’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan
Published: 12th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da daruruwan fasinjoji a ranar Talata a wani yunkurin ci gaba da ta da hankali da wata kungiyar ’yan aware ke yi a Kudu maso yammacin Pakistan.
’Yan bindigar sun raunata direban jirgin kasan a kokarinsu na kwace iko da jirgin a yankin Balochistan mai duwatsu da ke iyaka da Afghanistan da kuma Iran.
Wani babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin sufurin jiragen kasa Muhammad Kashif ya shaida wa AFP cewa adadin mutane da aka yi garkuwa da su ya kai 450.
Sai dai kuma shafin jaridar rnz na intanet ya ruwaito cewa, daga bisani an kubutar da akalla fasinjoji 100 yayin da ajali ya katse hanzarin wasu uku a yayin harin da ya auku a kudu maso gabashin Balochistan.
Kungiyar Baloch Liberation Army (BLA) mai yunkurin neman cin gashin kan yankin Balochistan, ta dauki alhakin garkuwar baya ga zargin hukumomi da mamaye arzikin yankin.
Kungiyar dai BLA ta dade ta na tayar da zaune tsaye a Pakistan kuma ta na ikirarin a bar mata yankunanta don rike madafun iko.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba wa rundunar sojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa daƙile hare-haren ’yan bindiga a wasu sassan jihar.
Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.
Kocin Super Eagle ya lashi takobin lashe kofin nahiyar Afirka Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na AmurkaAbba ya yi wannan yabo ne, yayin da yake karɓar babban kwamandan rundunar soji ta 1, a Hedikwatar Kaduna, Manjo Janar Abubakar Sadiq Muhammad Wase, a fadar gwamnati da ke Kano.
Manjo Janar Wase, ya ziyarci Kano domin duba halin tsaro a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa.
Ya bayyana yadda mahaifinsa, marigayi Kanal Muhammad Abdullahi Wase, ya taɓa zama kwamishinan soja na Jihar Kano a shekarar 1994.
“Tun lokacin da na karɓi jagorancin rundunar, na ziyarci wuraren da aka kai hare-hare domin na yaba wa jarumtar sojojimmu,” in ji Janar Wase.
Gwamnan ya gode wa sojoji bisa jajircewarsu, tare da jinjina wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan naɗa sabbin hafsoshin tsaro masu ƙwazo da kishin ƙasa.
Ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta bayar da kyautar motoci ƙirar Hilux guda 10 da babura 60 ga rundunar haɗin gwiwa da ke aiki a yankunan da abin ya shafa.
Haka kuma ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu.
Idan ba a manta Aminiya ta ruwaito yadda dakarun soji suka daƙile hari tare da kashe ’yan bindiga 19 a yankin Shanono yayin wani samame da suka kai.