Shugaban SWAN Ya Kafa Kwamatin Hadin Gwiwa Kan Harkar Zuba Jari
Published: 6th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar marubuta wasanni ta kasa SWAN, Kwamared Isaiah Benjamin, ya bukaci sabon kwamitin hadin gwiwar SWAN da aka kaddamar da su farfado da kungiyar ta hanyar jawo masu zuba jari don tallafa wa marubutan wasanni a fadin kasar nan.
Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin kwamred Isaiah Benjamin ya jaddada mahimmancin karfafa kudi ga ‘yan jaridun wasanni, yana mai baiwa kwamitin ‘yancin gudanar da aiki yadda ya kamata.
“Aikin da ke gaba yana da girma, amma ina da yakinin iya karfin ku na karfafa tattalin arzikin marubutan wasanni a Najeriya ta hanyar hadin kai. Kuna da cikakken goyon bayanmu, ”in ji shi.
Ya bayyana cewa zaben ‘yan kwamitin wanda shugaban kungiyar SWAN na jihar Nasarawa, Kwamared Smah George ya jagoranta ya dogara ne da irin nasarorin da suka samu da kuma gudunmawar da suke baiwa kungiyar.
Da yake mayar da martani a madadin kwamitin, Comrade Smah George ya nuna godiya ga hukumar zartaswa ta kasa bisa wannan dama da aka ba shi, ya kuma yi alkawarin yin aiki tukuru tare da masu ruwa da tsaki domin cika aikin kwamitin.
“Za mu bincika dukkan hanyoyin da ake da su don fitar da saka hannun jari a cikin SWAN. Ina kira ga mambobin kwamitin da su ci gaba da jajircewa kan wannan aiki domin yana da matukar muhimmanci wajen inganta walwala da kwanciyar hankali na marubutan wasanni,” inji shi.
Sabbin mambobin kwamitin da aka kaddamar sun hada da Ijeoma Peter Nwante mai wakiltar Kudu maso Gabas, Austin Ajayi arewa maso gabas, Clarkson Ogo Kudu maso Kudu, Bisi Ogunleye Kudu maso yamma, Hassan Abubakar arewa ta tsakiya da kuma Jacob Enjewo arewa maso yammat, wanda zai zama sakatare.
Aliyu Muraki/Lafia.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Lafiya nasarawa Wasanni
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA
Kwamitin koli na tsaron kasa ya amince da yarjejeniyar da hukumar makamashin nukiliya ta duniya IAEA
Kwamitin koli na tsaron kasar Iran ya yi gargadin cewa, idan aka dauki wani mataki na nuna adawa ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran da cibiyoyinta na makamashin nukiliya, ciki har da sake farfado da kudurorin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da suka kare, za a dakatar da aiwatar da tsare-tsare da yarjejeniyoyin da aka kulla da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA.
Sakatariyar kwamitin tsaron kasar Iran ta fitar da wata sanarwa a jiya Lahadi, bayan yarjejeniyar da aka rattabawa hannu tsakanin Seyyed Abbas Araqchi da Rafael Grossi. An yi wannan bayani ne dangane da tsare-tsare da ministan harkokin wajen kasar da babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA suka rattabawa hannu dangane da tsarin mu’amala tsakanin Iran da IAEA bisa la’akari da sabbin yanayi da ake ciki bayan hare-haren soji da gwamnatin yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan cibiyoyin makamashin nukiliya na kasar Iran bisa tsarin kariya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci