Leadership News Hausa:
2025-12-07@00:37:19 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Published: 8th, March 2025 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Ruwan kanwa wani ruwa ne da akeyiwa mai azumi yanada dadi sosai sannan idan mai azumi ya sha bayasa kasala yana warware cikin ko hanji cikin mutum zance, idan mai azumi yasaba da shan ruwan kanwa duk randa baisha ba bazai taba jin dadi ba.

Ya ake ruwan kanwa?

Da farko za ki samu gero sai a surfashi a cire masa dusa sannan a wankeshi a shanyashi yasha iska wato ya bushe sosai sai kidan soyashi yayi kanshi haka sannan ki zuba masa kayan kamshi citta, kanunfari, musuru, saiki bayar a nikamiki shi yayi laushi sosai kamar na kunu kizo ki shanyashi ya bushe sai ki ajiyeshi duk idan zaki dama saiki diba ki zuba a wani dan bokiti haka sai ki damashi da dan ruwan kanwa dama kin dora ruwa a wuta kamar de yadda zakiyi kunu idan ruwa ya tafasa saiki kashe shi kidan barshi yasha iska saboda karyazama kunu saiki zuba sannan ki zuba can suga haka saiki ajiyeshi haka ake shanshi da dumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa tsohon shugaban rundunar sojin ruwa kuma tsohon Kantoman jihar Ribas, Ibok-Ete Ekwe Ibas a matsayin Jakadan Najeriya.

Tinubu ya kuma naɗa Ita Enang, tsohon sanata da uwargidan tsohon gwamnan jihar Imo Chioma Ohakim da tsohon ministan cikin gida kuma tsohon shugaban rundunar sojin ƙasa Abdulrahman Dambazau, a matsayin jakadun.

’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Sunayensu nasu na zuwa ne ’yan kwanaki bayan Tinubu ya aike wa Majalisar Dattijai jerin farko na waɗanda yake son nadawa a matsayin jakadun.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar sabbin naɗe-naɗen a gaban majalisar a yayin zamanta na ranar Alhamis.

A cikin wasikar, shugaban ƙasa ya roƙi ’yan majalisa da su yi gaggawar duba sunayen domin bai wa gwamnati damar cike muhimman guraben jakadun.

Akpabio ya mika jerin sunayen ga kwamitin majalisar dattawa kan harkokin ƙasashen waje, tare da umarnin cewa kwamitin ya kammala tantancewa ya kuma dawo da rahoto cikin mako guda.

Shugaban ƙasa a baya ya naɗa tsohon mai ba da shawara na fadar shugaban ƙasa Reno Omokri da tsohon ministan sufurin jiragen sama Femi Fani-Kayode da tsohon shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin jakadu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro