Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet
Published: 11th, March 2025 GMT
Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.
Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.
Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.
Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.
Sauran sun haɗa da Enugu da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.
NiMet ta ce wasu jihohin da ka iya fuskantar wannan barazana sun hada da Taraba da Adamawa da Filato da Kaduna da Zamfara da kuma Sakkwato.
Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zafin rana
এছাড়াও পড়ুন:
Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
Sheikh Ahmad Gumi ya yi martani kan kiraye-kirayen da ake yi na kama shi, inda ya ce masu yin kiran na yi ne domin kawar da rawar da yake takawa wajen magance matsalar ’yan bindiga a Arewa.
Gumi, ya ce duk ganawar da yake yi da ’yan bindiga yana yi ne domin samar da zaman lafiya, kuma hukumomin tsaro sun san da komai.
Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — AkpabioMaganar ta sake fitowa fili ne bayan da ya sake jaddada cewa tattaunawa hanya ce da za ta iya kawo ƙarshen tashin hankali a karkara.
A cikin dogon saƙon da ya wallafa a Facebook a ranar Lahadi, Gumi ya soki masu cewa ya kamata a kama shi saboda ya ganawar da ya yi da shugabannin ’yan bindiga.
Ya bayyana kiran a matsayin don rai la’akari da irin ƙoƙarin da ya yi a baya domin daƙile matsalar tsaro a Arewa.
Ya ce ba shi niyyar goyon bayan masu laifi; kawai yana ƙoƙari rage tashin hankali da kuma shawo kan ’yan bindiga su miƙa wuya.
Gumi, ya ce ya yi muhimmin zama da mahara a Janairun 2021 a dajin Sabon Garin Yadi da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.
Kuma ya ce tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna ya je a lokacin d aka yi ganawar, wanda ya wakilci Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa.
Ya ce taron ya samu halartar ’yan bindiga da shugabanninsu sama da 600, kuma sun yi alƙawarin daina kai hare-hare idan gwamnati ta samar musu da wasu muhimman abubuwa.
“Na je dajin Sabon Garin Yadi tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna.”
“Wannan zama ɓangare ne na aikin samar da zaman lafiya, inda muka yi wa ’yan bindiga sama da 600 da shugabanninsu wa’azi, suka kuma amince za su ajiye makamai idan gwamnati ta samar musu da tsaro da ingantaccen rayuwa,” in ji shi.
Gumi, ya ce duk abin da ya yi bisa ƙa’ida ya yi sa, kuma hukumomi sun san da komai.
Ya ce maimakon mutane su kai su soke shi, kamata ya yi su tambayi dalilin da ya sa gwamnati ba ta yi buƙatun ’yan bindiga ba.
Sheikh Gumi ya kuma tambayi dalilin da ya sa wasu ke son a kama shi, alhali manufarsa ita ce kawo ƙarshen tashin hankali a Najeriya.
“To me zai sa kama ni? Domin na yi kira su ajiye makamai… ko saboda na faɗakar da al’umma game da labarin ’yan bindiga?”.
Gumi ya zargi masu sukarsa da nuna wariya, inda ya tunatar da su cewa kundin tsarin mulki ya bai wa kowa damar faɗin albarkacin bakinsa.
“Shin faɗin ra’ayi ba haƙƙinmu ba ne na kundin tsarin mulki ba? Shin kira da suke yi na a kama ni ba nuna son rai ba ne kuma zai iya haifar da tashin hankali?”.
Ya bayyana cewa buƙatun ’yan bindigar suka nema waɗanda suka haɗa da ababen more rayuwa, kariya daga kame ba bisa ƙa’ida ba, da hanankai musu hari ba idan sun miƙa wuya.
Ya ce babu ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan da aka aiwatar, wanda hakan ya wargatsa tattaunawar.
Gumi, ya ce kamata ya yi mutane su mayar da hankali kan mafita a aikace, ba zagi da fushi ba.