kuma inganta gudanar da shari’a a jihar Jigawa.
Usman Mohammad Zaria