Aminiya:
2025-11-24@17:54:00 GMT

Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Published: 11th, March 2025 GMT

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.

Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.

Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.

Sauran sun haɗa da Enugu da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.

NiMet ta ce wasu jihohin da ka iya fuskantar wannan barazana sun hada da Taraba da Adamawa da Filato da Kaduna da Zamfara da kuma Sakkwato.

Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zafin rana

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewar an ceto dukkanin mutanen da mahara suka sace a wata coci a yankin Eruku na Jihar Kwara.

’Yan bindigar sun sace masu ibadar ne a ranar Talata, lokacin da suka kai hari cocin Christ Apostolic Church (CAC) da ke Oke Isegun a Eruku, wani gari da ke iyaka da Kogi a Karamar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

ISWAP ta sace ’yan mata 13 a Borno Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji

A cikin wani sako da Tinubu ya wallafa a X a ranar Lahadi, ya ce yana bibiyar yanayin tsaro a fadin kasar nan, kuma zai tabbatar da cewa gwamnatinsa ta kare ’yan Najeriya.

An yada bidiyon yadda maharan suka shiga cocin suka yi awon gaba da masu ibada yayin da suke tsaka da addu’a.

Lokacin da maharan suka dinga harbe-harbe a ciki cocin, wani Fasto ya jagoranci jama’a inda suka nemi mafaka.

Ya kuma ce an ceto dalibai 51 da aka sace a Jihar Neja.

Tinubu ya kara da cewa: “’Yan uwana ’yan Najeriya, za ku iya tuna cewa na soke zuwa taron G20 da aka yi a Afirka ta Kudu domin na mayar da hankali kan sha’anin tsaro a gida.

“Ina yi wa jami’an tsaro godiya kan aiki tukuru da suka cikin kwanaki biyun da suka wuce, an ceto dukkanin masu ibada 38 da aka sace a Eruku, a Jihar Kwara.

“Ina kuma farin ciki cewa an gano dalibai 51 daga cikin wadanda aka sace a wata makaranta a Jihar Neja.

“Ina bibiyar sha’anin tsaro sosai kuma ina samun rahotanni kai-tsaye. Ba zan yi kasa a gwiwa ba. Kowane dan Najeriya yana da ’yancin samun tsaro, kuma a karkashin jagorancina, za mu kare wannan kasa da mutanen ciki.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • An rufe duk makarantu a Kebbi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu
  •  Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 160