Sin Za Ta Buga Karin Haraji Kan Wasu Hajojin Canada Da Ake Shigarwa Kasar Bayan Kammalar Bincike
Published: 8th, March 2025 GMT
Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta sanar a Asabar din nan cewa, za ta kara haraji kar kaso 100 kan wasu kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga Canada, bayan da ta kammala bincike kan batun nuna banbanci a hada-hadar cinikayya.
Harajin zai fara aiki ne tun daga ranar 20 ga watan nan na Maris, zai kuma kunshi karin kaso 100 bisa mai rapeseed, da tunkuza, da waken peas, yayin da kuma albarkatun teku, da naman alade da ake shigarwa Sin daga Canada, aka yi musu karin harajin kaso 25 bisa dari.
Mahukuntan kasar Sin sun ce matakin ya biyo bayan binciken da aka gudanar game da nuna banbanci a hada-hadar cinikayya, wanda ya tabbatar da cewa, matakan da kasar Canada ta dauka kan hajojin Sin da ake shigarwa kasar sun haifar da cikas, ga harkokin cinikayyar da aka saba gudanarwa tsakanin sassan biyu, kana sun illata halastacciyar moriyar kamfanonin kasar Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani mutum, mai shekaru 35 daga ƙauyen Kunji da ke Kwadon, bisa zargin mallakar jabun kuɗi.
Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama Kawu ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025, a ofishin ’yan sanda na Lawanti, sannan aka kai shi ofishin Amada domin ci gaba da bincike.
Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugabaYa ce an samu dalar Amurka 1,000 da ake zargin na bogi ne (kimanin Naira miliyan 1.5), da kuma Naira 10,000 a cikin kayansa.
A yayin bincike, Kawu ya amsa cewa kuɗin na wani mutum ne.
’Yan sanda sun ce suna ci gaba da bincike domin gano wanda ya ba shi kuɗin.
Rundunar ta kuma ce za ta ci gaba da yaƙar masu ta’ammali da jabun kuɗi tare da tabbatar da cewa za ta sanar da jama’a yadda binciken ke tafiya.