Takunkumi kan Musulmi masu ibada a Indiya
Published: 11th, March 2025 GMT
Wani babban jami’in ‘yan sanda a jihar Uttar Pradesh ta Indiya ya bukaci musulmi da su yi sallar Juma’a a gida.
A cewar radiyon gwamnatin Pakistan, Firimiyan Jihar Uttar Pradesh Yogi Adityanath ya kare kalaman jami’in ‘yan sandan game da musulmi, inda ya ce, “A yayin da ake gudanar da bukukuwan Holi sau daya a shekara, ana gudanar da sallar Juma’a a duk mako.
Ya bayyana jami’in a matsayin gwarzo jarumi, tare da bayyana cewa wannan ra’ayi nasa daidai ko da kuwa hakan ya bakantawa wasu.
Ya kara da cewa: “Bikin Holi ya fi sallar Juma’a muhimmanci, amma ana gudanar da shi sau daya ne kawai a shekara, don haka gudanar da shi yana da fifiko a kan Jum’a.”
Jami’in ‘yan sandan da ake magana a kai ya fada a wata hira da manema labarai cewa: “Idan musulmi suna son fita to babu matsala, kuma idan aka watsa musu musu kaloli to kada su yi korafi kan hakan, ko kuma su zauna a gida.
Firimiyan Uttar Pradesh ya bayar da hujjar cewa ana iya jinkirta Sallar Juma’a har zuwa lokacin da ‘yan Hindus za su kammala bukukuwansu, ko kuma kowane musulmi ya yi sallar Juma’a a gida.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da malamin addinin musulinci Maulana Khalid Rashid Faranji ya bayyana cewa za a gudanar da sallar Juma’a kamar yadda aka saba a ranar 14 ga watan Maris, ranar da ‘yan addinin Hindus suke gudanar da wasu bukukuwansu na addini.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sallar Juma a a gudanar da
এছাড়াও পড়ুন:
MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
Babban zauren MDD ta amince da kudurori guda biyu wadanda suka yi tir da HKI a jiya talata dangane da mamayar da take yiwa kasar Falasdinu tun shekara 1967 da kuma tuddan golan na kasar Siriya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI ta mamaye tuddan golan na kasar Siriya ne tun yakin kwanaki 6 a shekara 1967 sannan gwamnatin HKI ta tabbatar da kwace yankin a shekara ta 1981. Amma kwamatin tsaron MDD ta yi watsi da mamayar tun lokacin, ta bayyana hakan mamaya ne ba bisa ka’ida ba.
Labarin ya kara da cewa, kasashen Djibouti, Jordan, Mauritania, Qatar, Senegal, da Palestinu ne suka gabatar da kudurin wanda ya sami amincewar kasashe 151, 11 na wadanda basu amince ba (wadanda suka hada da Amurka da HKI) da kuma 11 na wadanda basu kada kuri’arsu ba.
Dangane da tuddan golan kuma wanda kasar Masar ta gabatar, ya sami amincewar kasashe 123, 7 na wadanda basu amince ba sannan 41 na wadanda suka ki kada kuri’unsu. Kudurin da babban zauren ya amince da shi dangane da Falasdinu dai y ana goyon bayan samar da kasashe biyu. Da kuma kira zuwa ga kawo karshen mamayar da HKI take wa kasar Falasdinu tun shekara ta 1967
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran December 3, 2025 Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci December 3, 2025 Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci