Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyararsa A Birtaniya Da Ireland Da Halartar Taron Kolin Kwamitin Sulhu Da Na Tsaro A Munich Da Na G20
Published: 23rd, February 2025 GMT
A jiya Asabar 22 ga wannan wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi bayani ga kafofin watsa labaru na kasar Sin bayan da ya kammala ziyararsa a Birtaniya da Ireland, da halartar taron kiyaye tsaro na Munich karo na 61, da shugabantar taron kolin kwamitin sulhun MDD a birnin New York, da kuma halartar taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G20 a kasar Afirka ta Kudu.
A matsayin kasar da take shugabantar kwamitin sulhun MDD a wannan wata, kasar Sin ta yi kira ga taron koli na kwamitin mai taken “Bin ra’ayin bangarori daban daban da yin kwaskwarima kan kyautata aiwatar da harkokin duniya”. Inda game da hakan, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi bayani game da ra’ayinta na kafa tsarin daidaita harkokin duniya cikin adalci, wato tabbatar da zaman daidaito kan ikon mallakar kasa, da tabbatar da adalci da yin hadin gwiwa da kuma bin taswirar aiwatar da ayyuka, kuma ra’ayin na kasar Sin ya samu amincewar kasashen da suka halarci taron.
Game da kara kaimin samar da yanayin dogaro da bangarori masu yawa maimakon daya tilo, Wang Yi ya yi nuni da cewa, yin hakan a duniya shi ne muhimmin ra’ayi da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, kuma shi ne kyakkyawan fatan da kasar Sin ta nuna wa duniya. Kana, kasar Sin za ta tabbatar da tsarin dogaro da bangarori masu yawa, da samar da gudummawa ga duniya yayin da ake fuskantar sauyin duniya.
Ban da wannan kuma, Wang Yi ya bayyana cewa, za a gudanar da taron kolin shugabannin kasashen kungiyar G20 a watan Nuwamban bana a nahiyar Afirka a karo na farko. Wannan shi ne lokacin da nahiyar Afirka ta samu cikakkiyar dama a kungiyar G20 da kuma aiwatar da harkokin duniya, wanda ya shaida cewa, shi ne babban canji a tarihi ga yanayin tattalin arziki da siyasa na duniya, kuma lamarin yana da babbar ma’ana. A gun taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G20 a wannan karon a birnin Johannesburg dake Afirka ta Kudu kuwa, kasar Sin ta ce ya kamata a kara sauraron ra’ayin kasashen Afirka, da maida hankali ga batutuwan Afirka, da nuna goyon baya ga Afirka, da rike damar hadin gwiwa ta kungiyar G20 don sa kaimi ga samun ci gaba da wadata a nahiyar ta Afirka. Wannan ra’ayi ya samu amincewar kasa da kasa. (Zainab Zhang)
কীওয়ার্ড: kasar Sin ta kungiyar G20
এছাড়াও পড়ুন:
Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
Daga Salihu Tsibiri
Tsohon shugaban masu rinjaye na Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya bayyana tabarbarewar tsaro da ake fuskanta, wato ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma hare-haren ’yan bindiga, a matsayin barazana ga siyasar ƙasar nan gabanin zaɓen 2027.
Ya yi wannan tsokacin ne a jawabinsa yayin bude zaman taron musamman na yini biyu da Majalisar Wakilai ta shirya kan halin tsaro da ƙasar ke ciki.
Alhassan Ado Doguwa, wanda ya yaba da ayyukan da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanarwa, ya ce halin da Arewa ke ciki abin takaici ne ƙwarai, la’akari da yawan mutanen da ke hannun masu garkuwa da kuma waɗanda ke rayuwa cikin tsananin rashin tabbas.
Tsohon shugaban ya jaddada cewa duk da cewa su ma gwamnoni suna da alhakin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a tare da gwamnatin tarayya, lokaci ya yi da za a duba batun tsaro a matsayin barazana da ba ta da alaƙa da jam’iyya, addini ko ƙabila.
Ya kara da cewa idan matsalar tsaro ta ci gaba da ta’azzara, akwai bukatar a rufe majalisa gaba ɗaya tare da ayyana dokar ta-baci, har sai an ɗauki matakin gaggawa don kare ƙasar daga halin da take ciki.
A nasa bangaren, shugaban kwamitin majalisar kan harkokin ’yan sanda, Makki Abubakar Yalleman, ya bayyana tsaro a matsayin alhakin kowa, inda ya yaba wa umarnin shugaban ƙasa na janye ’yan sanda daga wasu manyan mutane domin ƙara ƙarfi a yaki da laifuka a fadin ƙasar.
Sai dai Makki Yalleman ya yi kira da a samar da isasshen kuɗi da na’urorin zamani domin inganta ƙwarin gwiwa da ƙwarewar rundunar ’yan sandan Najeriya a yakin da take yi da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ’yan bindiga.
A nasa bangaren, shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda, ya danganta matsalolin tsaro da ake fuskanta ga gazawar bangarorin gwamnati uku wajen tabbatar da bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki, musamman kan ta’addanci, garkuwa da mutane, ’yan bindiga da kuma masu yi wa gwamnati tawaye.