Matsin Amurka Ya Zama Zaburarwa Ga Kasar Sin Wajen Kara Samun Ci Gaba
Published: 12th, March 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta soki kalaman sakataren baitul-malin Amurka da ya bayyana dangantakar tattalin arziki dake tsakanin kasashen biyu a matsayin zamba.
An shafe gomman shekaru ana huldar cinikayya tsakanin bangarorin biyu, a gani na, idan har akwai zamba a ciki, ba na jin huldar za ta kawo matakin da take kai a yanzu.
Abun da ya kamata Amurka da kawayenta su gane shi ne, kasar Sin ta fi mayar da hankali kan habaka bukatun cikin gida domin karfafa tattalin arzikinta maimakon dogaro da kasashen waje. Matsin da Amurka ta dade tana yi wa kasar Sin, ya kara tabbatar da cewa, tattalin arzikin Sin ba ya dogaro da kasashen waje, bisa la’akari da yadda matsin bai sa tattalin arzikin ya durkushe ba, maimakon haka, ya zama wani karin zaburarwa ga kasar Sin ta nacewa ga habaka bukatun cikin gida da kirkire-kirkire, domin biyan bukatunta da na sauran kasashe duniya.
Yayin gabatar da rahoton aikin gwamnati ga majalisar dokokin kasa a makon jiya, firaministan Sin Li Qiang ya ce kasar na da burin habaka tattalin arzikinta da kaso 5 cikin dari a bana, lamarin da ya ja hankalin duniya matuka. Hakika wannan buri da ta sanya gaba, ya kara bayyanawa duniya kwarin tubalin tattalin arzikinta da kuma irin ci gaba da za ta samu. Har kullum na kan ce, ci gaban kasar Sin, ci gaba ne ga duniya baki daya. A matsayinta na babbar abokiyar cinikayya ta kasa da kasa, kuma cibiyar kirkire-kirkire a duniya, kana mai bayar da gudummawar kaso 1 bisa 3 na ci gaban tattalin arzikin duniya, karuwar tattalin arziki da ci gaban Sin babbar dama ce kuma abun murna ga kasashe musamman masu tasowa. (Faeza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
Ministan harkokin cikin gidan kasar Venezuela ya bayyana cewa al’ummar Venezuela ba ta tsoron barazanar da Amurka take yi ma ta, domin juyin juya halin kasar zai ci gaba, kuma azamar al’umma ce za ta yi nasara a gaban masu wuce gona da iri.
Ministan harkokin cikin gidan kasar ta Venezuela Diosdado Cabello Rondón wanda kuma shi ne sakataren jam’iyyar gurguzu ta kasar, ya ce a halin yanzu juyin juya halin kasar yana fuskatar gwagwarmaya ce wacce ba ta makami domin fuskantar matsin lamba na kowace rana daga Amurka.
Ministan harkokin cikin gidan kasar ta Venezuela wanda ya halarci bikin rantsar da sabbin shugabannin al’umma a jihar Monagas ya yi Ishara da yadda Amurka ta girke jiragen yaki a ruwa kasa da Venezuela, da kuma jiragen yaki na sama, ba don komai ba,sai kokarin tilastawa al’ummar Venezuela su mika ma ta wuya ta hanyar tsoratarwa.
Haka nan kuma ya jaddada cewa, abinda Amurkan take yi ba zai harfar ma ta Da, mai ido ba; domin ba su da masaniya akan cewa al’ummar kasar ba su tsoron wani abu ba.
Haka nan kuma ministan harkokin cikin gidan kasar ta Venezuela ya ce, babu wani abu da al’ummar kasar suke tsoro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Zama Zakaran Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025 Dubban Mutane Suna Guduwa Daga Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025 Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci