Aminiya:
2025-10-13@17:49:59 GMT

Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba

Published: 23rd, February 2025 GMT

Jami’ar Sojojin Nijeriya da ke Biu (NAUB) ta ƙaddamar da taron magance zamba ta hanyar binciken fasaha karo na farko, wanda ya nuna ƙaruwar tasirin wannan jami’a a fagen ilimi a Nijeriya.

Taron ya gudana ne bisa taken “Kididdigar Forensic: Zuwa Ga Sabon Tsarin Magance da Gano Zamba,” wanda Farfesa Ahmad Imam, ƙwararre a fannin ƙididdigar kuɗi da magance zamba ya gabatar.

Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen Mai Pataskum ya buɗe masallacin garin Danga a Yobe

Tattaunawar ta jaddada dabarun zamani domin tunkarar zamba mai salo da kuma tsare-tsaren da za su taimaka wajen gano da magance laifukan kuɗi da ke ƙara ƙamari.

Shugaban Jami’ar NAUB, Farfesa Kyari Mohammed, ya bayyana wannan taro a matsayin wani muhimmin mataki ga jami’ar.

A cewarsa: “Abin alfahari ne mu yi bikin wannan muhimmin taro na farko, wanda ke nuna jajircewar NAUB wajen habaka ilimi da warware matsalolin al’umma.”

Shugaban Kwamitin Shirya Taron, Farfesa Adamu Isa Harir, ya bayyana taron a matsayin wata al’ada mai cike da tarihi a fagen ilimi.

Ya ce: “Wannan taro ba wai kawai nasara ce ga jami’a ba, har ila yau, yana nuna muhimmancin bincike da kirkire-kirkire wajen kawo sauyi ga al’umma.”

Farfesa Ahmad Imam ya jaddada bukatar sabon salo wajen yakar zamba, tare da bayyana yadda zamani ke buƙatar sababbin hanyoyin daidaitawa da matsalolin laifukan kudi a duniya da ke sauyawa cikin sauri.

A jawabin godiya, Magatakardar Jami’ar, Birgediya Janar H.Y. Abdulhamid, ya gode wa dukkan wadanda suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar taron.

A cewarsa: “Muna matukar godiya da goyon bayan shugabannin jami’a da kuma kokarin ma’aikata wajen tabbatar da nasarar wannan taro.”

Haka kuma, Shugaban Sashen Kididdiga, Dakta S.J. Inyada, ya gabatar da kyauta ta musamman ga Farfesa Ahmad Imam a matsayin yabo kan gudunmawarsa a fannin kididdigar bincike ta hanyar fasahar zamani.

Dakta Inyada ya yaba wa Mataimakin Shugaban Jami’ar da shugabannin jami’a bisa jajircewarsu wajen inganta bincike da harkokin ilimi a jami’ar.

Wannan taro ba wai kawai ya zama wani babban ci gaba ga NAUB ba, har ila yau, ya tabbatar da alkawarin jami’ar na ci gaba da girmama bincike, kirkire-kirkire, da kawo sauyi mai ma’ana ga al’umma.

Wannan ya tabbatar da rawar NAUB a matsayin jagora wajen bunkasa bincike da ilimi a Nijeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Sojoji jihar Borno wannan taro

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh

Shugaban kasar Amurka Donal Trunp ya isa HKI a safiyar yau Litinin, inda ake  saran zai yi jawabi a majalisar dokokin HKI, kafin ya wuce zasu Sharm sheikh na kasar Masar inda zai halarci bikin sanyawa yarjeniyar tsagaita wuta tsakanin kungiyar Hamas da kuma HKI wanda aka fara aiki da shi a wannan makon.

Tashar talabijin ta Al-mayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto hotunan bidiyo kai tsaye daga Telaviv a lokacinda jirgin shugaban kasar ya sauka, sannan shuwagaban HKI  da kuma firai ministan HK Benyamin Natanyahu ne suka tarbe shi a tashar jiragen sama na Bengerion.

Shugaban ya iso HKI a dai dai lokacinda kungiyar Hamas ta mika fursinonin HKI 7 ga kungiyar Red Cross a zirin Gaza. Wanda daya ne daga cikin matakan aiwatar da yarjeniyar sulhu a HKI .

Tun 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ne har zuwa watan octoban shekara ta 2025 sojojin HKI sun kashe Falasdinawa kimani 70,000 tare da tallafin Amurka da kuma kasashen yamma wadanda suka hada da Burtania, Jamus da Faransa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Fara Musayar Fursinoni Tsakanun Hamas Da HKI A Safiyar Yau Litini October 13, 2025 Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal October 13, 2025 Iran Ba Zata Halarci Zaman Taron Sharm El-Sheikh Ba Saboda Wasu Dalilai Da Ta Bayyana October 13, 2025 Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta October 13, 2025 Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta October 13, 2025 Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje October 13, 2025 Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk October 13, 2025 Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza October 12, 2025 ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice   October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Amurka Donal Trump Ya Isa HKI Kafin Taron Sharm Sheikh
  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara