Aminiya:
2025-11-11@19:55:32 GMT

Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Published: 11th, March 2025 GMT

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.

Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.

Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.

Sauran sun haɗa da Enugu da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.

NiMet ta ce wasu jihohin da ka iya fuskantar wannan barazana sun hada da Taraba da Adamawa da Filato da Kaduna da Zamfara da kuma Sakkwato.

Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zafin rana

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata duk ɗan Najeriya ya damu da barazanar Trump– Jigon APC

Wani jigo a Jam’iyyar APC a Jihar Osun, Olatunbosun Oyintiloye, ya ce ya kamata kowane ɗan Najeriya ya damu game da barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu da hukumomin tsaro bisa ƙoƙarinsu na yaƙar rashin tsaro, tare da kiran ’yan Najeriya da su haɗa kai don kare ƙasar.

Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga ’Yan bindiga sun kashe kansila yayin Zaɓen Gwamnan Anambra

Oyintiloye, ya ce matsalar tsaro ba a zamanin Tinubu ta samo asali ba, kuma a cewarsa matsalar na shafar addinai daban-daban a ƙasar.

“Dole ne mu tsaya tare da Shugaba Tinubu. Wannan ba lokacin rabuwar addini ko siyasa ba ne. Abin da muke buƙata yanzu shi ne haɗin kai don kare ƙasarmu,” in ji shi.

Ya shawarci ’yan adawa da su yi hattara da kalamansu, tare da kira ga manyan hafsoshin soji da su tabbatar da amincewar da aka ba su ta hanyar yin aiki tuƙuru wajen murƙushe ’yan ta’adda.

Oyintiloye, ya kuma roƙi gwamnatin Amurka da ta taimaka wa Najeriya da bayanan leƙen asiri da kayan yaƙi maimakon turo sojojinta, inda ya ce hakan na iya ƙara dagula lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan ta’adda na kafa doka da karɓar haraji a Arewa — Dambazau
  • An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
  • An sake rage kuɗin aikin Hajjin 2026 a Najeriya
  • Yarin Fika ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC a Yobe
  • Yarin Fika ya sauya sheƙa PDP zuwa APC a Yobe
  • Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa
  • Gwamna Kebbi ya gargaɗi manoma da makiyaya kan su zauna lafiya ko su fuskanci hukunci
  • Ya kamata duk ɗan Najeriya ya damu da barazanar Trump– Jigon APC
  • Wasu Kasashe Takwas Sun Bukaci Ganin An kama Benjamine Netanyahu
  • Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza