Matsin Amurka Ya Zama Zaburarwa Ga Kasar Sin Wajen Kara Samun Ci Gaba
Published: 12th, March 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta soki kalaman sakataren baitul-malin Amurka da ya bayyana dangantakar tattalin arziki dake tsakanin kasashen biyu a matsayin zamba.
An shafe gomman shekaru ana huldar cinikayya tsakanin bangarorin biyu, a gani na, idan har akwai zamba a ciki, ba na jin huldar za ta kawo matakin da take kai a yanzu.
Abun da ya kamata Amurka da kawayenta su gane shi ne, kasar Sin ta fi mayar da hankali kan habaka bukatun cikin gida domin karfafa tattalin arzikinta maimakon dogaro da kasashen waje. Matsin da Amurka ta dade tana yi wa kasar Sin, ya kara tabbatar da cewa, tattalin arzikin Sin ba ya dogaro da kasashen waje, bisa la’akari da yadda matsin bai sa tattalin arzikin ya durkushe ba, maimakon haka, ya zama wani karin zaburarwa ga kasar Sin ta nacewa ga habaka bukatun cikin gida da kirkire-kirkire, domin biyan bukatunta da na sauran kasashe duniya.
Yayin gabatar da rahoton aikin gwamnati ga majalisar dokokin kasa a makon jiya, firaministan Sin Li Qiang ya ce kasar na da burin habaka tattalin arzikinta da kaso 5 cikin dari a bana, lamarin da ya ja hankalin duniya matuka. Hakika wannan buri da ta sanya gaba, ya kara bayyanawa duniya kwarin tubalin tattalin arzikinta da kuma irin ci gaba da za ta samu. Har kullum na kan ce, ci gaban kasar Sin, ci gaba ne ga duniya baki daya. A matsayinta na babbar abokiyar cinikayya ta kasa da kasa, kuma cibiyar kirkire-kirkire a duniya, kana mai bayar da gudummawar kaso 1 bisa 3 na ci gaban tattalin arzikin duniya, karuwar tattalin arziki da ci gaban Sin babbar dama ce kuma abun murna ga kasashe musamman masu tasowa. (Faeza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
Iran ta sanar da soke zaman tattaunawa da ya kamata ta yi da Amurka kan batun nikiliyarta a Oman yau Lahadi saka makon hare-haren da Isra’ila ta kai mata a ranar Juma’a.
Bayanai sun ce a wannan Lahadin ce ya kamata a gudanar da ganawa ta shida tsakanin wakilan Amurka da na Iran a birnin Musqat na Oman.
Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a BenuweSai dai kakakin Ministan harkokin wajen Iran, Esmaeil Baqaei ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, Amurka ta nuna fuska biyu, inda a gefe guda take tattaunawar cimma masalahar jingine ƙera nukiliya da Iran, amma a ɗaya gefen kuma ta goyi bayan harin da Isra’ila ta kai mata.
Iran ta zargi Amurka da goyon bayan harin da Isra’ila ta kai mata, sannan kuma ta ce tattaunawar yarjejeniyar dakatar da ƙera makamin ƙare dangi na nukiliya da take yi da Amurkar ba ta da wani amfani.
A nasa ɓangaren, Ministan harakokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce babu buƙatar ci gaba da tattaunawa da aka faro tsakiyar watan Afirilun wannan shekara lura da harin dabbanci da Isra’ila ta kai mata.
Kafofin yaɗa labarai da dama a Iran sun shaida cewa guda daga cikin masu baiwa jagoran addinin musluncin Iran ayatoAllah Ali Khamenei kuma mai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar, Ali Shamkhani, na daga cikin waɗanda su ka ji rauni a hare-haren na Isra’ila.
Tun farko Isra’ila ce ta fara kai wa Iran hari kan cibiyoyin nukiliyarta tare da halaka manyan hafsoshin tsaronta, cikin daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a, kuma ta ci gaba da kai farmaki da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, mafarin buɗe kofar wani sabon rikici a tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna adawa da juna tsawon shekaru.
Harin ramuwar gayya da Iran ta kai wa Isra’ila da safiyar Asabar ya halaka mutane uku, tare da jikkata wasu da dama a biranen Jerusalem da Tel Aviv, inda hukumomin Isra’ila ke ci gaba da gargaɗin ‘yan kasar su nemi mafaka.
A wani jawabi da jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gabatarwa al’ummar kasar ranar Juma’a, ya ce ba za su saurara wa Isra’ila ba sakamakon munin abin da ta aikata musu.