Aminiya:
2025-07-05@22:16:53 GMT

Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu

Published: 9th, March 2025 GMT

Iyalan marigayi Janar Sani Abacha, sun gargaɗi Tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Babangida, da ya daina faɗin maganganun da ka iya ɓata sunan mahaifinsu.

A cikin wata sanarwa da Mohammed Abacha, ya fitar a madadin iyalan marigayin a ranar Lahadi, sun musanta iƙirarin da Babangida ya yi a cikin littafinsa mai suna ‘A Journey in Service’.

Ramadan: Ali JC ya bai wa jama’a tallafin kayan abinci a Gombe An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

Ya ce Janar Abacha ne, ya ke da alhakin soke zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga wata Yunin 1993.

“Duk wani yunƙuri na ɗora wa Janar Sani Abacha laifin soke zaɓen, wanda a lokacin ya kasance babban jami’in soja a mulkin Babangida, ƙoƙari ne na sauya tarihi da gangan.

“Shekaru da dama, wasu mutane na ƙoƙarin ɓata haƙiƙanin abin da ya faru a wannan lokaci a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya,” in ji sanarwar.

Iyalan Abacha sun jaddada cewa a lokacin da aka soke zaɓen, Janar Abacha ba shi ne Shugaban Ƙasa ko Babban Kwamandan Askarawan Najeriya ba.

Sun ce Babangida ne, ya ke da cikakken iko, kuma shi kaɗai ne ke da alhakin duk wani hukunci da gwamnatinsa ta yanke.

“Hukuncin soke zaɓen ya fito ne daga gwamnatin Janar Ibrahim Babangida, wanda yake a matsayin Shugaban Ƙasa, yana da cikakken iko kuma shi ne ke da alhakin duk wani abu da gwamnatinsa ta aikata,” in ji sanarwar.

Haka kuma, iyalin Abacha sun yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji “ƙagaggun labarai da ake ƙirƙira don karkatar da tunanin jama’a saboda wasu muradu na siyasa ko na ƙashin kai.”

Sun jaddada cewa, “Ba za mu yarda a ɓata tarihin mahaifinmu da wasu zarge-zargen banza da aka ƙirƙira don kare waɗanda suka aikata laifin ba.”

“Mun kuma ga dacewar tunatar da mutane cewa a lokacin da rayuwar Janar Babangida ta shiga hatsari, Janar Abacha ne, ya kawo masa ɗauki, ya tabbatar da cewa ba a cutar da shi ba,” in ji iyalan.

A ƙarshe, sun soki littafin ‘A Journey in Service’, inda suka ce littafin bai bayar da sahihin tarihin abubuwan da suka faru ba.

“A cewar wani da ya yi sharhi a kan littafin, gaskiya, amana ba halaye ba ne da za a alaƙanta su da marubucin ba,” in ji su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi iyalai soke zaɓen

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Wata Kotun Majistare da ke jihar Kano ta yanke wa fitaccen ɗan TikTok, Umar Hashim da aka fi sani da Tsulange, hukuncin ɗauri na shekara ɗaya bisa laifin aikata abinda ya saɓa da tarbiyya a bainar jama’a.

Alƙaliyar kotun, Hadiza Muhammad Hassan, wadda ke zaune a Gyadi Gyadi, ta samu Tsulange da laifi na zubar da mutunci a idon jama’a bayan gabatar da hujjoji da shaidu. Ta bayyana cewa an tabbatar da cewa ɗan TikTok ɗin ya aikata laifin ne cikin gangan.

Ɗan TikTok Tsulange Ya Shiga Hannu Bisa Wanka Da Rigar Mama A Titi Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

A hukuncin da ta yanke, ta ba da umarnin da a ɗaure shi na tsawon shekara guda, ko kuma ya biya tarar Naira 80,000 a matsayin madadin ɗaurin. Haka kuma, kotun ta umarce shi da ya biya hukumar tace fina-finai ta jihar Kano Naira 20,000 don rage kuɗin bincike da shari’ar da aka yi.

Rahoton LEADERSHIP ya nuna cewa an gurfanar da Tsulange ne a watan Yuni 2025 bayan hukumar ta kama shi kan wani faifan barkwanci da ya ɗauka yana wanka a titi yana sanye da kayan mata a matsayin wani ɓangare na wasan kwaikwayo.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”
  • Jalali: Mun  Hana Fitowar Sanadarorin Nukiliya Ta Hanyar Aiki Da Ka’idojin Tsaro
  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
  • Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran