Aminiya:
2025-06-27@00:35:41 GMT

Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba

Published: 23rd, February 2025 GMT

Jami’ar Sojojin Nijeriya da ke Biu (NAUB) ta ƙaddamar da taron magance zamba ta hanyar binciken fasaha karo na farko, wanda ya nuna ƙaruwar tasirin wannan jami’a a fagen ilimi a Nijeriya.

Taron ya gudana ne bisa taken “Kididdigar Forensic: Zuwa Ga Sabon Tsarin Magance da Gano Zamba,” wanda Farfesa Ahmad Imam, ƙwararre a fannin ƙididdigar kuɗi da magance zamba ya gabatar.

Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen Mai Pataskum ya buɗe masallacin garin Danga a Yobe

Tattaunawar ta jaddada dabarun zamani domin tunkarar zamba mai salo da kuma tsare-tsaren da za su taimaka wajen gano da magance laifukan kuɗi da ke ƙara ƙamari.

Shugaban Jami’ar NAUB, Farfesa Kyari Mohammed, ya bayyana wannan taro a matsayin wani muhimmin mataki ga jami’ar.

A cewarsa: “Abin alfahari ne mu yi bikin wannan muhimmin taro na farko, wanda ke nuna jajircewar NAUB wajen habaka ilimi da warware matsalolin al’umma.”

Shugaban Kwamitin Shirya Taron, Farfesa Adamu Isa Harir, ya bayyana taron a matsayin wata al’ada mai cike da tarihi a fagen ilimi.

Ya ce: “Wannan taro ba wai kawai nasara ce ga jami’a ba, har ila yau, yana nuna muhimmancin bincike da kirkire-kirkire wajen kawo sauyi ga al’umma.”

Farfesa Ahmad Imam ya jaddada bukatar sabon salo wajen yakar zamba, tare da bayyana yadda zamani ke buƙatar sababbin hanyoyin daidaitawa da matsalolin laifukan kudi a duniya da ke sauyawa cikin sauri.

A jawabin godiya, Magatakardar Jami’ar, Birgediya Janar H.Y. Abdulhamid, ya gode wa dukkan wadanda suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar taron.

A cewarsa: “Muna matukar godiya da goyon bayan shugabannin jami’a da kuma kokarin ma’aikata wajen tabbatar da nasarar wannan taro.”

Haka kuma, Shugaban Sashen Kididdiga, Dakta S.J. Inyada, ya gabatar da kyauta ta musamman ga Farfesa Ahmad Imam a matsayin yabo kan gudunmawarsa a fannin kididdigar bincike ta hanyar fasahar zamani.

Dakta Inyada ya yaba wa Mataimakin Shugaban Jami’ar da shugabannin jami’a bisa jajircewarsu wajen inganta bincike da harkokin ilimi a jami’ar.

Wannan taro ba wai kawai ya zama wani babban ci gaba ga NAUB ba, har ila yau, ya tabbatar da alkawarin jami’ar na ci gaba da girmama bincike, kirkire-kirkire, da kawo sauyi mai ma’ana ga al’umma.

Wannan ya tabbatar da rawar NAUB a matsayin jagora wajen bunkasa bincike da ilimi a Nijeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Sojoji jihar Borno wannan taro

এছাড়াও পড়ুন:

An tallafawa iyalan jami’an ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta gabatar da cakin kuɗi Naira 13 da dubu ɗari 4 da 28 da ɗari 6 da 59.95 ga ’yan uwan ​​’yan sanda 10 da suka mutu a bakin aiki.

Taron gabatar da kuɗin wanda aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Maiduguri, na da nufin bayar da tallafin kuɗi ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana hakan ne manema labarai a hedikwatar rundunar da ke garin Maiduguri.

Kwamishinan ’yan sanda, CP Naziru Abdulmajid ne ya gabatar da jawabin a madadin Sufeto-Janar na ’yan sanda (IGP), Kayode Adeolu Egbetokun.

Wannan shiri yana ƙarƙashin Ƙungiyar ’yan sandan Najeriya (Group Assurance Life and IGP Welfare Scheme) wanda aka tsara don rage wahalhalun da iyalan ma’aikatan da suka yi sadaukarwa ke fuskanta.

Kwamishina Abdulmajid ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasu, yana mai tabbatar musu da jajircewar sufeto-janar na ’yan sanda na tabbatar da jin daɗin jami’an da ke aiki da kuma jaruman da suka mutu.

Ya jaddada cewa, sadaukarwar da waɗannan jami’an suka yi ba za a taɓa mantawa da su ba, kuma rundunar ta ci gaba cewa za ta ci gaba sadaukar da kai wajen tabbatar da jin daɗin iyalan da suka bari.”

Kwamishinan ’yan sandan ya kuma shawarci waɗanda suka ci gajiyar kuɗaɗen da su yi amfani da kuɗaɗen cikin adalci, inda ya buƙace su da su saka hannun jari a harkar kasuwanci mai ɗorewa da zai taimaka wajen tabbatar da makomar waɗanda suka mutu na jami’an na su.

Da yake jawabi a madadin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Jerry Joel ya bayyana matuƙar godiya ga rundunar ’yan sandan Najeriya da babban sufeton ’yan sandan ƙasar bisa goyon bayan da suka bayar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale a gare su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • An tallafawa iyalan jami’an ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
  • PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta
  • Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Bejjo Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027
  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC