Aminiya:
2025-12-02@09:41:31 GMT

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata

Published: 10th, March 2025 GMT

Assalamu alaikum. Barkanmu da sake haduwa cikin wannan fili. Da fatan Allah Ya amfanar damu dukkan bayanan da za su zo cikinsa, amin.

Ga ci gaban bayani kan alherai goma ga ma’aurata cikin Ramadan.

4. Salon buɗa baki

Ma’aurata za su yi amfani da lokacin buɗa baki don ƙara kusanci, farfaɗo da shau’uka cikin zuciya da ɗumama sha’awa.

Ma’aurata su tsara buɗa bakinsu ta yadda za su zama kamar dai su sabbin masoya ne da suka sami kansu tsundum cikin sabuwar soyayyar juna.

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa

Suna buɗa bakin cikin wasa da raha da tsokanar juna, ciyar da juna a baki, kallon marmasa soyayya da kiran juna sunayen soyayya masu ƙayatarwa da sa nishaɗi.

5.Wasanni:

Don ɗebe ma juna kewa lokacin azumi, ta hanyar wasanni na baka, na jiki da kuma na wasa kwakwalwa.

Misali da Yamma lokacin da uwargida ke kakaniyar aikin gida, Maigida da iya ɗebe mata kewa da wannan wasan kacici kacicin: maigida zai ce da uwargida na fi son ki saboda kaza da kaza. Ita ma sai ta ba shi amsa, a’a nice dai na fi son ka saboda kaza da kaza.

Haka za su yi tayi wanda dalilai suka ƙare masa shi ya faɗi wasan. Bayan buɗa baku kafin lokacin tarawiyyi wasan tsere, ko tsalle ko kuma wanda yafi dace.

A kwanakin karshen mako kuma Ma’aurata su shirya ma juna kacici kacici akan wani ɓangare na ilmi, kamar akan Ramadan, Kur’ani ko tarihin Annabi Sallalahu Alayhi wa Sallam. Wanda ya ci kuma a gabatar da wata ’yar kyauta gare shi.

Waɗannan wasanni suna da matukar muhimmanci da kara karfin igiyar auren, minti goma ya yi yawa wajen aikantar da su, amma za su bar farin ciki na har abada a zuciyar Ma’aurata.

6.Ɗauke nauyi:

A dubi wani abu mai nauyi ga abokin aure sai a sauke masa wannan nauyin dan ya ji saukin Ramadan kuma a sami lada mai yawa.

Kamar wata rana Maigida ya ce uwargida ta huta, ya je ya haɗo kayan buɗa baki gaba ɗaya daga waje sai dai a zuba a ciki. Ko in uwargida ta kwashi adashenta ta canza su zuwa sababbin kuɗi ta sa ambulan ta ba Maigida ta ce ga shi ya ƙara na hidimar azumi da Sallah.

Ma’aurata dai su dubi abinda ya nauyaya ga abokin aurensu wanda sauke sa zai kawo masu saukin rayuwa sai su sauke ma shi daidai iyawarsu.

7.Sadaukarwa

Shi ne Ma’aurata su sadaukar da wani abu daga rayuwarsu dan kyautatawa ga abokin aurensu.

Kyakykyawan zamantakewar aure itace mai cike da yawan sadaukarwa ta kowane ɓangare.

Don dacewa da nun’in ladar da ke cikin Ramadan, Ma’aurata sai su aikatar da ayyukan sadaukarwa ga junansu.

Kamar maigida ya rika taya uwargida aikin gida ko ta fannin wanki da gugar kayan yara ne kawai.

Yana daga cikin Sadaukarwa kau da kai daga abubuwa marasa daďi ta ɓangaren abokin aure, kar a zarge shi game da nakasun sa da kuma yafe ma kurakurensa

8.Tunatarwa:

Sai Ma’aurata su yi nazari kan wani rauni na junansu ta ɓangaren Addini, hallayya da zamantakewa, musamman in wannan rauni da zai haifar masu da matsala a ranar hisabi, kamar rashin yin Sallah cikin lokaci, kamar yawo da zancen mutane, kamar rashin zuwa masallaci ga maigida da sauransu.

Sai a shirya nasiha da tunatarwa mai ratsa zuciya ga abokin aure akan wannan rauni nasa.

A rika nuna masa illolinsa da kuma irin halakar da za su auka da shi tun a duniya da kuma lahira.

Wannan tunatarwar za a yi ta da kalamin baki, a rubuce a takarda ko a sakon wayar tafi da gidanka.

A lura ban da zargi da ɗora laifi a cikin nasiha sai dai faɗakarwa da nusantarwa.

9.Romansiyya:

Misalan abubuwan romansiyya da Ma’aurata za su iya yi cikin Ramadan, in uwargida tana sanwa a kichin maigida ya lallaɓa ya rufe mata ido ta baya, uwargida ta rubuta wasikar soyayya ta sa a ma’ajiyar kuɗin mijinta ko a aljhunsa sai ya tafi wajen aiki ya fito da ita ya karanta.

Bayani mai lamba 5 shi ma ya shigo cikin ayyukan Romansiyya musamman wasan ‘na fi son ki saboda kaza’

10. Yin ibada tare:

Wannan shi ne mafi muhimmanci a cikin abubuwa goman da suka gabata. Ma’aurata su rika neman kusancin Allah ta hanyar yin ibadojinsu tare duk lokacin da yin hakan ta kama kuma suna waje ɗaya.

Maimakon Maigida ya yi tasbihi da yatsunshi, yana iya yi da yatsun matarsa, ita ma haka. Yin musafar Al-Qur’ani tare, ko ɗaya ya karanta ɗaya ya karanta fassarar Ayoyin.

Sai mako na gaba in sha Allah, da fatan Allah Ya sa mu kasance cikin kulawarsa a ko yaushe, amin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ma aurata Ramadan Ma aurata su uwargida ta

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma

A daidai lokacin ziyarar Paparoma Leo na XIV  shugaban Katolika na duniya a kasar Lebanon, kungiyar Hezbollah ta fitar da wata sanarwa a hukumance da aka aike masa.

Kungiyar ta yi maraba da ziyarar Paparoma, ta kuma jaddada muhimmancin Lebanon a matsayin kasa mai bambance-bambance na addini da kabilu da akidu, wadda al’ummominta suke bukatar rayuwa tare juna a cikin kwanciyar hankali da fahimtar juna a zamantakewa da siyasa.

A cikin wannan sakon, Hezbollah ta gabatar da Lebanon a matsayin gada wadda ta hada tsohon tarihi tsakanin Musulunci da Kiristanci da kuma tsakanin al’adu da akidu daban-daban.

Wasikar ta ambaci kalaman Paparoma John Paul II, wanda ya dauki Lebanon ba wai kawai a matsayin gida ba, a’a a ya dauki kasar ne a matsayin daya daga cikin wurare masu tasiri na addinai da aka saukar daga sama.

Hezbollah ta jaddada rawar da kasar ke takawa wajen samar da fahimta tsakanin addinai da al’adu. Wasikar ta nuna cewa rikicin duniya da ya samo asali daga rashin girmama hakkin dan adam, tare da hankoron bautar da shi da kuma tauye masa hakkokinsa, wanda kuma wannan Rashin adalcin ne ya share hanyar kaiwa zuwa ga tashe-tashen hankula da Rashin zaman lafiya a duk inda aka samu hakan.

Wani muhimmin bangare na wasikar ya yi ihara ne ga halin da ake ciki a Falasdinu. Hezbollah ta kira halin da ake ciki a Gaza da  “kisan kare dangi a fili” sannan kuma ta bayyana ayyukan Isra’ila a Lebanon shi ma a matsayin  “wani zalunci da ba za a yarda da shi ba,” kuma ta dauki wadannan matsalolin a matsayin sakamakon kwadayin gwamnatin Sihiyona na shimfida ikonta a  kan albarkatu da filaye na wadannan al’ummomi. Ta kuma jaddada cewa goyon bayan manyan ƙasashe ga Isra’ila a bayyane take haƙƙoƙin al’ummomin yankin ne.

Hizbullah ta kuma nanata alƙawarinta na kasancewa tare da gwamnatin dimokuraɗiyya mai zaman kanta, kiyaye tsaron cikin gida, da kuma fuskantar duk wani zalunci ko mamaye, kuma ta bayyana adawarta da tsoma bakin ƙasashen waje da ke barazana ga ‘yancin kai na Lebanon.

Wasikar ta kuma jaddada abubuwan da suka shafi Musulmai da Kiristoci, kuma ta bayyana mabiyan tafarkin Almasihu a matsayin manzannin zaman lafiya da kare haƙƙin ɗan adam.

Hizbullah ta yi kira ga Paparoma da ya ɗauki matsayi bayyananne wajen nuna Rashin amincwarsa da duk wani rashin adalci da zaluncin Isra’ila a lokacin ziyararsa a Lebanon, da kuma nuna haɗin kai da goyon ga al’ummar Lebanon.

Wasikar ta kammalawa da cewa,  Kungiyar Hizbullah na yin fatan alheri da fatan samun nasarar cimma burin tafiyar, na ganin an yada zaman lafiya da karfafa fahimtar juna tsakanin dukkanin Mabiya addinai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025  Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu November 30, 2025 Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5 November 30, 2025 Najeriya :  Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru   November 30, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano