Leadership News Hausa:
2025-03-17@23:49:49 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Published: 8th, March 2025 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Ruwan kanwa wani ruwa ne da akeyiwa mai azumi yanada dadi sosai sannan idan mai azumi ya sha bayasa kasala yana warware cikin ko hanji cikin mutum zance, idan mai azumi yasaba da shan ruwan kanwa duk randa baisha ba bazai taba jin dadi ba.

Ya ake ruwan kanwa?

Da farko za ki samu gero sai a surfashi a cire masa dusa sannan a wankeshi a shanyashi yasha iska wato ya bushe sosai sai kidan soyashi yayi kanshi haka sannan ki zuba masa kayan kamshi citta, kanunfari, musuru, saiki bayar a nikamiki shi yayi laushi sosai kamar na kunu kizo ki shanyashi ya bushe sai ki ajiyeshi duk idan zaki dama saiki diba ki zuba a wani dan bokiti haka sai ki damashi da dan ruwan kanwa dama kin dora ruwa a wuta kamar de yadda zakiyi kunu idan ruwa ya tafasa saiki kashe shi kidan barshi yasha iska saboda karyazama kunu saiki zuba sannan ki zuba can suga haka saiki ajiyeshi haka ake shanshi da dumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump

Gwamnatin kasar Amurka ta ce bata bukatar samuwar jkadan kasar Afrika ta kudu Ebrahim Rasool a kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Jumma’a, ya kuma kara da cewa Rasool mutum ne wanda yake nuna wariya, yake kuma kin Amurkawa. Don haka bama da abinda zamu tattauna da shi, kawai bama son ganinsa a cikin kasar babba.

Rubio bai bayyana dalilan daukar wannan matakin a kan jakadan ba, amma hakan ya faru ne bayan da Jakadan Rasool ya wata cibiyar bincike na Afrika ta kudu inda a jawabin da ya gabatar ya zargi shugaban kasar Amurka Donal Trump da, da samar da shirin “sake maida Amurka kasa babba” da wani shirin fifita fararem Amurka  a kan sauran mutane a duniya.

Labarin ya kara da cewa tun lokacinda Trump ya sake dawowa fadar white house aka hana jakadan Afirka ta kudu a kasar ganawa da jami’an fadar white House kamar yadda ya dace. Fakon haka Amurka ta yi barazanar dakatar da tallafin da take bawa kasar Afrika ta kudu saboda karar da ta shigar kan HKI wacce ta aiwatar da kissan kiyashi kan Falasdinawa a Gaza daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 har zuwa yanzun. Banda haka kasar ta sami goyon baya daga kasashen duniya da dama. Kuma gwamnatin Amurka ta bukata Afirka ta kudu ta janye karar amma taki amincewa.

Ya zuwa yanzu dai kotun ta ICC ta fidda sammacin kama Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministansa na Tsaro Yauf Galant. Kafin haka dai Ebrahim Rasool ya taba zaman jakadan Afrika ta kudu a kasarAmurka daga shekara ta 2010-2015 a lokacin shugabancin Barak Obama

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sudan sun sanar da samun gagarumin ci gaba a tsakiyar Khartoum
  • Madalla da hutu ga ’yan makaranta domin azumi
  • Yadda za a girka ‘Kamoniya’
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  • Hasashen Samun Ruwan Sama A 2025: Shawarwarin Da Kwararru Suka Bai Wa Manoma
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 102
  • Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa
  • Jim Ratcliffe Ya Ce Zai Iya Barin Manchester United Idan Aka Ci Gaba Da Cin Zarafinsa
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho
  • Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump