’Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji 450 a Pakistan
Published: 12th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da daruruwan fasinjoji a ranar Talata a wani yunkurin ci gaba da ta da hankali da wata kungiyar ’yan aware ke yi a Kudu maso yammacin Pakistan.
’Yan bindigar sun raunata direban jirgin kasan a kokarinsu na kwace iko da jirgin a yankin Balochistan mai duwatsu da ke iyaka da Afghanistan da kuma Iran.
Wani babban jami’in gwamnati mai kula da harkokin sufurin jiragen kasa Muhammad Kashif ya shaida wa AFP cewa adadin mutane da aka yi garkuwa da su ya kai 450.
Sai dai kuma shafin jaridar rnz na intanet ya ruwaito cewa, daga bisani an kubutar da akalla fasinjoji 100 yayin da ajali ya katse hanzarin wasu uku a yayin harin da ya auku a kudu maso gabashin Balochistan.
Kungiyar Baloch Liberation Army (BLA) mai yunkurin neman cin gashin kan yankin Balochistan, ta dauki alhakin garkuwar baya ga zargin hukumomi da mamaye arzikin yankin.
Kungiyar dai BLA ta dade ta na tayar da zaune tsaye a Pakistan kuma ta na ikirarin a bar mata yankunanta don rike madafun iko.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
Cibiyar Blue Sapphire ta kaddamar da wani shiri na musamman da aka kirkiro domin ƙarfafa gwiwar mata ’yan kasuwa a fannin dinkin kayan sawa da kuma harkokin kirkira a arewa maso yammacin Najeriya.
Cibiyar na aiwatar da wannan shiri ne tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar ’Yan Kasuwa Mata ta Arewa (ANWE) da Jami’ar Northwest Kano, tare da tallafin Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU).
Dukiyar sama da miliyan 500 ta kone a gobarar kasuwar katako ta Gombe ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’Da take jawabi a wajen kaddamarwar a Kano ranar Talata, shugabar cibiyar, Maryam Lawan Gwadabe, ta ce an kirkiro shirin ne domin samar wa mata amintaccen muhallin da za su yi amfani da shi wajen bunƙasa kasuwancinsu.
Ta ce shirin zai gudana a jihohin Kano, Katsina da Sakkwato domin ƙarfafa tattalin arzikin mata da kuma tabbatar da sun samu dogaro da kai.
“Mun sanya wa shirin suna Women Venture Studio domin tabbatar da cewa mata za su ji daɗin kasancewa a cikin muhalli mai tsaro. Masu ba da shawara a nan su ne ’yan kasuwa da matan da suka yi nasara, waɗanda za su saurara, su jagoranta, kuma su tallafa wa mahalarta shirin,” in ji ta.
Maryam ta ƙara da cewa cibiyar tana bayar da wuraren yin aiki na zahiri da na intanet, domin tabbatar da cewa ana damawa da mat aba tare da an ware su ba.
Shugabar cibiyar ta kuma ce matakin farko na shirin zai haɗa da horar da mata 150, wato mata 50 daga kowacce jiha.
Ita ma da take jawabi, Shugabar ANWE, Hafsat Sahabi Dange, ta ce shirin ya fi mayar da hankali kan mata a fannin kirkira, musamman a harkar dinka kaya, sana’o’in hannu da fasaha.
“Manufarmu ita ce mu sauya waɗannan kasuwancin zuwa tsarin zamani domin mata su iya yin gogayya, ba kawai a Najeriya ba, har ma a duniya. Wannan shiri zai shafi ’ya’ya mata da kuma mata ta hanyar amfani da kirkirarsu da kuma ƙarfafa musu tsarin kasuwanci a Arewacin Najeriya,” in ji ta.
A nata bangaren, wakiliyar Tarayyar Turai a Najeriya da ECOWAS, Inga Stefanovic, ta ce EU ta ware sama da Yuro miliyan 700 a matsayin tallafi domin tallafa wa ayyuka daban-daban a fadin Najeriya.
Ta jaddada cewa haɗin gwiwar EU da Najeriya ya shafi fannoni da dama ciki har da fasahar zamani, bunkasa tattalin arziki, dimokuraɗiyya, zaman lafiya da tsaro, lafiya, ilimi, samar da makamashi da kuma noma.