Leadership News Hausa:
2025-11-27@04:36:49 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Published: 8th, March 2025 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Ruwan kanwa wani ruwa ne da akeyiwa mai azumi yanada dadi sosai sannan idan mai azumi ya sha bayasa kasala yana warware cikin ko hanji cikin mutum zance, idan mai azumi yasaba da shan ruwan kanwa duk randa baisha ba bazai taba jin dadi ba.

Ya ake ruwan kanwa?

Da farko za ki samu gero sai a surfashi a cire masa dusa sannan a wankeshi a shanyashi yasha iska wato ya bushe sosai sai kidan soyashi yayi kanshi haka sannan ki zuba masa kayan kamshi citta, kanunfari, musuru, saiki bayar a nikamiki shi yayi laushi sosai kamar na kunu kizo ki shanyashi ya bushe sai ki ajiyeshi duk idan zaki dama saiki diba ki zuba a wani dan bokiti haka sai ki damashi da dan ruwan kanwa dama kin dora ruwa a wuta kamar de yadda zakiyi kunu idan ruwa ya tafasa saiki kashe shi kidan barshi yasha iska saboda karyazama kunu saiki zuba sannan ki zuba can suga haka saiki ajiyeshi haka ake shanshi da dumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere

Yundunar ’Yan Sandan Jihar Borno ta tabbatar da cewa ɗaya daga cikin ’yan mata 14 da ƙungiyar ISWAP ta sace a Ƙaramar Hukumar Askira-Uba ta kuɓuta, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano sauran 13.

A sanarwar da ya fitar dangane da irin ƙoƙarin da Jami’an tsaron ke yi na ceto sauran ‘yan matan 13 da ke hannun ‘yan ta’addan, kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce, shugaban gundumar Huyum ya bayar da rahoto a ranar Asabar 22 ga Nuwamba cewa waxanda ake zargin mayaƙan Ƙungiyar ISWAP ne suka sace ‘yan matan, yayin da suke aiki a wata gona a gundumar Mussa.

Tawagar ’yan sanda, sojoji, Sibiliyan JTF, da mafarauta da ’yan banga nan da nan suka fara aikin bincike don ceto ’yan matan.

“Ɗaya daga cikin waxanda abin ya shafa ta tsira ba tare da wata matsala ba a lokacin aikin kuma an ceto ta,” in ji Daso.

Mayaƙan Boko Haram sun file kan mata 2 a Borno Sace ɗalibai: Idan ba zai iya ba ya sauka kawai— PDP

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Naziru Abdulmajid, ya yi kira ga mazauna yankin da su kasance masu lura yayin da hukumomin tsaro ke ƙara himma wajen ƙoƙarin ceto sauran ‘yan matan.

Sanarwar ta ce, “Ana shawartar manoma da mazauna yankin da su yi aiki a yankunan da jami’an tsaro ke sintiri,” in ji sanarwar.

Rundunar ta ce za a samar da ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da aikin gano wurin da waɗannan mata suke.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan
  • Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
  • Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare  
  • Sace ɗalibai: Idan Tinubu ba zai iya ba ya sauka kawai — PDP
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162