Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53
Published: 9th, March 2025 GMT
Abin da ya sa wannan tsari ya yi daban shi ne ba wai domin irin tsarin gine-gine da za a yi ba; akwai allunan batun siyasa da kuma ‘yancin Falasdinawa.
A jawabinsa a wajen taron, shugaban Masar Abdul Fattah al-Sisi ya yi kira da a samar da tsare-tsare guda biyu da za su tafi lokaci daya wanda aka fi sani da tsarin kasa biyu – kasar Falasdinawa da kuma ta Isra’ila.
Larabawa da kuma sauran mutane na ganin wannan itace kadai hanyar samar da mafita ga rikicin da aka dade ana fama da shi, sai dai Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da kawayensa sun yi watsi da batun.
Wannan sabon tsari ya bayyana cewa Gaza za ta zauna karkashin kulawar “gwamnatin Falasdinawa na wucin-gadi” wanda ya kunshi kwararru.
Sai dai ba su bayar da cikakkun bayanai ba kan rawar da har ma idan akwai wanda Hamas za ta taka.
A kann batun barazanar kungiyoyin mayaka, kungiyar ta ce za a warware wannan matsala idan aka magance abin da yake janyo rikicin daga bangaren Isra’ila.
Yayin da wasu kasashen Larabawa ke yin kira don kawo karshen Hamas; saura kuma sun yi imanin cewa matakin haka ya rage ga Falasdinawa.
An bayyana cewa Hamas ta ce ta amince ba za ta taka wata rawa ba wajen tafiyar da Gaza, amma sun bayyana karara cewa ajiye makamai ba abu ne mai yiwuwa ba.
Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, wanda ya yaba da tsarin shugaba Trump kan Gaza, ya sha bayyana cewa Hamas ba ta da wata rawa da za ta taka, har ma da hukumomin Falasdinawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Larabawa
এছাড়াও পড়ুন:
EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama tare da tsare Tsohon Ministan Ƙwadago kuma Tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Chris Ngige.
Mai magana da yawun Ngige, Fred Chukwuelobe ne, ya tabbatar da hakan da safiyar ranar Alhamis. bayan wasu rahotanni da aka yaɗa cewar an sace Ngige.
An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPCChukwuelobe, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa, “Ngige yana tare da EFCC. Ba a sace shi aka yi ba.”
Har zuwa yanzu EFCC ba ta bayyana dalilin da ya sa ta tsare Ngige ba.
Ana sa ran hukumar za ta fitar da sanarwa game da kama shi da kuma binciken da ta ke yi a kansa.
Ngige ya zama mutum na biyu daga cikin tsoffin ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da aka tsare a baya-bayan nan.
Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, shi ma yana hannun EFCC.
Hukumar ta ce tana binciken Malami ne kan wasu kuɗaɗen dala miliyan 310, wanda aka dawo da su Najeriya.
Sai dai ya musanta tuhumar da ake masa, inda ya bayyana cewa zarge-zargen ba su da tushe.
Masu sharhi a shafukan sada zumunta sun nuna damuwa kan yadda ake tsare tsoffin ministoci ba tare da bayyana dalili ba.
A gefe guda kuma, masu sharhi kan harkar siyasa sun ce irin wannan mataki na EFCC na nuna yadda hukumar ke zage damtse wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.