Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta sanar a Asabar din nan cewa, za ta kara haraji kar kaso 100 kan wasu kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga Canada, bayan da ta kammala bincike kan batun nuna banbanci a hada-hadar cinikayya.

Harajin zai fara aiki ne tun daga ranar 20 ga watan nan na Maris, zai kuma kunshi karin kaso 100 bisa mai rapeseed, da tunkuza, da waken peas, yayin da kuma albarkatun teku, da naman alade da ake shigarwa Sin daga Canada, aka yi musu karin harajin kaso 25 bisa dari.

Mahukuntan kasar Sin sun ce matakin ya biyo bayan binciken da aka gudanar game da nuna banbanci a hada-hadar cinikayya, wanda ya tabbatar da cewa, matakan da kasar Canada ta dauka kan hajojin Sin da ake shigarwa kasar sun haifar da cikas, ga harkokin cinikayyar da aka saba gudanarwa tsakanin sassan biyu, kana sun illata halastacciyar moriyar kamfanonin kasar Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zanga: Jami’an tsaro sun kafa shingayen bincike a wajen Abuja

Rundunar sojin da ke tsaron shugaban ƙasa da ’yan Sanda sun kafa shingayen bincike a manyan hanyoyin shiga Abuja da fata Abuja.

Matakin ya biyo bayan zanga-zangar neman a sako jagoran ƙungiyar ta’addanci ta IPOB, masu neman ɓallewa daga Najeriya, Nnamdi Kanu.

Zanga-zangar na zuwa ne a yayin da ake zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, har aka tsare wasu manyan sojoji aƙalla 16 da ake zargin wani tsohon gwamna ya ɗauki nauyinsu juyin mulkin suka shirya aiwatarwa.

Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta musanta zargin alhali wasu majiyoyi masu tushe sun tabbatar mana da gaskiyar zargin yunƙurin.

Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya Jami’an tsaro sun buɗe wa masu zanga-zangar Nnamdi Kanu wuta a Abuja

A safiyar Litinin ɗin nan ne Omoyele Sowore, jagoran tafiyar #RevolutionNow, ya jagoranci zanga-zangar neman sakin Nnamdi Kanu a sassan Abuja.

Zanga-zangar ta haddasa cunkoson ababen hawa a wurare da dama da suka hada da yankin Bwari, Zuba, Nyanya da sauran hanyoyin shiga birnin Abuja.

Musamman, an rufe hanyar da ke haɗa Bwari da Tsakiyar Birni a yankin War College da ke Ushafa, da kuma Dutse-Sokale, abin da ya sa ma’aikatan gwamnati da dama suka maƙale a hanya.

Da fari, jami’an tsaro sun taƙaita tsauraran matakai ne a wuraren da suka haɗa da Fadar Shugaban Kasa, Majalisar Tarayya, Kotun Daukaka Kara, Hedikwatar ’Yan Sanda ta Kasa, da kuma Dandalin Eagle Square.

Sai dai wata majiya daga hukumar tsaro ta shaida wa wakilinmu cewa faɗaɗa shingayen zuwa unguwannin da ke wajen birnin ya zama dole domin hana “’yan kutse daga waje” shiga cikin birnin.

“Yanzu ana binciken kowace mota da ke shigowa cikin birni. Wannan mataki ne domin bambance masu neman tayar da fitina da ’yan ƙasa na gari. Ba za mu yarda a samu tashin hankali a cibiyar gwamnati ba,” in ji majiyar.

Wani jami’in tsaro ya kuma bayyana cewa bayanan sirri sun nuna masu zanga-zangar na sake tsara dabaru tare da yiwuwar shigo da wasu matasa zauna-gari-banza domin tayar da da tarzoma.

Wani ma’aikacin gwamnati, Isaac Babalola, ya shaida wa wakilinmu cewa ya koma gida bayan ya maƙale na tsawon lokaci a cunkoson motoci a kusa da War College Camp da ke Ushafa.

“Ana tsayawa ana binciken kowace mota sosai, abin ya haddasa cunkoso mai tsanani,” in ji shi.

Haka kuma, wasu direbobi da suka taso daga Mararaba–Nyanya sun bayyana takaici, suna cewa sun karaya saboda ba su shirya irin wannan tsaiko ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
  • Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
  • Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana
  • Zanga-zanga: Jami’an tsaro sun kafa shingayen bincike a wajen Abuja
  • Gwamnatin Colombia Ta Bukaci Bayani Daga Amurka Kan Kashe Wani Dan Kasar A Tekun Carabian
  • Gwamnatin Colombia Ta Bukatci Bayani Daga Amurka Kan Kashe Wani Dan Kasar A Tekun Carabian
  • Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan
  • Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka
  • Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba