Ƙungiyar Malaman Tsangaya a Jihar Gombe ta karrama Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya lambar yabo ta ‘Khadimul Qur’an’ a matsayin girmamawa ga goyon bayansa maras misaltuwa ga ilimin Alƙur’ani da kuma matakan da ya ɗauka wajen kyautata tsarin Almajiranci.

Ƙungiyar Malaman Tsangaya ta miƙa wannan girmamawa ga Gwamnan yayin wani taron buɗa-baki na musamman da aka shirya musu a Fadar Gwamnati da ke Gombe, wanda ya tattaro shugabannin malaman Tsangaya daga faɗin jihar.

Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto Yadda masana’antun Arewa suka koma kufai

Wannan taron na cikin tsarin shekara-shekara na Gwamna Inuwa Yahaya na shirya shan ruwa tare da jama’a, wanda hakan wani mataki ne da yake ƙara haɗin kai, zaman lafiya, da hulɗa a tsakanin al’ummar Musulmi.

A jawabinsa bayan buɗa-bakin azumi, Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kyautata jin daɗin malaman Tsangaya da kuma yara Almajirai.

Ya bayyana muhimmancin ilimin Alƙur’ani ga al’umma tare da jaddada buƙatar samar da yanayi mai ɗaukaka koyo da koyarwa.

Gwamnan ya yi bayanin yadda gwamnatinsa ta yi gagarumin ƙoƙari wajen gina manyan makarantun Tsangaya da ƙananan makarantun Almajirai a faɗin jihar, tare da haɗa ilimin Alƙur’ani da na zamani cikin tsarin karatu.

Haka kuma, ya yi nuni da cewa yara Almajirai an sanya su cikin shirin lafiya na Go-Health, wanda ke ba su damar samun kulawar lafiya kyauta domin tabbatar da lafiyarsu.

“Mu a matsayin gwamnati mun fahimci muhimmiyar rawa da makarantun Tsangaya ke takawa wajen tarbiyya da cigaban ilimi ga yaranmu.

“Wannan ne ya sanya muka fifita jin daɗinsu ta hanyoyi daban-daban, ciki har da gina makarantun Tsangaya da kuma shigar da su cikin shirin Go-Health domin samun ingantacciyar kulawar lafiya ba tare da wata matsala ba,” in ji Gwamna Inuwa.

Da yake magana a madadin malaman Tsangaya, Goni Mai Babban Allo ya yaba wa Gwamna Inuwa Yahaya kan goyon bayan da yake bayarwa ba dare ba rana.

Ya kuma bayyana cewa Gwamnan ya ɗauki matakai na musamman, ciki har da gina makarantun Tsangaya, sanya fitilu masu aiki da hasken rana a makarantun, da haɗa Almajirai cikin shirin kula da lafiya na jihar Gombe.

“Ba mu taɓa samun gwamnati da ta damu da jin daɗin malaman Tsangaya da ɗalibanmu kamar wannan ba,” in ji Goni Mai Babban Allo.

A cikin girmamawa ga ƙoƙarinsa da kuma sadaukarwarsa, Ƙungiyar Alarammomi ta naɗa Gwamna Inuwa Yahaya sarautar ‘Khadimul Qur’an’, alamar kasancewarsa bawan Alƙur’ani mai sadaukarwa.

Tun da farko, a jawabinta na maraba, Sayyada Amina Sheikh Dahiru Bauchi, mai bai wa gwamna shawara ta musamman kan harkokin Tsangaya da Ilimin Almajiranci, ta yi kira ga Alarammomi da su ƙara yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Inuwa Yahaya jihar Gombe malaman tsangaya Gwamna Inuwa Yahaya makarantun Tsangaya malaman Tsangaya a makarantun Tsangaya da

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wasu mutum uku da ake zargi da laifin sata da kuma ƙone gidan wani Bature a unguwar G.R.A, kusa da gidajen ’yan majalisa a jihar.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Hannatu Ibrahim mai shekaru 28 daga Kumo, Ahmed Adamu mai shekaru 20, da Abubakar Ibrahim mai shekaru 28.

Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4

A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, lamarin ya faru ne ranar 22 ga watan Maris, 2025 da misalin ƙarfe 8 na dare.

Sanarwar ta bayyana cewa Hannatu Ibrahim, wacce ke aiki a matsayin mai girki ga Mohammed Jurdi, wanda ɗan kasar Siriya da ke aiki da kamfanin Triacta Nigeria Limited, ta sace dala 35,000 (kimanin Naira miliyan 53.5) tare da banka wa gidan wuta.

Bayan samun rahoton, ‘yan sanda sun garzaya wajen, inda suka kama ta tare da gano dala 7,100 a wajenta.

A yayin bincike, ta ce Ahmed Adamu ne, mutum na farko da ta tuntuɓa bayan aikata laifin.

An samu dala 100 a cikin sakar hannunsu.

An kuma kama Abubakar Ibrahim, mai gadin gidan da aka yi satar, wanda ake zargi da taimaka musu wajen aikata laifin.

DSP Abdullahi, ya ce suna ci gaba da bincike, kuma suna shirin gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu.

Ya kuma tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka tare da tabbatar da adalci a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Sallah Karama Ta 2025/1446
  • Sarkin Kano Na 15 Ya Soke Hawan Daba Saboda Matsalar Tsaro
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe
  • Kwamishinan Abba ya yi murabus bayan watanni 7 da naɗinsa
  • Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa