Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53
Published: 9th, March 2025 GMT
Abin da ya sa wannan tsari ya yi daban shi ne ba wai domin irin tsarin gine-gine da za a yi ba; akwai allunan batun siyasa da kuma ‘yancin Falasdinawa.
A jawabinsa a wajen taron, shugaban Masar Abdul Fattah al-Sisi ya yi kira da a samar da tsare-tsare guda biyu da za su tafi lokaci daya wanda aka fi sani da tsarin kasa biyu – kasar Falasdinawa da kuma ta Isra’ila.
Larabawa da kuma sauran mutane na ganin wannan itace kadai hanyar samar da mafita ga rikicin da aka dade ana fama da shi, sai dai Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da kawayensa sun yi watsi da batun.
Wannan sabon tsari ya bayyana cewa Gaza za ta zauna karkashin kulawar “gwamnatin Falasdinawa na wucin-gadi” wanda ya kunshi kwararru.
Sai dai ba su bayar da cikakkun bayanai ba kan rawar da har ma idan akwai wanda Hamas za ta taka.
A kann batun barazanar kungiyoyin mayaka, kungiyar ta ce za a warware wannan matsala idan aka magance abin da yake janyo rikicin daga bangaren Isra’ila.
Yayin da wasu kasashen Larabawa ke yin kira don kawo karshen Hamas; saura kuma sun yi imanin cewa matakin haka ya rage ga Falasdinawa.
An bayyana cewa Hamas ta ce ta amince ba za ta taka wata rawa ba wajen tafiyar da Gaza, amma sun bayyana karara cewa ajiye makamai ba abu ne mai yiwuwa ba.
Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, wanda ya yaba da tsarin shugaba Trump kan Gaza, ya sha bayyana cewa Hamas ba ta da wata rawa da za ta taka, har ma da hukumomin Falasdinawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Larabawa
এছাড়াও পড়ুন:
Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi
Majalisar Wakilai za ta ƙada kuri’a a ranakun 10 da 11 ga watan Disamba kan muhimman kudurorin gyaran kundin tsarin mulkin 1999, ciki har da kirkirar sabbin jihohi da kafa ’yan sandan jihohi.
Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Okezie Kalu, ya sanar da jadawalin a zaman majalisar, inda ya ce tattaunawa kan kudirin sauya kundin tsarin mulki za ta gudana yau da gobe kafin kada kuri’ar mako mai zuwa.
An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron NijeriyaKalu, wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan nazarin kundin tsarin mulki, ya bukaci ’yan majalisa su halarci zaman.
Ya shaida wa majalisar kwanan nan cewa kwamitin ya kammala aikin da ake bukata a wannan mataki, kuma yana shirin gabatar da takardun da aka daidaita don a yi la’akari da su.
A farko dai an gabatar da jimillar kudirori 87 da ke neman sauya sassa daban-daban na kundin tsarin mulki.
Kudirorin sun shafi gyaran harkokin zabe da shari’a, ’yan sandan jihohi da batutuwan kudi.
Sai dai bayan jin ra’ayin jama’a a matakin jihohi, taron jin ra’ayin jama’a na kasa a Abuja, tattaunawa da masu ruwa da tsaki da kuma daidaitawa da kwamitin majalisar dattawa kan kundin tsarin mulki, adadin kudirin da za a kada kuri’a ya ragu zuwa kusan 45.
A ranar Litinin, 24 ga watan Nuwamba, kwamitocin majalisar wakilai da na majalisar dattawa kan gyaran kundin sun gudanar da taron hadin gwiwa da kakakin majalisun jihohi a Abuja yayin da tsarin sauya kundin ya shiga matakin karshe.
Kalu da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, sun shaida wa kakakin majalisun jihohi cewa makomar kudirin sauye-sauyen yanzu ta dogara ne da majalisun jihohi bayan majalisar tarayya ta kammala aikinta. Kalu ya ce taron ya nuna matakin karshe kafin fara kada kuri’a.
Muhimman kudirorin da ake son gyarawaDaga cikin muhimman sauye-sauyen da aka gabatar kirƙirar ’yan sandan jihohi, ware kujeru na musamman ga mata a majalisa, ’yancin tsayawa takara ba tare da jam’iyya ba, karin ayyuka ga sarakunan gargajiya, karfafa ikon majalisar tarayya da ta jihohi wajen kira shugaban ƙasa da gwamnonin jihohi kan harkokin tsaro da sauransu.
Kazalika, wani kudiri na neman sauya kundin domin mayar da gudanar da zaben kananan hukumomi daga hukumar zabe ta jihohi zuwa INEC.
Haka kuma, wani kudiri na neman tabbatar da cewa a kammala dukkan shari’un zabe kafin rantsar da zababbun jami’ai.
Babban kudiri kuma shi ne na neman kafa ’yan sandan jihohi ta hanyar sauya kundin tsarin mulki domin cire su daga jerin dokokin tarayya zuwa jerin dokokin hadin gwiwa.
Masu goyon baya sun ce wannan mataki zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da suka yi yawa kuma suke neman fin ƙarfin ’yan sandan tarayya.
Kallo zai koma majalisun jihohiBayan an kammala kada kuri’a, za a tura kudirin da aka amince da su zuwa majalisun jihohi 36 don samun amincewa.
Aƙalla majalisun jihohi 24 (wato kashi biyu bisa uku) dole ne su amince da shi kafin a tura su ga shugaban ƙasa don ya sanya hannu.
Duk kudirin da bai samu amincewar jihohi ba zai mutu nan take.