HausaTv:
2025-11-14@20:35:38 GMT

Takunkumi kan Musulmi masu ibada a Indiya

Published: 11th, March 2025 GMT

Wani babban jami’in ‘yan sanda a jihar Uttar Pradesh ta Indiya ya bukaci musulmi da su yi sallar Juma’a a gida.

A cewar radiyon gwamnatin Pakistan, Firimiyan Jihar Uttar Pradesh Yogi Adityanath ya kare kalaman jami’in ‘yan sandan game da musulmi, inda ya ce, “A yayin da ake gudanar da bukukuwan Holi sau daya a shekara, ana gudanar da sallar Juma’a a duk mako.

Ya bayyana jami’in a matsayin gwarzo jarumi,  tare da bayyana cewa wannan ra’ayi nasa daidai ko da kuwa hakan ya bakantawa  wasu.

Ya kara da cewa: “Bikin Holi ya fi sallar Juma’a muhimmanci, amma ana gudanar da shi sau daya ne kawai a shekara, don haka gudanar da shi yana da fifiko a kan Jum’a.”

Jami’in ‘yan sandan da ake magana a kai ya fada a wata hira da manema labarai cewa: “Idan musulmi suna son fita to babu matsala, kuma idan aka watsa musu musu kaloli to kada su yi korafi kan hakan, ko kuma su zauna a gida.

Firimiyan Uttar Pradesh ya bayar da hujjar cewa ana iya jinkirta  Sallar Juma’a har zuwa lokacin da ‘yan Hindus za su kammala bukukuwansu, ko kuma kowane musulmi ya yi sallar Juma’a a gida.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da malamin addinin musulinci Maulana Khalid Rashid Faranji  ya bayyana cewa za a gudanar da sallar Juma’a kamar yadda aka saba a ranar 14 ga watan Maris, ranar da ‘yan addinin Hindus suke gudanar da wasu bukukuwansu na addini.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sallar Juma a a gudanar da

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara

An kashe wani da ake zargin ɗan bindiga ne, yayin wani artabu da ’yan sanda da ’yan sa-kai suka yi da wasu mahara a Jihar Kwara.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Adekanbi, kusa da garin Bode Saadu.

Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa Mutfwang ya musanta raɗe-raɗin sauya sheƙa zuwa YPP

Rahotanni sun nuna cewa ’yan bindigar sun yada zango a saman wani dutse da ke kallon ƙauyen.

Suna hangar jami’an tsaro sai suka fara harbi ba ƙaƙƙautawa.

’Yan sanda da jami’an sa-kai sun yi artabu tare da tarwatsa maharan, inda wasu daga cikinsu suka tsere da raunin harbin bindiga.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a.

Bayan an artabun, jami’an tsaro sun duba yankin, inda suka samu gawar mutum ɗaya da ake zargin ɗan bindiga ne.

Haka kuma an gano bindiga ƙirar AK-49 da harsasai 32 a wajen.

SP Adetoun, ta ce wannan aikin wani muhimmin ci gaba ne a ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen kawar da masu aikata laifi a jihar.

Ta kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimaka wa yaƙi da laifuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • Limamin Juma’a Ya Bukaci Ganin An Kai Karar Donald Trump A Kotunan Duniya
  • Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa
  • GORON JUMA’A
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Iraki: Hukumar Zabe Ta Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu
  • DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma