Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol
Published: 8th, March 2025 GMT
Wata kotu a Koriya ta Kudu, ta saki tsohon shugaban ƙasar, Yoon Suk Yeol, bayan da ta yi watsi da kama shi, duk da cewa ana ci gaba da bincike kan zargin da ake masa.
Yoon, wanda aka dakatar daga mulki, an tsare shi ne tun a watan Janairu bayan da ake zarginsa da ƙoƙarin kifar da mulkin farar hula.
Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a KebbiA ranar 3 ga watan Disamban 2024, jami’an tsaro sun kai masa samame bisa zargin tayar da zaune tsaye.
Bayan an sake shi, Yoon ya fito daga gidan yari yana murmushi, sannan ya sunkuyar da kai domin nuna godiya ga magoya bayansa da suka zo ganinsa.
A ranar Juma’a, kotu ta soke umarnin da aka bayar na kama shi, inda ta ce babu isassun hujjoji da ke tabbatar da laifin da ake zarginsa da shi.
Duk da haka, ana ci gaba da shari’a kan batun tsige shi daga mulki.
Masu gabatar da ƙara sun ce za su mayar da hankali kan gabatar da hujjoji a gaban kotu maimakon ɗaukaka ƙara kan sakinsa.
Idan har kotun tsarin mulki ta tabbatar da tsige shi, Koriya ta Kudu dole ne ta gudanar da sabon zaɓen shugaban ƙasa cikin kwanaki 60.
Duk da haka, ana sa ran za a ci gaba da shari’ar Yoon, ko da kuwa an sauke shi daga mulki gaba ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Koriya ta Kudu zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
“An zabo Abubakar Dantsoho ne, daga cikin sauran wadanda aka karamma da lambar yabon bisa kokarin da yake ci gaba da yi, na bunkasa fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar wanda hakan ya sanya, aka kara samun fitar da kaya daga kasar nan, ta hanyar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa dIMODantsohoa tsarin NSW ta hanyar yin amfani da dabarar PCS domin janyo ra’ayin masu zuba jari daga ketare a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, da aka samar da kayan aiki na zamani, ” Inji sanarwar.
“Akawi kuma batun kara daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar a tsakanin hukumomin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma wato PMAWCA da kuma zabar Dantsoho, a matsayin mataimakin shugaban kungiyar masu tafiyar da hukumomin Jiragen Ruwa na kasa da kasa wato IAPH,” A cewar sanarwar.
Hukumar ta NPA ta bayyana cewa, a karkashin shugabancin Dantsoho tare da taimakawar ministan bunkasa tattalin arziki na teku Adegboyega Oyetola, an sake zabar Nijeriya, zuwa mataki na C a karkashin kungiyar kasa da kasa ta tafiyar da harkar sufurin Jiragen Ruwa wato IMO.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA