Zan Samar da Karin Makarantu a Zaria – Dr. Abbas Tajuddeen
Published: 23rd, February 2025 GMT
Shugaban majalisar wakilai, Dr Abbas Tajuddeen ya bayyana aniyar kafa karin makarantu a Zaria.
Shugaban majalisar wakilai, Dr Abbas Tajuddeen ya ce za a kafa karin makarantu a mazabar tarayya ta zaria a kasafin kudin shekarar 2026.
Shugaban majalisar ya bayyana haka ne lokacin babban taron shekara karo na 31 da 32 na kungiyar bunkasa ilimi ta zaria, watau ZEDA da aka gudanar a Zaria.
Ya bayyana cewa makarantun da ake shirin kafa wa sun hada da makarantar firamare da sakandare na yara masu bukata ta musamman da kwalejin tarayya na koyon aikin noma da kiwo.
Shugaban majalisar ya kuma bayyana fara bada tallafi na musamman ga dalibin da ya fi kowa kwazo a fannin koyon ilimin kwamfuta da kuma dalibin da ya fi kowa nuna hazaka a bangaren makarantun sakandare dake lardin zazzau.
Abbas Tajuddeen bayan ya nuna rashin jin dadin sa bisa jinkirin da aka samu wajen biyan dalibai su 2500 kudin tallafin karatu da suke lardin zazzau,ya kuma bayyana kara yawan daliban zuwa 3000 a shekarar 2025.
Shugaban majalisar ya dora alhakin jinkirin da aka samu wajen biyan tallafin akan kaddamar da kasafin kudin shekarar 2024 inda ya bayyana cewa za a biya kudin da zarar al’amura sun daidaita.
Haka kuma ya bada sanarwar cewa zai gina wa kungiyar zeda tare da sanya kayayyaki irin na zamani a dakin taro da zai dauki kimanin mutane dubu daya.
Shugaban majalisar ta wakilai ya kara da cewa kudurin majalisar ne ganin ta bunkasa ilimi a matakin farko da inganta ilimin sakandare da na kimiyya da kawo sauyi a fannonin kirkira.
Domin haka a cewar sa zai magance matsalolin da ake fuskanta da kuma mai tasowa.
A don haka sai ya bukaci kungiyar da ta bullo da wani tsari da zai samar da yanayin baiwa malaman horo da shigar da iyaye cikin harkokin tattauna batutuwan da suka shafi ilimi.
Tun farko a jawabin sa na maraba,shugaban kwamitin tsare-tsare na kungiyar ta ZEDA, Dr Abdul Alimi Bello ya ce Kungiyar ta sami gagarumar nasara da ya nuna aniyar ta na samar da ingantaccen ilimi da bunkasa al’umma.
Ya ce cikin shekaru da dama, kungiyar ta kasance jagoran kungiyoyi masu zaman kansu a lardin zazzau da suke kula da ilimin zamani da bunkasa sana’o’in hannu.
A nashi jawabin, mai martaba Sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya bukaci kungiyar da ta yi amfani da kudaden shigar ta wajen tabbatar da samar da kyakkyawar sauyi a bangaren ilimi.
Haliru Hamza
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Makarabtu Zaria Shugaban majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkukuMai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.
Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.
Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.
Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.
Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.
Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.
Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.
“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,” in ji alkalin.
Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.
Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.
Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.