Aminiya:
2025-11-19@07:41:04 GMT

Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu

Published: 9th, March 2025 GMT

Iyalan marigayi Janar Sani Abacha, sun gargaɗi Tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Babangida, da ya daina faɗin maganganun da ka iya ɓata sunan mahaifinsu.

A cikin wata sanarwa da Mohammed Abacha, ya fitar a madadin iyalan marigayin a ranar Lahadi, sun musanta iƙirarin da Babangida ya yi a cikin littafinsa mai suna ‘A Journey in Service’.

Ramadan: Ali JC ya bai wa jama’a tallafin kayan abinci a Gombe An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

Ya ce Janar Abacha ne, ya ke da alhakin soke zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga wata Yunin 1993.

“Duk wani yunƙuri na ɗora wa Janar Sani Abacha laifin soke zaɓen, wanda a lokacin ya kasance babban jami’in soja a mulkin Babangida, ƙoƙari ne na sauya tarihi da gangan.

“Shekaru da dama, wasu mutane na ƙoƙarin ɓata haƙiƙanin abin da ya faru a wannan lokaci a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya,” in ji sanarwar.

Iyalan Abacha sun jaddada cewa a lokacin da aka soke zaɓen, Janar Abacha ba shi ne Shugaban Ƙasa ko Babban Kwamandan Askarawan Najeriya ba.

Sun ce Babangida ne, ya ke da cikakken iko, kuma shi kaɗai ne ke da alhakin duk wani hukunci da gwamnatinsa ta yanke.

“Hukuncin soke zaɓen ya fito ne daga gwamnatin Janar Ibrahim Babangida, wanda yake a matsayin Shugaban Ƙasa, yana da cikakken iko kuma shi ne ke da alhakin duk wani abu da gwamnatinsa ta aikata,” in ji sanarwar.

Haka kuma, iyalin Abacha sun yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji “ƙagaggun labarai da ake ƙirƙira don karkatar da tunanin jama’a saboda wasu muradu na siyasa ko na ƙashin kai.”

Sun jaddada cewa, “Ba za mu yarda a ɓata tarihin mahaifinmu da wasu zarge-zargen banza da aka ƙirƙira don kare waɗanda suka aikata laifin ba.”

“Mun kuma ga dacewar tunatar da mutane cewa a lokacin da rayuwar Janar Babangida ta shiga hatsari, Janar Abacha ne, ya kawo masa ɗauki, ya tabbatar da cewa ba a cutar da shi ba,” in ji iyalan.

A ƙarshe, sun soki littafin ‘A Journey in Service’, inda suka ce littafin bai bayar da sahihin tarihin abubuwan da suka faru ba.

“A cewar wani da ya yi sharhi a kan littafin, gaskiya, amana ba halaye ba ne da za a alaƙanta su da marubucin ba,” in ji su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi iyalai soke zaɓen

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda November 17, 2025 Manyan Labarai Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon November 17, 2025 Manyan Labarai Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja November 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mai taɓin hankali ya kashe soja a Legas
  • Sojojin Najeriya Sun Karyata Cewa “ISWAP” Ta Kashe Wani Babban Jami’i Mai Mukamin  Birgediya
  • Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji
  • Ana Zargin ’Yan Ta’adda Sun Kashe Janar Ɗin Soji A Harin Kwanton-Ɓauna A Borno
  • Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
  • Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
  • Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio
  • Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato
  • NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji