Aminiya:
2025-06-22@15:39:08 GMT

NAJERIYA A YAU: Yadda za ku yi girke-girken azumi da kuɗi kaɗan

Published: 3rd, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yanayin tsadar rayuwa da ake ciki ya sa dole a yi tattalin kuɗin da ake kashewa.

An saba  a watan Ramadana ana yawan yin girke-girke da kayan buɗa-baki iri-iri, amma kuma wannan azumin ya zo cikin yanayi na matsin tattalin arziki.

NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

Shirin Najeriya a Yau ya duba hanyoyin da za ku yi girke-girken da yawa yadda aka saba cikin sauki ba tare da kashe maƙudan kuɗaɗe ba.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abincin Ramadan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

An yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a garin Mangu, da ke Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Waɗanda aka kashe sun haɗa da maza, mata da yara.

Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani Mahaifin Rahama Sadau ya rasu

Dukkaninsu mazauna unguwar Basawa-Anguwan Rimi ne da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.

Sun tashi ne daga Zariya zuwa Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure, amma aka kai musu hari a hanya.

An yi jana’izarsu tare da birne su da yammacin ranar Asabar a maƙabartar Hayi, ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro.

Malamai a Mangu sun ce iyalan mamatan sun amince a birne su a Filato domin kaucewa shiga tashin hankali a garinsu.

Kafin yi musu jana’iza, malamai sun roƙi Musulmai su ɗauki lamarin a matsayin ƙaddara daga Allah, su kuma guji ɗaukar doka a hannunsu.

Sheikh Suleiman Haruna, ɗaya daga cikin malamai a yankin da ya jagoranci jana’izar, ya buƙaci jama’a da su zauna lafiya tare da yin haƙuri da juna.

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya umarci jami’an tsaro da su kamo masu hannu a lamarin.

Ga hotunan yadda jana’izar ta wakana:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
  • ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
  • Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki