Aminiya:
2025-12-02@20:22:29 GMT

Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Published: 11th, March 2025 GMT

Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki huɗu.

Wata sanarwa da Nimet ta fitar ranar Litinin a Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3.

Ainihin abin da ke kawo wa Manchester United koma baya ‘Yarjejeniyar sayar wa Matatar Dangote ɗanyen mai a farashin naira za ta ƙare a ƙarshen Maris’

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

Jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa da Neja da Kwara da Oyo da Kogi da Nasarawa da kuma Benue.

Sauran sun haɗa da Enugu da Anambra da Abia da Ebonyi da Cross River da birnin tarayya Abuja.

NiMet ta ce wasu jihohin da ka iya fuskantar wannan barazana sun hada da Taraba da Adamawa da Filato da Kaduna da Zamfara da kuma Sakkwato.

Ta kuma shawarci al’umma da su riƙa shan isasshen ruwa a tsawon lokacin – su kuma yi amfani da fanka da na’urar sanyaya ɗaki da kuma zama a wurare masu inuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zafin rana

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na ‘Sharhin bayan labarai, wand ani tahar amin zan karanta.

A cikin shirimmu na yau zamu yi Magana dangane cewa, shin gaskiyar ne ‘HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.

Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya bayyana cewa gwamnatin HKI a karon farko a hukumance, ta bada sanarwan cewa, tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar, kuma wannan Babbar barazana ce kuma hatsari ne ga samuwar kasar kai tsaye. Tambaya ta farko it ace, menene Alamar karancin sojoji a cikin rundunonin sojojin HKI?

Sanarwan ma’aikatar yakin HKI dangane da wannan ta ce, tana fada da karancin sojoji kimani 1300 a dukka rassan sojojin kasar kama daga kananan sojoji har zuwa manya. Bayanin ya kara da cewa ma’aikatar tana fama da karancin sojoji masu mukamin kanar har guda 300 a cikin rundunoninta gaba daya.

Har’ila, rahoton ya kara da cewa kashi 30 na kwamandojin sojojin kasar masu manya-manyan mukamai zasu yi ritaya a shekara mai zuwa. Sannan wasu kashi 30% na sojoji na ko ta kwana da kuma wadanda suke aiki na dindin din a cikin sojojin kasar suma zasu yi ritaya, ba zasu sake komawa cikin sojojin haramtacciyar kasar ba.

Rahoton ya kara da cewa, kashi 37% na sojojin suna son ci gaba da aikinsu a rundunonin ta, wanda ya nuna cewa adadin ya kara yin kasa idan an kwanatnta da shekara ta 2018 wanda ya kai kashi 58%.

Sannan tambaya ta gaba itace, menene dalilan da suka kawo karancin sojojin a cikin HKI ?.

Masu Nazari sun bayyana cewa matsalar karancin sojoji a HKI yana komawa daga asali zuwa ga matsalolin tsaro da kuma tattalin arziki. Yaki mai tsawo musamman a cikin shekaru biyu da suka gabata, da gajiya mai tsanani ya rage kodayin sojojin da kuma iyalansu ci gaba da wannan aikin.

A cikin rahoton da ma’aikatar yakin HKI ta fitar ta bayyana cewa, kashi 70% na matsalolin da sojojin haramtacciyar kasar suka fuskanta sun hada da tsawon yakin da suka kutsa cikinsa, wanda ya wuce lokacin da yakamata su yi.

Banda haka a cikin shekaru biyu da suka gabata, yakin ya tsananta kuma yayi tsawo ta yadda sojojin da iyalansu sun kasa hakuri fiye da hakan.

A bangaren tattalin arziki kuma, tsadar rayuwa a cikin kasar ya kai ga sojojin da kuma iyalansu sun ga cewa shiga harkar kasuwanci ne kawai zai fiddasu daga matsalolin tattalin arzikin da suka shiga musamman bayan yakin shekaru biyu da suka gabata. Don haka albashin da suke samu a aikin soje ya yi kasa sosai ta yadda ba za’a iya kwatantaci da wasu ayyuka wanda ba na soje ba.

Sannan tambaya ta gabata ita ce, karancin sojoji a cikin rundunonin HKI zuwa ga me yake nuni?  Wannan a fili yake, kuma hatta a cikin rahoton da ma’aikatar yakin ta fitar ta yi nuni ga wannan al-amarin. Inda take cewa, matsalar karancin sojoji a rundunonin haramtacciyar kasar ya kai ga barazana ga tsarin cikin gida na kasar, kuma dole ne gwamnati kasar ta dauki matakan da suka dace, don magance ta , da gaggawa.

Ta kuma kara da cewa ratayar kashi 30% na kwamandojin sojojin kasar yana nuna zuwa ga matsalolin gudanarwa a cikin rundunonin sojojin kasar da kuma matsalolin horar da sabbin sojoji.

Masana suna ganin wannan matsalar tana iya zama barazana ga HKI musamman idan ta sake shiga yaki da kungiyoyi ko kasashe masu gwagwarmaya da ita a yankin. Kuma idan haka ya faru raunin sojojin HKI zai bayyana a fili a duk wani yakin da zata shiga nan gaba a yankin Asiya ta kudu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufar December 2, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Janar Chiristopher Musa ( Ritaya) A Matsayin Ministan Tsaro December 2, 2025 Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa December 2, 2025  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota December 2, 2025 Hamas Ta Caccaki Isra’ila Game Da Hana Shigar Da Kayayyakin Agaji  A Yankin Gaza December 2, 2025 Ministan Tsaron Najeriya  Ya Mika Takardar Ajiye Aiki Ga Shugaban Kasa Ahmad Tinubu. December 2, 2025 Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango December 2, 2025 Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau December 2, 2025 An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran December 2, 2025 Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma
  • MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano