Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ, FRCN Kaduna Chapel, ta jaddada kudirinta na inganta jin dadin mambobinta ta hanyar bullo da sabbin tsare-tsare da shirye-shiryen tallafi.

Shugaban kungiyar, Kwamared Umar Adamu Sarikin Fada ne ya bayyana haka a lokacin rabon kayan abinci na Ramadan ga ‘yan kungiyar a Kaduna.

Umar Adamu Sarikin Fada ya bayyana cewa shirin rabon kayayyakin na daga cikin dabarun da kungiyar ta keyi na dakile tasirin tabarbarewar tattalin arzikin kasar nan.

Ya tabbatar da cewa sama da ‘yan uwa Musulmi dari da hamsin ne suka ci gajiyar shirin na watan Ramadan na bana, inda ya jaddada cewa su ma Kirista na kungiyar sun samu irin wannan tallafi a lokacin bukukuwan Kirsimeti na 2024.

Shugaban ya kuma yi kira ga mambobin kungiyar da su sake sadaukar da kansu wajen gudanar da ayyukansu domin ci gaban FRCN da kasa baki daya.

REL/MANSUR S PAKI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 
  • Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
  • Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu
  • Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
  • Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
  • Jami’in Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12
  • Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
  • Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka