An Yi Kira Ga Al’ummar Musulmi Da Su Kara Yawan ‘Ya’yan Itatuwa Da Sha A Ramadan
Published: 6th, March 2025 GMT
An yi kira ga al’ummar musulmi da su kara yawan ruwa da ‘ya’yan itatuwa a lokacin azumin watan Ramadan domin inganta sinadaran jiki.
Wani kwararre a fannin lafiya a Jami’ar Ilorin, Farfesa AbdulRahman Afolabi ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Ilorin, jihar Kwara.
Ya ce a lokacin azumi da ake tsananin zafi a hankali ruwan jiki yana raguwa.
A cewarsa karuwar cin ‘ya’yan itatuwa daban-daban zai yi matukar amfani ga musulmi mai azumi.
Farfesa Afolabi ya bayyana cewa a lokacin azumin watan Ramadan musulmi sun kaurace wa abinci da abin sha, tare da hana jikinsu cin abinci da suka saba.
Ya ba da shawarar a kara amfani da ‘ya’yan itatuwa irin su kankana, karas, da lemu domin dawo da abin da jiki ya rasa.
Farfesa Afolabi ya ci gaba da cewa sanya ‘ya’yan itatuwa a cikin abincinmu na iya samar da kuzari, da sinadirai masu mahimmanci, da kuma samar da ruwa don kiyaye jiki da kuzari a lokacin azumin Ramadan.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara ya yan itatuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp