Leadership News Hausa:
2025-12-12@01:54:09 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Published: 8th, March 2025 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Ruwan kanwa wani ruwa ne da akeyiwa mai azumi yanada dadi sosai sannan idan mai azumi ya sha bayasa kasala yana warware cikin ko hanji cikin mutum zance, idan mai azumi yasaba da shan ruwan kanwa duk randa baisha ba bazai taba jin dadi ba.

Ya ake ruwan kanwa?

Da farko za ki samu gero sai a surfashi a cire masa dusa sannan a wankeshi a shanyashi yasha iska wato ya bushe sosai sai kidan soyashi yayi kanshi haka sannan ki zuba masa kayan kamshi citta, kanunfari, musuru, saiki bayar a nikamiki shi yayi laushi sosai kamar na kunu kizo ki shanyashi ya bushe sai ki ajiyeshi duk idan zaki dama saiki diba ki zuba a wani dan bokiti haka sai ki damashi da dan ruwan kanwa dama kin dora ruwa a wuta kamar de yadda zakiyi kunu idan ruwa ya tafasa saiki kashe shi kidan barshi yasha iska saboda karyazama kunu saiki zuba sannan ki zuba can suga haka saiki ajiyeshi haka ake shanshi da dumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa

Daga Usman Muhammad Zaria

Ma’aikatar mata da walwalar jama’a ta jihar Jigawa za ta kashe naira milyan dubu 10 da milyan 599 wajen gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a sabuwar shekara.

Kwamishinar ma’aikatar, Hajiya Hadiza Abdulwahab, ta bayyana hakan lokacin kare kiyasin kasafin kudin ma’aikatar a gaban kwamatin harkokin mata na majalisar dokokin jihar Jigawa.

A cewar ta, za su mayar da hankali wajen inganta shirye shiryen bunkasa rayuwar mata da al’amuran da su ka jibinci kananan yara domin bada kariya ga masu rauni a cikin al’umma.

Hajiya Hadiza Abdulwahab ta ce ma’aikatar ta samu nasarori wajen aiwatar da tanade tanaden kasafin kudin 2025, yayin da za su ci gaba da daukar matakan da su ka dace domin inganta ayyukan su a sabuwar shekara.

Ta kuma yi nuni da cewar, batun kula da rayuwar masu rauni a cikin al’umma ya kasance ginshiki daga cikin kudurorin Gwamna Malam Umar Namadi.

Hajiya Hadiza, ta bada tabbacin aiki tukuri domin samun nasarar da ake bukata a sabuwar shekara.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Kamfanin Mangal ya kori direba kan dauko yara 21 da aka kama a Kogi
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”