Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol
Published: 8th, March 2025 GMT
Wata kotu a Koriya ta Kudu, ta saki tsohon shugaban ƙasar, Yoon Suk Yeol, bayan da ta yi watsi da kama shi, duk da cewa ana ci gaba da bincike kan zargin da ake masa.
Yoon, wanda aka dakatar daga mulki, an tsare shi ne tun a watan Janairu bayan da ake zarginsa da ƙoƙarin kifar da mulkin farar hula.
Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a KebbiA ranar 3 ga watan Disamban 2024, jami’an tsaro sun kai masa samame bisa zargin tayar da zaune tsaye.
Bayan an sake shi, Yoon ya fito daga gidan yari yana murmushi, sannan ya sunkuyar da kai domin nuna godiya ga magoya bayansa da suka zo ganinsa.
A ranar Juma’a, kotu ta soke umarnin da aka bayar na kama shi, inda ta ce babu isassun hujjoji da ke tabbatar da laifin da ake zarginsa da shi.
Duk da haka, ana ci gaba da shari’a kan batun tsige shi daga mulki.
Masu gabatar da ƙara sun ce za su mayar da hankali kan gabatar da hujjoji a gaban kotu maimakon ɗaukaka ƙara kan sakinsa.
Idan har kotun tsarin mulki ta tabbatar da tsige shi, Koriya ta Kudu dole ne ta gudanar da sabon zaɓen shugaban ƙasa cikin kwanaki 60.
Duk da haka, ana sa ran za a ci gaba da shari’ar Yoon, ko da kuwa an sauke shi daga mulki gaba ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Koriya ta Kudu zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
Bayan da ƙasashen biyu maƙwabtan juna na Congo da Rwanda suka sanya hannu a yarjejeniyar zaman lafiya da Donald Trump ya bayyana a matsayin mai cike da tarihi, jagoron na Amurka ya jinjinawa shugabannin ƙasashen biyu waɗanda ya ce sun yi hangen nesa wajen amincewa da kawo ƙarshen zubar da jinin dubban mutane tsawon shekaru.
An dai haska wannan zaman sanya hannu kai tsaye ta gidajen talabijin, inda shugabannin biyu wato Felix Tshisekedi na Jamhuriyyar Congo da Paul Kagame na Rwanda suka rattaɓa hannu a yarjejeniyar a gaban idon Donald Trump can a birnin Washington.
A cewar Trump shugabannin biyu sun ajje banbance-bambancen da ke tsakaninsu wajen rungumar zaman lafiya don jama’arsu.
Sai dai an sanya hannu a yarjejeniyar can a Washington dai dai lokacin da ake ganin ci gaban yaƙi tsakanin Sojin Congo da mayaƙan M23 da Rwanda ke marawa baya a kudancin lardin Kivu.
Babu dai wakilcin M23 a wannan tattaunawa ta Washington, hasalima basu aminta da yarjejeniyar da ka cimma a zaman ba, maimakon haka suna halartar nasu taron na daban wanda Qatar ke jagorantar sulhunta su da Congo a birnin Doha.
Masu sharhi na ganin abu ne mai matuƙar wahala, yarjejeniyar ta birnin Washington ta yi tasiri wajen kawo ƙarshen wannan yaƙi na shekaru.
Yarjejeniyar na zuwa a dai dai lokacin da Amurka ke son zuba jari a ɓangaren haƙar ma’adinai a Congo inda a gefe guda itama Qatar ke faɗaɗa shirinta na zuba jari a ƙasashen Afrika.