Aminiya:
2025-12-14@01:36:31 GMT

Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol

Published: 8th, March 2025 GMT

Wata kotu a Koriya ta Kudu, ta saki tsohon shugaban ƙasar, Yoon Suk Yeol, bayan da ta yi watsi da kama shi, duk da cewa ana ci gaba da bincike kan zargin da ake masa.

Yoon, wanda aka dakatar daga mulki, an tsare shi ne tun a watan Janairu bayan da ake zarginsa da ƙoƙarin kifar da mulkin farar hula.

Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a Kebbi

A ranar 3 ga watan Disamban 2024, jami’an tsaro sun kai masa samame bisa zargin tayar da zaune tsaye.

Bayan an sake shi, Yoon ya fito daga gidan yari yana murmushi, sannan ya sunkuyar da kai domin nuna godiya ga magoya bayansa da suka zo ganinsa.

A ranar Juma’a, kotu ta soke umarnin da aka bayar na kama shi, inda ta ce babu isassun hujjoji da ke tabbatar da laifin da ake zarginsa da shi.

Duk da haka, ana ci gaba da shari’a kan batun tsige shi daga mulki.

Masu gabatar da ƙara sun ce za su mayar da hankali kan gabatar da hujjoji a gaban kotu maimakon ɗaukaka ƙara kan sakinsa.

Idan har kotun tsarin mulki ta tabbatar da tsige shi, Koriya ta Kudu dole ne ta gudanar da sabon zaɓen shugaban ƙasa cikin kwanaki 60.

Duk da haka, ana sa ran za a ci gaba da shari’ar Yoon, ko da kuwa an sauke shi daga mulki gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Koriya ta Kudu zargi

এছাড়াও পড়ুন:

BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40

Kamfanin samar da siminti na BUA ya bayar da tallafin karatu Naira miliyan 40 ga ɗalibai 200 da ke manyan makarantu a jihohin tsohuwar Jihar Sakkwato.

An bayar da tallafin domin ganin sun cimma burinsu a fannin ilmi.

An kai hari gidan jami’in ɗan sanda a Yobe Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota

Ɗaliban da suka ci gajiyar sun haɗa da matasa 50 daga Sakkwato, 50 daga Kebbi da 50 daga Zamfara, sai 50 a Wamakko inda cibiyar kamfanin simintin yake.

Kowane ɗalibi zai karɓi Naira dubu 200, an samu ninkin ɗaliban kuɗin ma an samu ƙari da kashi 100 bisa ga shekarun baya.

Shugaba kuma Daraktan kamfanin, Injiniya Yusuf Binji ya ce sun ninka yawan ɗalibai daga 100 zuwa 200 haka kuɗin daga dubu 100 zuwa 200.

Injiniya Binji ya bayyana tallafin karatun matsayin saka jari ne da zai samar da al’ummar mai ɗorawa a gaba.

Ya yi kira ga waɗanda suka ci gajiyar su yi abin da ya dace kuma kamfani zai bibiyi karatunsu.

Shugaban Kamfanin na BUA ya gode wa gwamnatin jiha kan samar musu filin kasuwanci ba tsangwama.

Mai baiwa Gwamanan Sakkwato shawara, Honarabul Usman Arzika Fako ya ce tallafin zai bunƙasa ilmi da samar da aikin yi ga matasa.

Ya yaba wa kamfanin ga wannan hoɓɓasar, akwai buƙatar a duba wasu ɓangarori suma a yi abin da ya kamata.

Balkisu Bello Muhammad, ɗaliba daga Kebbi ta bayyana BUA ginshiƙi ne na samar da cigaba ta gode wa kamfanin kan wannan saka jarin da suka yi da za su ci gajiyarsa a gaba.

Umar Bello ɗalibi daga Zamfara ya nuna farin cikinsa ga kamfanin yadda ya ɗaga karatunsa zai samu nasara a gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki
  • Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige