Ƙungiyar Malaman Tsangaya a Jihar Gombe ta karrama Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya lambar yabo ta ‘Khadimul Qur’an’ a matsayin girmamawa ga goyon bayansa maras misaltuwa ga ilimin Alƙur’ani da kuma matakan da ya ɗauka wajen kyautata tsarin Almajiranci.

Ƙungiyar Malaman Tsangaya ta miƙa wannan girmamawa ga Gwamnan yayin wani taron buɗa-baki na musamman da aka shirya musu a Fadar Gwamnati da ke Gombe, wanda ya tattaro shugabannin malaman Tsangaya daga faɗin jihar.

Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto Yadda masana’antun Arewa suka koma kufai

Wannan taron na cikin tsarin shekara-shekara na Gwamna Inuwa Yahaya na shirya shan ruwa tare da jama’a, wanda hakan wani mataki ne da yake ƙara haɗin kai, zaman lafiya, da hulɗa a tsakanin al’ummar Musulmi.

A jawabinsa bayan buɗa-bakin azumi, Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kyautata jin daɗin malaman Tsangaya da kuma yara Almajirai.

Ya bayyana muhimmancin ilimin Alƙur’ani ga al’umma tare da jaddada buƙatar samar da yanayi mai ɗaukaka koyo da koyarwa.

Gwamnan ya yi bayanin yadda gwamnatinsa ta yi gagarumin ƙoƙari wajen gina manyan makarantun Tsangaya da ƙananan makarantun Almajirai a faɗin jihar, tare da haɗa ilimin Alƙur’ani da na zamani cikin tsarin karatu.

Haka kuma, ya yi nuni da cewa yara Almajirai an sanya su cikin shirin lafiya na Go-Health, wanda ke ba su damar samun kulawar lafiya kyauta domin tabbatar da lafiyarsu.

“Mu a matsayin gwamnati mun fahimci muhimmiyar rawa da makarantun Tsangaya ke takawa wajen tarbiyya da cigaban ilimi ga yaranmu.

“Wannan ne ya sanya muka fifita jin daɗinsu ta hanyoyi daban-daban, ciki har da gina makarantun Tsangaya da kuma shigar da su cikin shirin Go-Health domin samun ingantacciyar kulawar lafiya ba tare da wata matsala ba,” in ji Gwamna Inuwa.

Da yake magana a madadin malaman Tsangaya, Goni Mai Babban Allo ya yaba wa Gwamna Inuwa Yahaya kan goyon bayan da yake bayarwa ba dare ba rana.

Ya kuma bayyana cewa Gwamnan ya ɗauki matakai na musamman, ciki har da gina makarantun Tsangaya, sanya fitilu masu aiki da hasken rana a makarantun, da haɗa Almajirai cikin shirin kula da lafiya na jihar Gombe.

“Ba mu taɓa samun gwamnati da ta damu da jin daɗin malaman Tsangaya da ɗalibanmu kamar wannan ba,” in ji Goni Mai Babban Allo.

A cikin girmamawa ga ƙoƙarinsa da kuma sadaukarwarsa, Ƙungiyar Alarammomi ta naɗa Gwamna Inuwa Yahaya sarautar ‘Khadimul Qur’an’, alamar kasancewarsa bawan Alƙur’ani mai sadaukarwa.

Tun da farko, a jawabinta na maraba, Sayyada Amina Sheikh Dahiru Bauchi, mai bai wa gwamna shawara ta musamman kan harkokin Tsangaya da Ilimin Almajiranci, ta yi kira ga Alarammomi da su ƙara yin addu’o’in zaman lafiya da ci gaban Jihar Gombe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Inuwa Yahaya jihar Gombe malaman tsangaya Gwamna Inuwa Yahaya makarantun Tsangaya malaman Tsangaya a makarantun Tsangaya da

এছাড়াও পড়ুন:

Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio

Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio

Daga Musa Kutama, Kalaba

Yusuf Muhammad Abdullahi da aka fi sani da Yusuf Lazio, fitaccen jarumi ne a Masana’antar Finafinan Hausa, wato Kannywood. Jarumin ya yi shura a fim xin Na-Ladidi, inda ya ce, haxa waqa da fim a lokaci xaya, a wurinsa ba wani abu ba ne, hasali ma mawaqi ne shi kafin ya fara fitowa cikin fim.

Ga yadda hirar ta kasance:

Gabatar da kanka ?

Sunana Yusuf  Mohammad Abdullahi  ana kira na da  Yusuf Lazio.

Dama can kana da alaqa da Lazio ne ko kuwa kulob xin ne ake kiran ka da shi?

A’a sunan ya samo asali ne daga goya wa qungiyar wasan qwallon qafa ta Lazio baya da nake yi.

An lura a ‘yan kwanakin nan ka xauke qafa a harkar fim, ka fi karkata a kan waqa. Me za ka ce a nan?

Ba xauke qafa na yi ba, ina nan ina fitowa a wani fim mai suna Gidan Sarauta sannan kuma yanzu haka ina aiki ma a wani fim xin daban.

Ga alama ka fi mayar da hankali wajen yin waqa a kan fim, wane qarin bayani za kayi a nan?

Har yanzu ina yin waqa kuma ina yin fim, domin waqa ce ta fara fito da ni. Sannan kafin ma in fara fitowa a fim da ma ni waqa nake yi sannan na dawo yin fim.

Kana ganin za ka iya haxa taura biyu?

Eh,  ba za su yi wahala ba, tunda duk biyun suna da alaqa.

Tsakanin yin fim da kuma waqa wanne ya fi wani wahala?

Gaskiya wannan wata harka ce da zan ce ma kamar ado ne. Ita waqa ana yin ta daban, abu ne na basira. Sannan fim ma abu ne na sha’awa, don haka haxa biyun bai ba ni wahala ba kwatakwata.

Ka lura da irin sauyi da ci gaban da ake samu ta harkar fim da kayan aiki na zamani ya kawo?

Eh, to dama ai kasan duk mai sana’a duk wacce ta fi kawo maka riba ai ita za ka fi mayar da hankali a kai. Cikin ikon Allah mun samu sauyi mai yawa, mun samu nasara a kan haka, wanda a da qaramin jarumi ba zai iya yin fim nasa na kansa ba. Amma yanzu zai iya fitowa, ya yi fim nasa, ya bayar da umarni. Hakan ya sa na yi matuqar farin ciki da wannan ci gaba da aka samu.

Da ka ce an samu ci gaba ta wane vangare sai ka yi bayani?

Yanzu idan ka duba, zan iya yin fim ba darakta, ka ga zan iya yi, in sanya a Youtube, mutane su kalla. Ka ga wannan ba qaramin ci gaba ba ne aka samu a fannin yin fim. Sannan kuma yanzu ba sai ka naxi fim a kaset ko a wani CD ba, kana iya shiga Youtube ka sa, a kalla.

Ko kwalliya na biyan kuxin sabulu a sanya finafinanku ta kafar sada zumunta. Kuxaxen da kuka sanya aka yi aikin ko suna fitowa hala har ma a sa rai za a samun riba?

Qwarai ana samun nasara a kan haka, akwai riba.

Shin xora waqoqi ko fim a YouTube kana ganin zai magance satar fasahar waqa ko fim?

Ka san kowane mai sana’a yana yi don riba ce.  Alhamdulillahi, wannan sabuwar dabara nasara ce a cikin sana’armu, duk da yake ba za a rasa samun qananan abubuwa da za su riqa tasowa ba.

Ya alaqa take tsakaninku da Hukimar Tace Finafinai lura da cewa, yanzu ana sanya fim a YouTube mai yiwuwa ba tare da an kai mata, ta tantance fim xin ba?

Gaskiya ni ban tava karo da su ba, domin ni duk abin da nake yi ina tabbatar da cewa na kare abin da addinina yake so na kuma kiyaye abin da ba ya so. Ka ga ba zan shiga wani layi ba da na san abin zai kawo min zubar da mutuncina.

Bari mu koma kan waqa, ka ce ka haxa biyu fim da waqa wane vangare kake yi wa waqa ‘ya siyasa ko masu kuxi ko iya ta fim ka tsaya?

Gaskiya na fi mayar da hankali a waqoqin gambara, wato Hiphop na Hausa. Akwai albom da nake aiki a kansa na wasu sababbin waqoqin da na yi wanda na gambara ne gaba xaya.

Kuma kwalliya na biyan kuxin sabulu ?

Alhamdulillahi.

Wacce shawara kake xauke da ita ga masu tasowa don su mayar da hankali a kan abin da suka sa gaba?

Shawarata ita ce su mayar da hankali su tabbatar sun cim ma burinsu.

 

Tauraron Finanfinan Indiya na Bollywood, Dharmendra ya rasu yana da shekara 89

Dharmendra ya rasu ranar Litinin a wani asibiti a birnin Mumbai na Indiya bayan gajeruwar rashin lafiya.

Firayim Ministan Indiya, Narendra Modi ya yi ta’aziyyar jarumin a cikin, yana mai cewa rasuwarsa “ta kawo babban givi a Masana’antar Fim ta Indiya”.

An haifi tsohon tauraron Bollywood a ranar 8 ga Disambar 1935 a qauyen Nasrali da ke Gundumar Ludhiana ta Punjab.

Mahaifinsa malamin makaranta ne, kuma shi ya sanya masa suna Dharam Singh Deol.

A lokacin rayuwarsa, Dharmendra ya bayyana kansa a matsayin “mutum mai sauqin kai”, wanda ya sami qauna da aminci daga miliyoyin magoya bayansa.

Ya taka rawar gani da dama, amma an fi sanin sa da Veeru, a cikin fim xin Sholay na 1975. Duk da haka, Dharmendra ya fito a finafinai sama da 300 da waqoqi da yawa,waxanda suka ja hankalin masu kallo tsawon shekaru da yawa.

A wani lokaci, jarumin, wanda aka tava yi masa laqabi da “Asalin Mutumin Bollywood” da “Garam  wato mai zafin nama”, ya shiga jerin “mazaje mafi kyau” a duniya a lokacin da ya kai qololuwar nasararsa; kuma akasarin magoya bayansa mata ne, inda ta kai har  suna kwana da hotunansa a qarqashin matashin kansu.

Ya bar mata biyu Prakash Kaur da Hema Malini da ‘ya’ya shida, Sunny Deol da Bobby Deol da Esha Deol da Ahana Deol da Vijeta da Ajeeta Deol da kuma jikoki goma sha uku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio