Matsin Amurka Ya Zama Zaburarwa Ga Kasar Sin Wajen Kara Samun Ci Gaba
Published: 12th, March 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta soki kalaman sakataren baitul-malin Amurka da ya bayyana dangantakar tattalin arziki dake tsakanin kasashen biyu a matsayin zamba.
An shafe gomman shekaru ana huldar cinikayya tsakanin bangarorin biyu, a gani na, idan har akwai zamba a ciki, ba na jin huldar za ta kawo matakin da take kai a yanzu.
Abun da ya kamata Amurka da kawayenta su gane shi ne, kasar Sin ta fi mayar da hankali kan habaka bukatun cikin gida domin karfafa tattalin arzikinta maimakon dogaro da kasashen waje. Matsin da Amurka ta dade tana yi wa kasar Sin, ya kara tabbatar da cewa, tattalin arzikin Sin ba ya dogaro da kasashen waje, bisa la’akari da yadda matsin bai sa tattalin arzikin ya durkushe ba, maimakon haka, ya zama wani karin zaburarwa ga kasar Sin ta nacewa ga habaka bukatun cikin gida da kirkire-kirkire, domin biyan bukatunta da na sauran kasashe duniya.
Yayin gabatar da rahoton aikin gwamnati ga majalisar dokokin kasa a makon jiya, firaministan Sin Li Qiang ya ce kasar na da burin habaka tattalin arzikinta da kaso 5 cikin dari a bana, lamarin da ya ja hankalin duniya matuka. Hakika wannan buri da ta sanya gaba, ya kara bayyanawa duniya kwarin tubalin tattalin arzikinta da kuma irin ci gaba da za ta samu. Har kullum na kan ce, ci gaban kasar Sin, ci gaba ne ga duniya baki daya. A matsayinta na babbar abokiyar cinikayya ta kasa da kasa, kuma cibiyar kirkire-kirkire a duniya, kana mai bayar da gudummawar kaso 1 bisa 3 na ci gaban tattalin arzikin duniya, karuwar tattalin arziki da ci gaban Sin babbar dama ce kuma abun murna ga kasashe musamman masu tasowa. (Faeza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta samu ci gaba sosai wajen magance matsalar rashin tsaro a faɗin ƙasar cikin shekaru biyu da suka gabata.
Shugaban ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na daƙile ayyukan ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiyar ƙasa.
Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masaiA wata sanarwa da Tinubu ya fitar a shafinsa na sada zumunta, a ranar Juma’a, ya ce ƙalubalen tsaro a Najeriya, da suka haɗa da ta’addanci da aikata laifuka, ana magance su da sabbin tsari da sauye-sauyen dabarun dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.
“Haƙiƙa muna fuskantar ta’addanci – ƙalubalen da Najeriya ta fuskanta kusan shekaru ashirin, kuma ba za mu ja da baya ba, za mu yi nasara a kan ta’addanci kuma mu yi iƙirarin samun nasara a wannan yaƙin, ba za mu taɓa yin sulhu harkar tsaro ba.
“Najeriya ƙasa ɗaya ce mai haɗin kai, mun tashi tare, mun ci gaba tare, kuma mun ƙi yanke ƙauna domin tabbatar da ƙuduri.
“Aikin da ke gabanmu yana da yawa, amma duk da haka ƙudurinmu ya fi girma, za mu ci gaba da ɗorewa tare da inganta nasarorin da muka samu na sake fasalin ƙasa da kuma samar da ci gaba a Najeriya.
“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba kuma ba za mu bar wani abu ba a cikin aikinmu na kawar da masu aikata laifuka a cikin al’ummarmu, muna kira ga abokan haɗin gwiwarmu da su tsaya tsayin daka tare da mu yayin da muke ƙara faɗaɗa yaƙin da muke yi da ta’addanci, mun samu gagarumin ci gaba a cikin shekaru biyu da suka gabata, kuma za mu kawar da wannan barazana.”