HausaTv:
2025-08-17@05:35:25 GMT

Takunkumi kan Musulmi masu ibada a Indiya

Published: 11th, March 2025 GMT

Wani babban jami’in ‘yan sanda a jihar Uttar Pradesh ta Indiya ya bukaci musulmi da su yi sallar Juma’a a gida.

A cewar radiyon gwamnatin Pakistan, Firimiyan Jihar Uttar Pradesh Yogi Adityanath ya kare kalaman jami’in ‘yan sandan game da musulmi, inda ya ce, “A yayin da ake gudanar da bukukuwan Holi sau daya a shekara, ana gudanar da sallar Juma’a a duk mako.

Ya bayyana jami’in a matsayin gwarzo jarumi,  tare da bayyana cewa wannan ra’ayi nasa daidai ko da kuwa hakan ya bakantawa  wasu.

Ya kara da cewa: “Bikin Holi ya fi sallar Juma’a muhimmanci, amma ana gudanar da shi sau daya ne kawai a shekara, don haka gudanar da shi yana da fifiko a kan Jum’a.”

Jami’in ‘yan sandan da ake magana a kai ya fada a wata hira da manema labarai cewa: “Idan musulmi suna son fita to babu matsala, kuma idan aka watsa musu musu kaloli to kada su yi korafi kan hakan, ko kuma su zauna a gida.

Firimiyan Uttar Pradesh ya bayar da hujjar cewa ana iya jinkirta  Sallar Juma’a har zuwa lokacin da ‘yan Hindus za su kammala bukukuwansu, ko kuma kowane musulmi ya yi sallar Juma’a a gida.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da malamin addinin musulinci Maulana Khalid Rashid Faranji  ya bayyana cewa za a gudanar da sallar Juma’a kamar yadda aka saba a ranar 14 ga watan Maris, ranar da ‘yan addinin Hindus suke gudanar da wasu bukukuwansu na addini.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sallar Juma a a gudanar da

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Harkokin Shari’ar Kasa Da Kasa Na Iran Ya Yi Tofin Allah Tsine Kan Furucin Jami’ar Shari’ar Kasa Da Kasa

Mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da kasa da kasa ya mayar da martani ga son zuciya da wani jami’in kasa da kasa ke yi game da mamayar ‘yan sahayoniyya

Mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya yi tsokaci game da kalaman mataimakiyar shugaban kotun kasa da kasa (ICJ) na goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila, yana mai cewa: “Wannan wani lamari ne mai ban mamaki da ya saba wa ka’idojin shari’a da kuma ka’idar rashin son kai na shari’a.”

A wata sanarwa dayta fitar a dandalin X, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin shari’a da harkokin kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya rubuta cewa: “Wannan wani lamari ne mai ban mamaki da ya saba wa ka’idojin shari’a. Mataimakiyar shugabar kotun kasa da kasa ta fito fili ta bayyana goyon bayanta ga hukumar Isra’ila, yar mamaya da ake ci gaba da gudanar da shari’a da dama a gaban kotu.”

Gharibabadi ya kara da cewa: Wannan ra’ayi na nuna son kai yana zubar da mutuncin kotun kasa da kasa da kuma saba ka’idar amincin shari’a da rashin son kai.

Ya kamata a lura cewa mataimakiyar shugabar kotun kasa da kasa (ICJ) ta Uganda Julia Sebutinde, ta bayyana cewa “Allah yana goyon bayanta, kan tsayawa tare da Isra’ila,” bisa la’akari da cewa “wannan alamun ƙarshen duniya ne da ya bayyana a Gabas ta Tsakiya.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araqchi  Ya Gode Wa Gwamnatin Iraki Da Al’ummarta Kan Kyakkyawar Tarbar Masu Ziyarar Arba’een August 16, 2025 Kungiyar Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Sanya Ta Cikin Jerin Sunayen Bakin Littafin Majalisar Dinkin Duniya August 16, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Tafka Muggan Ayyukansu A Yankin Zirin Gaza August 16, 2025 Mataimakiyar Shugaban Kotun ICJ Ta Ce Tana Goyon Bayan HKI August 16, 2025 Burtaniya Zata Gurfanar Da mutane 60 Saboda Goyon Bayan Falasdinawa August 16, 2025 Qalibof: Dole Ne Musulmi Su Hada kai Don Matsin Lamba Ga HKI August 16, 2025 Aragchi: Yiyuwan Sake Shiga Yaki Da HKI Nan Kusa Yana Da Wuya August 16, 2025 Putin da Trump sun bayyana aniyarsu ta kawo karshen rashin jituwa da warware batun Ukraine August 16, 2025 Takht-Ravanchi: Iran a shirye take ta ci gaba da tattaunawa kan hakkinta na nukiliya August 16, 2025 Sudan: Al-Burhan ya ce babu sulhu tsakaninsu da dakarun RSF August 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Yi Allah Wadai Da Kalaman Fira Ministan Isra’ila Kan Mamaye Yankunan Kasashe
  • Jami’in Harkokin Shari’ar Kasa Da Kasa Na Iran Ya Yi Tofin Allah Tsine Kan Furucin Jami’ar Shari’ar Kasa Da Kasa
  • Qalibof: Dole Ne Musulmi Su Hada kai Don Matsin Lamba Ga HKI
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • GORON JUMA’A
  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16